25/05/2026
Sanarwa Ga Jama'a
08/Dhul/Hajji 1477AH - 25/May/2026M
Anyi Kira Ga Al'ummar Musulmi Dasu Bada Sadakar Fatun Layyarsu Ga Kungiyar Izala
Shugaban Kungiyar Jama'atu Izalatil Bid'ah Wa'iqatissunnah Na Tarayyar Najeriya Sheikh Dr Abdullahi Bala Lau Yayi Kira Ga Al'ummar Musulmi Dasu Cigaba Da Bada Gudummawar Sadaqar Fatun Layyarsu Ga Kungiyar Domin Cigaba Da Gudanar Da Ayyukan Addinin Musulunci A Fadin Kasa Baki Daya.
Shima A Nashi Jawabin Daya Gabatar Ga Ma Nema Labarai Shugaban Kungiyar Izala Na Kasa Reshen Jihar kano Sheikh Farfesa Abdallah Saleh Usman Pakistan JP Yayi Irin Wannan Kiran Musamman Ga Al'ummar Jihar Kano Wajen Cigaba Da Bada Sadaqar Fatun Layyar Tasu Ga Wannan Kungiya Ta Izala.
Shima A Nashi Jawabin Shugaban Kwamitin Fata Na Kasa Malam Alhaji Muhammad Labaran Azare Yayi Kira Ga Al'ummar Musulmi Dasu Kasance Masu Bada Gudummawar Fatun Layyarsu Ga Kungiyar Izala Kamar Yadda S**a Saba Bayarwa A Duk Shekara-Shekara Kasancewa Kungiyar Na Gabatar Da Ayyukan Cigaban Addinin Musulunci A Matakin Kasa Musamman Duba Da Yadda Kungiyar Ke Cigaba Da Aikin Gina Jami'ar Musulmi (Assalam Global University Hadejia) A Jihar Jigawa.
Haka Zalika Shugaban Kwamitin Fatun Layya Na Tarayyar Najeriya Malam Labaran Azare Ya Bayyana Cewa Wadanda Basu Samu Damar Yin Layya Ba Zasu Iya Bada Gudummawar Su Ta Hanyar Yankai Rasitai Na Naira 100, 200 Da Kuma 500.
Daga Karshe Daraktan Agajin Izalar Kano Malam Mukhtar Lawan Tudun Wada Ya Bayyana Cewa Za'a Iya Bada Gudummawar Fatun Layya Ko Siyen Rasitai Ne A Dukkan Masallatai, Majalisai Da Kuma Makarantun Kungiyar Dake Fadin Kasarnan Baki Daya. Akwai Wakilai Yan Agaji A Dukkan Wadannan Wuraren Da Aka Ambata.
Allah Ya Bada Iko,
Allah Yasa Ayi Bukukuwan Sallah Lafiya,
Allah Ya Dawo Da Alhazanmu Ya Karbi Dukkan Ibadun Mu Da Nasu Baki Daya.
AMEEN.
Sanarwa:
DSP A. Bello
Babban Jami'i,
Sashen Yaɗa Labarai Da Hulɗa Da Jama’a Na
Majalisar Agajin Izala Ta Jihar Kano.