17/11/2024
SANARWA!SANARWA!!SANARWA!!!
Assalumu alaikum
Ana sanarwa al-ummah cikin garin takum, jihar taraba dama fadin Nigeria Cewa akwai garabasa da cigaba da yasamu wannan Gari mai albarka na samarwa da bude sabuwar Makarantar haddan Al-Qur'ani Mai girma tare da rerashi cikin Murya da sauti Mai dadi hade da tajweed.
SUNAN MAKARANTAR πKULLIYATU SHEIKH MAHMOUD KHALEEL AL-HUSSARY TAKUM
Insha Allah wannan makaranta tayi tsari ingantacce domin baiwa dalibanta haddan Al-Qur'ani Mai inganci Wanda iyaye da sauran jama'ar gari bazasuyi danasani ba.
Wannan makaranta Mai Albarka ta qayyade cewa dalibai 30 kacal zata dauka a matakin farko,kuma tsarin daukar shine mutum 30 Wanda s**afara sayan form sune Wadanda zasu more wannan Garabasar.
TSARIN KARATUN
1.Dalibai maza Bodin sukul ne(zasu dinga kwana ne a Makarantar)
2.Dalibai Mata kuma Day sukul ne(Zasu zo daga safe zuwa 6pm yamma).
Domin neman karin bayani a tuntube wadannan lambobin:ππππππ
+234 813 782 1799 09017008200
Abin lura shine: Mutum 30 na farkon sayan form sune zasu kwashe wannan Garabasar
Wassalam.