18/11/2025
Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda, Ph.D., CON, ya umurci Yahaya Masuss**a da ya shirya kare kansa a gaban kwamitin malamai dangane da zarge-zargen da ake masa
Sanarwar wadda ta fito daga ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana cewa
Gwamnatin Jihar Katsina ta karɓi korafe-korafe cewa wa'azi da koyarwar Yahaya Massuss**a sun saba wa ƙa’idojin shari’ar Musulunci. Haka kuma, Gwamnati ta karɓi wata ƙara daga ɓangaren Yahaya Massuss**a cewa mambobin Jama’atu Izalatil Bid’a suna zagin sa tare da yi masa barazanar hari.
A kokarin magance wannan matsala daga tushe, an mika batun zuwa Masarautar Katsina ƙarƙashin jagorancin Mai Martaba Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman, CFR.
Sarkin ya gayyaci Yahaya Masuss**a da wasu malamai zuwa fadarsa, inda aka gudanar da tattaunawa
Duk da haka, rahotanni sun nuna cewa matsalar na ci gaba. A saboda haka, a wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jiha, Abdullahi Garba Faskari, Esq., ya sanya wa hannu, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, Ph.D., CON, ya umurci Malam Yahaya da ya shirya kare kansa a gaban kwamitin malamai dangane da zarge-zargen da ake masa. Bayan haka, za a kafa ƙa’idoji da dokoki, kuma duk wanda ya karya waɗannan ƙa’idojin, Gwamnati za ta ɗauki matakin da ya dace a kansa.
Gwamnati na roƙon jama’a da su yi haƙuri yayin da ake gudanar da wannan lamari cikin adalci da hankali.
Idan ba'a manta ba ranar Alhamis din da ta gabata Masarautar Katsina ta gabatar da zama da Shuwagabannin Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ikamatis Sunnah na Karamar Hukumar Dutsinma da Yahayya Masuss**a domin sauraren korafin da ya shigar
Wanda zaman ya gudana kaman haka
" An gabatar da zaman tattaunawar ne a fadar Mai Martaba Sarkin Katsina domin neman fahimtar juna da sasanta maganganun da s**a taso tsakanin Ƙungiyar JIBWIS ta Karamar Hukumar Dutsinma da Ƙungiyar Al-Qur’ani Zalla karkashin jagorancin Yahayya Masuss**a
Da farko an fara da bada mutane (wakilai) huɗu (4) daga kowanne bangare