09/07/2021
KWAMITIN MALAMAI MASU ADDU'A NA FAKON IDI SUNA CIGABA DA KARATUN AQUR'ANI DA ADDU'O'IN NEMAN ZAMAN LAFIYA DA WANZUWAR TATTALIN ARZIKI GA JIHAR SAKKWATO DA NAJERIYA BAKI DAYA.
Kwamitin Malamai Masu Addu'a dake Babban Masallacin FAQON IDI dake nan Sakkwato Suna Cigaba da gudanar da Karatun Al'qur'ani Da Addu'o'in Neman Samun Sauki a kan Sha'anin Tsaro da, Kuma Wanzuwar Tattalin Arziki a cikin Wannan jaha tamu ta Sakkwato da kasa Baki daya..
Wannan kwamitin Yana Kara Kira ga Al'ummar Musulmi a Duk inda Suke a Fadin Najeriya, da Suci gaba da Addu'o'in Neman Saukin Matsalolin Rashin Tsaro da Sunka addabi Alummar Wannan Kasa tamu da, Jihohin Arewa,
Ana gudanar da Addu'o'in ne a Masallacin FAQON IDI dake Nan Cikin Babban Birnin Sakkwato a Ranar kowace JUMU'A ta kowane Sati.
Muna Rokon Allah Ya Kawo muna Zaman lafiya ga Wannan Kasa tamu da, Kuma jahohin mu Na Arewa.
29th /11/1442. AH.