04/05/2021
Daren ashirin da uku yana daya daga cikin dararen da ake tsammani mai karfi na lailatul qadri, yazo a hadithi ingantacce daga Abdullahi bn Unais R.A yace: Manzo S.A.W yace: (An sanar dani daren lailatul qadri, Sai aka kuma mantar dani yaushe ne, amma kuma an nuna mini a cikin bacci, cewa nayi sujjada cikin ruwa da tabo a asubahin washe garin daren, sai aka mana ruwan sama cikin daren 23 ga wata, bayan munyi sallar asuba sai muka ga ruwa da tabo suna diga daga goshi da hancin Manzo S.A.W).
Duba Muslim: (1168). da Ahmada: (16088), da Baihaqee: (8799).
Karin bayani:
Kamar yadda aka sani mafarkin Annabawa gaskiya ne, kuma gashi kamar yadda muka gani a hadithin nan, daman kuma rufin Masallacin a lokacin sa S.A.W anyi shine da kaba da kuma ganyen dibino, sabida haka in anyi ruwa yakan isa kasa, don haka mu dage a wannan dare, kamar yadda mukayi bayani daren na iya zuwa 21, ko 23, ko 25, ko 27 ko ma 29.
Kada a manta da yawan maimaita Allahumma innaka afuwun tuhibbul afwa fa'fu annaa.
Allah ya datar damu ya karba mana.