Ilimi Kogi Mai Zurfi

Ilimi Kogi Mai Zurfi An kirkiri wannan page domin fadakar da Yan uwa musulmi bisa sha'anin musulunci

20/09/2024

Ya Allah Ka hadamu da abokai na gari 🙏

Wannan shine abinda zai faru idan DAJJAL ya bayyana a Duniya! 👇Idan Dajjal ya fito dubunnan YAHUDAWA za su bi shi, su yi...
21/10/2023

Wannan shine abinda zai faru idan DAJJAL ya bayyana a Duniya! 👇

Idan Dajjal ya fito dubunnan YAHUDAWA za su bi shi, su yi tururuwa a kansa, da nufin yaƙar Musulmi.

Daga nan sai Annabi Isa (a.s) ya sauko, a dai dai wannan lokacin Musulmin duniya za su bi shi don yaƙar DAJJAL da mabiyansa. Annabi Isah zai kira Yahudawa zuwa Musulunci, baya son komai daga gare su a lokacin sai su karɓi Musulunci.

Wasu daga cikinsu za su Musulunta, wasu kuma za su ci gaba da zama mabiya addinin Yahudanci, sannan yaƙin da Manzon Allah (ﷺ) ya ambata a cikin Hadisi zai wakana.

Manzon Allah (ﷺ) Yace: "Al-ƙiyama ba za ta tsaya ba har sai Musulmai sun yaƙi Yahudawa suna masu kashe su, har sai Bayahude ya ɓoye a bayan dutse da itatuwa suna kuka da neman ceto sai dutse yace: Ya kai Musulmi kazo akwai wani Bayahude yana ɓoye a bayana kazo gashi ka kashe shi"

Allah Maɗaukakin Sarki zai girmama Musulmi a wannan yaƙin da wannan mu'ujiza, wato duwatsu da bishiyoyi za su yi magana su kira Musulmi da su zo su kashe Yahudawan da za su fake a bayansu.

Wannan yaƙi da Musulmi zasu yi ƙarkashin jagorancin Annabi Isah (a.s) ɗaya daga cikin manzannin Allah masu daraja, zai kasance a kan DAJJAL ne da magoya bayansa (Kafirai) da s**a taru don yaƙar Musulmi.

Wannan yana nuni da cewa zai kasance yaƙi ne na adalci wanda Allah ya yarda da shi, kamar yadda ya faru a dukkannin yaƙunan Musulunci da nufin ɗaukaka kalmar Allah a doron ƙasa.

Yazo a cikin Hadisin da Musulim ya ruwaito Manzon Allah ﷺ Yace: "Duk wanda ya yi yaƙi domin kalmar Allah ta tabbata a (doron ƙasa) toh, haƙiƙa shine ya ke yaƙi a tafarkin Allah"

Allah ka ɗaukaka darajar Addinin Musulunci da Musulmi baki ɗaya! Allahumma Ameen 🤲

~A_sada_Wannan shine abinda zai faru idan DAJJAL ya bayyana a Duniya! 👇

Idan Dajjal ya fito dubunnan YAHUDAWA za su bi shi, su yi tururuwa a kansa, da nufin yaƙar Musulmi.

Daga nan sai Annabi Isa (a.s) ya sauko, a dai dai wannan lokacin Musulmin duniya za su bi shi don yaƙar DAJJAL da mabiyansa. Annabi I ~{A_sada modachi}

20/10/2023

Watarana Manzon Allah {ﷺ} ya tambayi Mala'ika JIBRIL (عَلَيْهِ ٱلسَّلَامُ) "Shin ka taɓa yin tafiya a cikin yanayin sauri?" Sai Mala'ika Jibril ya ce: Eh na taɓa yi sau huɗu. Sai Manzon Allah (ﷺ) ya ce: A ina da ina? Sai Mala'ika Jibril Yace:

1. A karon farko shine lokacin da za'a jefa Annabi Ibrahim (عَلَيْهِ ٱلسَّلَامُ) a cikin wuta, a lokacin ina kusa da Al-Arshi, Allah ya umarceni da nazo na sanyaya wutar. Nan take na bar inda nake na sauko saman bakwai cikin lokaci na isa a wajen.

2. A karo na biyu shi ne lokacin da Annabi Ibrahim (عَلَيْهِ ٱلسَّلَامُ) yake shirin yanka ɗansa Annabi Isma'il (A.S) a Mina, Allah ya umarceni da in musanya ɗansa da rago, kafin Annabi Ibrahim ya yanka wuyan ɗansa Ismail da wuƙa.

3. A karo na uku shine lokacin da 'yan uwan Annabi Yusuf (عَلَيْهِ ٱلسَّلَامُ) s**a jefa shi cikin rijiya, Allah ya umarceni da in ceci Annabi Yusuf, take na garzaya na sanya fika-fikina a karkashin inda za'a jefa Annabi Yusuf kafin ya isa wurin.

4. Na ƙarshe kuma shine lokacin da kai ya Rasulillah (Annabi Muhammad ﷺ) ka ji rauni a haƙorinka a yaƙin UHUDU. Sai Allah ya umurce ni da in tsayar da jinin ka kafin ya isa a ƙasa, idan ba haka ba babu wani tsiro ko bishiya da zata sake fitowa a doron ƙasa. Da jin haka sai na garzaya na tare jininka da fika-fikai na kafin ya sauka a ƙasa. SUBHANALLAH ☝️😭

Allah ka ƙarawa Annabi Muhammad ﷺ daraja, ya kuma ƙara mana sonshi a cikin zukatanmu 💚 🤍 ❤️ 💙 ❤️‍🩹 Allahumma Ameen 🤲

~{A_sada modachi}

Address

Sokoto

Telephone

+2348122664556

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ilimi Kogi Mai Zurfi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share