Jibwis Katsina

Jibwis Katsina Don Zumunta mai dorewa ga 'ya'yan Kungiyar Jibwis, da kuma fadada hanyar Da'awa. Allaah Ya tabbatar

Bayanin bayan taro na kammala taron 'Wold Muslim League' da Jama'atu Izalatil bid'ah wa iƙamatis sunnah da ya gabata a A...
15/08/2026

Bayanin bayan taro na kammala taron 'Wold Muslim League' da Jama'atu Izalatil bid'ah wa iƙamatis sunnah da ya gabata a Abuja.

Taron Ƙasa da Ƙasa kan Bambancin Addini da Al’adu da Zaman Lafiyar Al’umma.
Abuja, Najeriya | 11–12 ga Agusta, 2026

A ƙarƙashin kulawa ta musamman ta Mai Girma Bola Ahmed Tinubu, Shugaban Tarayyar Najeriya

Wanda ya shirya: Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (Muslim World League – MWL)
Tare da haɗin gwiwar: Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Najeriya

Gabatarwa

A ƙarƙashin kulawa ta musamman ta Mai Girma Shugaban Tarayyar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (MWL), tare da haɗin gwiwar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS) ta Najeriya, ta shirya taron ƙasa da ƙasa mai taken:

“Bambancin Addini da Al’adu da Zaman Lafiyar Al’umma: Haɗin Gwiwa Domin Kyakkyawar Makoma.”

An gudanar da taron a Abuja, babban birnin Tarayyar Najeriya, a ranakun 11 da 12 ga Agusta, 2026.

Taron ya haɗa manyan shugabannin addinan Musulunci da Kiristanci, manyan malamai da masana, masu yanke shawara, wakilan hukumomin gwamnati, ƙungiyoyin farar hula, hukumomin yanki da na ƙasa da ƙasa, da kuma wasu fitattun mutane daga Najeriya, Afirka ta Yamma da sauran ƙasashen duniya.

An gudanar da taron ne a daidai lokacin da duniya ke fuskantar ƙalubale masu yawa waɗanda ke shafar zaman lafiyar al’umma, ƙara yaɗuwar kalaman ƙiyayya, da haddasa rikice-rikicen addini da ƙabilanci, waɗanda ke barazana ga haɗin kan al’umma da kuma kawo cikas ga ci gaba da kwanciyar hankali.

Mahalarta taron sun tabbatar da cewa bambancin addini, al’adu da ƙabilu wata hakika ce ta rayuwar ɗan Adam, kuma bai k**ata a ɗauke shi a matsayin abin da ke haifar da rikici da rarrabuwar kai ba. Maimakon haka, bambance-bambancen na iya zama wata dama ta wadatar da wayewar ɗan Adam da haɓaka ci gaban al’umma.

Mahalarta sun jaddada muhimmiyar rawar da addinai ke takawa wajen samar da zaman lafiya, ƙarfafa dabi’un zama ɗan ƙasa, haɓaka tattaunawa da haɗin gwiwa, da kuma amfani da kyawawan ƙa’idojin ɗan Adam da aka yi tarayya a kansu wajen gina makoma mafi aminci da wadata ga al’ummar Najeriya, Afirka ta Yamma da daukacin bil’adama.

Mahalarta sun kuma tabbatar da cewa nahiyar Afirka, wadda take da ɗimbin tarihi, al’adu da gadon ɗan Adam, tana da damar zama abin koyi wajen gudanar da bambance-bambance cikin hikima, idan shugabannin addinai, hukumomin gwamnati da ƙungiyoyin farar hula s**a haɗa ƙarfi cikin tsarin kishin ƙasa, mutunta juna da bin ƙa’idojin addini da ɗabi’a da aka yi tarayya a kansu.

Dangane da ƙa’idojin da Shari’ar Musulunci da sauran saƙonnin Allah s**a tabbatar wajen kafa adalci, rahama da fahimtar juna tsakanin mutane; da kuma yin koyi da tanade-tanaden Yarjejeniyar Makka mai tarihi (Charter of Makkah) da ƙa’idojin da ta kafa na zaman tare da haɗin kan bil’adama; tare da fahimtar babban nauyin da ke wuyan shugabannin addini da masana wajen ƙarfafa zaman lafiya a cikin al’umma, zaman taron masana, tattaunawar manyan mutane, da babban taron shugabannin Musulmi da Kirista sun haifar da waɗannan matsaya da ƙuduri:

NA FARKO: ABUBUWAN DA AKA TABBATAR

1. Bambancin addini, ƙabila da al’adu hakika ne na duniya baki ɗaya. Gudanar da wannan bambanci cikin hikima yana daga cikin muhimman ginshiƙai na ƙarfafa haɗin kan ƙasa da gina al’umma mai ɗorewa da haɗin kai.

