29/04/2026
ANNABI MUHAMMADU (S.A.W) 🤍
Wani daga cikin masu aikata saɓo…
ya ga ANNABI (S.A.W) a cikin barcinsa—
yana zaune a tsakiyar bayin ALLAH salihai, masu tsarki da yardaddu.
Sai wannan bawan Allah ya ji kunyar kansa…
ya tuna da zunubansa,
ya tuna da sakacinsa…
ya ja baya, ya tsaya a gefe, yana jin bai cancanta ba. 😢
Amma cikin rahama da tausayi…
Sai ABUL-QASIM (S.A.W) ya kira shi da murya mai cike da ƙauna:
👉 “Ya kai bawan ALLAH! Zo kusa da ni…
Haƙiƙa cetona domin irinku ne,
ba domin waɗannan (tsarkaka) kaɗai ba!” 🤲🏼💔
ALLAHU AKBAR!!! 😭
Wannan ita ce rahamar ANNABI (S.A.W)…
Wannan ita ce shafa’arsa…
Wanda ya zo domin masu zunubi, domin masu nadama, domin mu!
🌹 Ash-Shafa’atu! Ash-Shafa’atu Ya Rasulullah! 🌹
Ya ALLAH… Ka sanya mu cikin waɗanda ANNABI (S.A.W) zai yi wa ceto.
Ka ƙara mana ƙaunarSA a cikin zukatanmu.
Ka sa mu mutu a kan sonSA da bin tafarkinSA. 🤲🏼
💫 TASHAR FAIRAH — Wurin Tunatarwa da Ƙaunar Manzon ALLAH (S.A.W) 💫