28/04/2026
Sanarwa! Sanarwa!! Sanarwa!!!
A madadin Shugaban Kwamitin Alarammomi na Jihar Neja, Dr. Ishaq Ibrahim Kagara, tare da mataimakansa, ana sanar da ɗaukacin Alarammomin jihar cewa za a gabatar da musaffa kamar yadda aka saba yi duk bayan watanni uku-uku.
An riga an gudanar da wannan taro a Zone B (garin Minna) da kuma Zone A (garin Bida). Yanzu kuma lokaci ya yi na Zone C, inda za a gudanar da shi a garin Kontagora.
A wannan karo, za a yi sauƙa (ختمة) In shā Allah, daga aya ta 46 a cikin (سورة العنكبوت) har zuwa ƙarshen (سورة الناس).
Muna roƙon Allah Ya ba mu ikon halarta, Ya sa a yi lafiya a gama lafiya, kuma Ya dawo da mu lafiya.
Sanarwa daga:
Mataimakin Shugaban Kwamitin Alarammomi na II
Muhammad Nura Umar Alkashnawee