2. Addini a asalinsa saƙo ne na rahama da zaman lafiya. Shugabannin addinai suna da alhakin bayyana sahihan ƙa’idojin addinai da yin watsi da amfani da addini wajen tayar da rikici ko halatta tashin hankali da tsattsauran ra’ayi.

3. Zaman lafiyar al’umma ginshiƙi ne mai muhimmanci na tsaron ƙasa, kuma ba za a iya samunsa ba sai ta hanyar haɗin gwiwar hukumomin gwamnati, shugabannin addini, cibiyoyin ilimi, kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin farar hula.

4. Tattaunawar ƙasa mai haɗa kowa ita ce hanya mafi inganci wajen magance tushen tashin hankali, ƙarfafa amincewa tsakanin al’ummomin addinai da ƙabilu daban-daban, da haɓaka al’adar haɗin gwiwa domin hidimar ƙasa.

5. Akwai matuƙar muhimmanci wajen ƙarfafa tsaron tunani da kare al’umma daga kiraye-kirayen tsattsauran ra’ayi, son zuciya da ƙiyayya, tare da yaɗa matsakaicin tsarin koyar da addini wanda ya ginu a kan hikima, daidaito da tafarkin tsaka-tsaki.

6. Akwai buƙatar ƙarfafa matasa da mata tare da shigar da su cikin shirye-shiryen ƙasa da nufin haɓaka al’adar zaman lafiya, ƙarfafa kishin al’umma da nauyin zama ɗan ƙasa, da kuma tabbatar da kyawawan ɗabi’un zama ɗan ƙasa.

7. Cibiyoyin ilimi da na addini suna da muhimmiyar rawa wajen tarbiyyantar da sababbin ƙarni su mutunta bambance-bambance, su ƙarfafa dabi’un haƙuri da zaman tare, tare da kare asalin ƙasa, yayin da suke riƙe da kuma alfahari da asalin addininsu.

8. Cigaba mai ɗorewa ba ya rabuwa da zaman lafiyar al’umma, yayin da tsaro da kwanciyar hankali su ne muhimman abubuwan da ke samar da yanayin da al’umma za ta bunƙasa kuma ta samu cigaba.

NA BIYU: ƘUDURORI

1. Shugabannin addinai da s**a halarci wannan taro, waɗanda ke wakiltar addinai da mazhabobi daban-daban, sun bayyana aniyarsu ta cigaba da gudanar da tattaunawar hukumomi akai-akai, da ƙarfafa haɗin gwiwa a dukkan abubuwan da za su taimaka wajen haɗin kan al’umma da kare tsaro da zaman lafiyarta.

2. A kafa wata hukumar haɗin gwiwa ta shugabannin Musulmi da Kirista da cibiyoyinsu a Najeriya, tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (MWL), domin daidaita shirye-shiryen haɗin gwiwa da ƙarfafa shawarwari da haɗin kai kan abubuwan da s**a shafi muradun bai ɗaya.

3. A amince da shirin Mai Girma Sakatare-Janar na Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya, Sheikh Dr. Mohammed Al-Issa, mai taken “Nigerian Youth for Peace” (Matasa ’Yan Najeriya Domin Zaman Lafiya).

Shirin zai yi aiki kafada da kafada da hukumar da aka ambata a sama, ya gudanar da ayyukansa a dukkan shiyyoyin siyasa shida na Najeriya, sannan ya yaɗa sak**akon ayyukansa da abubuwan da aka cimma ga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa.

4. A ƙaddamar da shirye-shiryen wayar da kan jama’a a ƙasa baki ɗaya waɗanda za su ƙarfafa kishin ƙasa da jin cewa mutum ɗan ƙasa ne, su haɓaka al’adar mutunta bambance-bambance, da yaƙi da kalaman ƙiyayya da dukkan nau’o’in rashin haƙuri.

5. A yi kira ga kafafen yaɗa labarai da cibiyoyin al’adu da su rungumi yaɗa saƙonnin da ke da alhaki, waɗanda ke inganta zaman lafiyar al’umma, yaƙi da jita-jita da kalaman da ke tayar da hankali, tare da nuna kyawawan misalan haɗin kai, zaman tare da fahimtar juna da ake samu a ƙasa.

6. A tallafa wajen samar da manhajojin karatu da shirye-shiryen horaswa waɗanda za su ƙarfafa dabi’un zama ɗan ƙasa, mutunta juna, tattaunawa da zaman tare, tare da ƙarfafa juriyar tunani da fahimtar matasa wajen fuskantar akidu masu haɗari.

7. A amince da tsarin aiki na haɗin gwiwa tsakanin hukumomin gwamnati, shugabannin addinai da ƙungiyoyin farar hula domin magance ƙalubalen zaman tare, ƙarfafa tsaron tunani da tabbatar da zaman lafiyar al’umma.

Haka kuma, a bibiyi sak**akon yarjejeniyoyin fahimtar juna (MoUs) da aka rattaba hannu a kansu a yayin taron, tare da daidaita shirye-shirye da ayyukan da za su samo asali daga gare su, domin tabbatar da aiwatar da su yadda ya k**ata da kuma cimma manufofinsu.

8. A ƙarfafa haɗin gwiwa a fannonin hana rikice-rikice, kare haɗin kan ƙasa da haɓaka amincewa da juna tsakanin al’umma.

9. A yaba wa ƙoƙarin Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (MWL) wajen inganta tattaunawa tsakanin mabiyan addinai da al’adu daban-daban.

Haka kuma, a yaba wa ƙa’idojin da ke cikin Yarjejeniyar Makka mai tarihi (Charter of Makkah) da kuma Yarjejeniyar Gina Gada tsakanin Makarantu da Mazhabobin Tunani na Musulunci (Charter of Building Bridges between Islamic Schools of Thought and Sects).

A kuma yi kira da a faɗaɗa shirye-shiryen ilimi, horaswa da kafafen yaɗa labarai na MWL ta hanyoyin da za su taimaka wajen haɓaka dabi’un matsakaici, haƙuri, da haɗin gwiwar ɗan Adam da na Musulunci.

A ƘARSHE
Mahalarta taron sun bayyana matuƙar godiya da yabo ga Mai Girma Shugaban Tarayyar Najeriya bisa karamcin da ya yi na ɗaukar nauyin kulawar taron.

Sun kuma nuna godiya ga Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (MWL) da Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS) ta Najeriya bisa kyakkyawan tsari da shirya taron, da kuma ƙoƙarin gaskiya da s**a yi wajen tabbatar da nasarar taron da cimma manufofinsa.

Haka kuma, sun nuna godiya ga dukkan ƙungiyoyi da cibiyoyin Musulmi da Kirista da s**a ba da haɗin kai, bisa irin gudummawar da s**a bayar da kuma halartar da s**a yi wajen tabbatar da nasarar taron da yaɗa saƙonsa da manufofinsa.

Mahalarta taron sun kuma yaba da kyakkyawan yanayin da ya kasance a dukkan zaman taron, da kuma sahihiyar aniyar da mahalarta s**a nuna wajen ƙarfafa gadojin amincewa da fahimtar juna tsakanin al’ummomin addinai da al’adu daban-daban.

Sun tabbatar da cewa zaman lafiyar al’umma nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa, kuma sahihiyar haɗin gwiwa tsakanin shugabannin addinai, hukumomin gwamnati da ƙungiyoyin farar hula ita ce hanya mafi inganci wajen gina makoma mafi aminci, kwanciyar hankali da wadata.

Sun kuma tabbatar da aniyarsu ta ci gaba da haɗin gwiwa da daidaita ayyuka, tare da mayar da sak**akon wannan taro zuwa shirye-shiryen aikace-aikace da ayyuka masu ɗorewa waɗanda za su ƙarfafa zaman lafiyar al’umma, haɓaka al’adar tattaunawa, tallafa wa tsaro, kwanciyar hankali da cigaba a Najeriya da Afirka ta Yamma. Haka kuma, za su ba da gudummawa wajen gina duniya mai zaman lafiya, adalci da haɗin kai.

Jibwis Nigeria

12/08/2026

Mai Wa’azi Na Gaba Sheikh Imam Abdullahi Bala Lau (Shugaban Kungiya Na Kasa)
Wazin Kasa, Abuja 2026
Muna kawo muku Wa'azin Ƙasa kai tsaye daga babban taron JIBWIS/Rabida International Conference 2026 da ke gudana a Abuja, Najeriya.
’azi

12/08/2026

W
a’azin Kasa, Abuja 2026
Muna kawo muku Wa'azin Ƙasa kai tsaye daga babban taron JIBWIS/Rabida International Conference 2026 da ke gudana a Abuja, Najeriya.
’azi

12/08/2026

ll Wa’azin Kasa, Abuja 2026
Muna kawo muku Wa'azin Ƙasa kai tsaye daga babban taron JIBWIS/Rabida International Conference 2026 da ke gudana a Abuja, Najeriya.
’azi

12/08/2026

Mai Wa’azi Na Farko ll Sheikh ll Wa’azin Kasa, Abuja 2026
Muna kawo muku Wa'azin Ƙasa kai tsaye daga babban taron JIBWIS/Rabida International Conference 2026 da ke gudana a Abuja, Najeriya.
’azi

HOTUNA: RANA TA FARKO TA TARON ƘASA DA ƘASA KAN TSARO A NAJERIYAA jiya Talata ne aka buɗe babban taron ƙasa da ƙasa kan ...
12/08/2026

HOTUNA: RANA TA FARKO TA TARON ƘASA DA ƘASA KAN TSARO A NAJERIYA

A jiya Talata ne aka buɗe babban taron ƙasa da ƙasa kan zaman lafiya, haɗin kan ƙasa da tsaro a Najeriya, wanda Jama’atu Izalatil Bidi’a Wa Ik**atis Sunnah (JIBWIS) ta shirya tare da haɗin gwiwar Muslim World League (Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya).

Ana gudanar da taron ne na tsawon kwanaki biyu a International Conference Centre (ICC), Abuja, inda manyan shugabannin addinai, malamai, sarakunan gargajiya, jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban s**a hallara.

Taron ya mayar da hankali ne kan tattauna hanyoyin da za su taimaka wajen ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kan al’umma da inganta tsaro, tare da duba alaƙar da ke tsakanin zaman lafiya, tsaro da ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin ƙasa.

Shugaban Jama’atu Izalatil Bidi’a Wa Ik**atis Sunnah (JIBWIS) ta Jihar Katsina, Sheikh (Dr.) Yakubu Musa Hassan Katsina (Sautus-Sunnah), na cikin manyan shugabannin ƙungiyar da s**a halarci wannan muhimmin taro.

Haka kuma, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, na daga cikin manyan shugabannin gwamnati da aka gayyato zuwa taron, inda ya samu wakilcin Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina, Hon. Faruk Lawal Jobe.

Taron yana ƙarƙashin jagorancin Mai Girma Sheikh Dr. Muhammad bin Abdulkarim Al-Issa, Babban Sakataren Muslim World League, wanda ya jagoranci tattaunawar da ta shafi manyan ƙalubalen tsaro da Najeriya ke fuskanta da kuma hanyoyin da za a bi wajen samar da ɗorewar zaman lafiya.

An kuma tattauna muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin malamai, shugabannin addinai, gwamnati, sarakunan gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki wajen magance matsalolin da ke barazana ga zaman lafiya da tsaron ƙasa.

Za'a kammala taron a yau Laraba, inda ake sa ran fitar da muhimman shawarwari da za su taimaka wajen ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kan ƙasa da tsaro a Najeriya.

JIBWIS Katsina
28 Safar, 1448
12 August, 2026

Shugaban Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ik**atis Sunnah ta Jihar Katsina Sheikh (Dr) Yakubu Musa Hassan Katsina (S...
11/08/2026

Shugaban Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ik**atis Sunnah ta Jihar Katsina Sheikh (Dr) Yakubu Musa Hassan Katsina (Sautus-Sunnah) tare da Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda wanda ya samu wakilcin mataimakin shi Hon. Faruk Lawal Jobe a dakin taro na ƙasa da ƙasa da ke Abuja

Wajen babban taron ƙasa da ƙasa wanda Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ik**atis Sunnah haɗin gwiwa da Muslim World League

JIBWIS Katsina
27 Safar, 1448
11 August, 2026

Ku kasance da mu domin ganin yadda taron ƙasa da ƙasa da ƙungiyar Jama'atu Izalatil Bid'ah Wa Iqamatis Sunnah tare da ha...
11/08/2026

Ku kasance da mu domin ganin yadda taron ƙasa da ƙasa da ƙungiyar Jama'atu Izalatil Bid'ah Wa Iqamatis Sunnah tare da hadin gwiwar Muslim World League

KUNGIYAR IZALA BA TA DA ALAKA DA WATA  ƘUNGIYA MAI SUNA “GAMAYYAR MATASAN IZALA DA DARIKA” A JIHAR KATSINA Kwamitin Mata...
10/08/2026

KUNGIYAR IZALA BA TA DA ALAKA DA WATA ƘUNGIYA MAI SUNA “GAMAYYAR MATASAN IZALA DA DARIKA” A JIHAR KATSINA

Kwamitin Matasa na Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ik**atis Sunnah ta Jihar Katsina ya ci karo da wani bayani a kafar sada zumunta ta Facebook, wanda ke magana kan wata ƙungiya mai suna “Gamayyar Matasan Izala da Darika”, wadda ta bayyana matsayarta dangane da zaɓen shekarar 2027 da ke tafe.

Kwamitin Matasan JIBWIS ta Jihar Katsina ya tabbatar da cewa Ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’a Wa Ik**atis Sunnah ba ta da wata alaƙa, haɗin gwiwa ko gamayya da wata ƙungiya mai suna “Gamayyar Matasan Izala da Darika” a Jihar Katsina.

Saboda Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ik**atis Sunnah tana da tsari da matakai na gudanar da ayyukanta, tun daga harkokin da’awa, wayar da kan al’umma, taimakon marayu da gajiyayyu, kula da marasa lafiya da sauran ayyukan jinƙai, har zuwa batutuwan da s**a shafi harkokin siyasa.

Saboda haka, duk wani muhimmin batu da ya shafi matsayar ƙungiyar yana buƙatar bin matakan da aka tanada kafin a bayyana shi a matsayin matsayar ƙungiyar.

Kwamitin ya bayyana cewa ba ta da masaniya kan taron da aka gudanar da sunan “Gamayyar Matasan Izala da Darika”, wanda daga bisani aka fitar da bayanin bayan taron. Haka kuma, an gudanar da wannan taro ba tare da yardar ko wakilcin JIBWIS ta Jihar Katsina ba.

MATSAYAR JIBWIS KAN ZAƁEN 2027

Dangane da batun siyasar shekarar 2027, Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ik**atis Sunnah ta Jihar Katsina ba ta yanke wata matsaya a kan zaɓen shekarar 2027 ba.

Amman idan bukatar hakan ta k**a za ta tattauna akan hakan, kuma za ta sanar ta hanyoyin da ta ke bi domin isar da sakonnin ta.

Don haka, duk wani mutum ko ƙungiya da ya fito ya bayyana wata matsaya ko ra’ayi dangane da zaɓen shekarar 2027, ba tare da an sanar da matsayar ƙungiyar ta hanyar da ta dace ba, ra’ayin kansa ne, ba matsayar Ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’a Wa Ik**atis Sunnah ba.

KIRA GA AL’UMMA

Kungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’a Wa Ik**atis Sunnah ta Jihar Katsina tana kira ga mambobin ƙungiyar da al’umma baki ɗaya da su yi hattara da duk wani bayani da za'a yaɗa a kafafen sada zumunta, musamman bayanan da ba a tabbatar da cewa sun fito daga shafin ƙungiyar ko shafukan da ƙungiyar ta amince da su ba.

Haka kuma, Kungiyar tana kira ga jama’a da su rika bibiyar shafin "Jibwis Katsina" domin samun sahihin bayani kan ayyukanta da sauran muhimman al’amuranta.

Allah ya ba mu ikon riƙon gaskiya da amana, ya kuma haɗa kan al’umma bisa gaskiya da adalci. Amin.

JIBWIS Katsina
26 Safar, 1448
10 August, 2026

Address

Ibb Way
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jibwis Katsina posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to Jibwis Katsina:

Shortcuts

Share