15/08/2026
Bayanin bayan taro na kammala taron 'Wold Muslim League' da Jama'atu Izalatil bid'ah wa iƙamatis sunnah da ya gabata a Abuja.
Taron Ƙasa da Ƙasa kan Bambancin Addini da Al’adu da Zaman Lafiyar Al’umma.
Abuja, Najeriya | 11–12 ga Agusta, 2026
A ƙarƙashin kulawa ta musamman ta Mai Girma Bola Ahmed Tinubu, Shugaban Tarayyar Najeriya
Wanda ya shirya: Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (Muslim World League – MWL)
Tare da haɗin gwiwar: Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Najeriya
Gabatarwa
A ƙarƙashin kulawa ta musamman ta Mai Girma Shugaban Tarayyar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (MWL), tare da haɗin gwiwar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS) ta Najeriya, ta shirya taron ƙasa da ƙasa mai taken:
“Bambancin Addini da Al’adu da Zaman Lafiyar Al’umma: Haɗin Gwiwa Domin Kyakkyawar Makoma.”
An gudanar da taron a Abuja, babban birnin Tarayyar Najeriya, a ranakun 11 da 12 ga Agusta, 2026.
Taron ya haɗa manyan shugabannin addinan Musulunci da Kiristanci, manyan malamai da masana, masu yanke shawara, wakilan hukumomin gwamnati, ƙungiyoyin farar hula, hukumomin yanki da na ƙasa da ƙasa, da kuma wasu fitattun mutane daga Najeriya, Afirka ta Yamma da sauran ƙasashen duniya.
An gudanar da taron ne a daidai lokacin da duniya ke fuskantar ƙalubale masu yawa waɗanda ke shafar zaman lafiyar al’umma, ƙara yaɗuwar kalaman ƙiyayya, da haddasa rikice-rikicen addini da ƙabilanci, waɗanda ke barazana ga haɗin kan al’umma da kuma kawo cikas ga ci gaba da kwanciyar hankali.
Mahalarta taron sun tabbatar da cewa bambancin addini, al’adu da ƙabilu wata hakika ce ta rayuwar ɗan Adam, kuma bai k**ata a ɗauke shi a matsayin abin da ke haifar da rikici da rarrabuwar kai ba. Maimakon haka, bambance-bambancen na iya zama wata dama ta wadatar da wayewar ɗan Adam da haɓaka ci gaban al’umma.
Mahalarta sun jaddada muhimmiyar rawar da addinai ke takawa wajen samar da zaman lafiya, ƙarfafa dabi’un zama ɗan ƙasa, haɓaka tattaunawa da haɗin gwiwa, da kuma amfani da kyawawan ƙa’idojin ɗan Adam da aka yi tarayya a kansu wajen gina makoma mafi aminci da wadata ga al’ummar Najeriya, Afirka ta Yamma da daukacin bil’adama.
Mahalarta sun kuma tabbatar da cewa nahiyar Afirka, wadda take da ɗimbin tarihi, al’adu da gadon ɗan Adam, tana da damar zama abin koyi wajen gudanar da bambance-bambance cikin hikima, idan shugabannin addinai, hukumomin gwamnati da ƙungiyoyin farar hula s**a haɗa ƙarfi cikin tsarin kishin ƙasa, mutunta juna da bin ƙa’idojin addini da ɗabi’a da aka yi tarayya a kansu.
Dangane da ƙa’idojin da Shari’ar Musulunci da sauran saƙonnin Allah s**a tabbatar wajen kafa adalci, rahama da fahimtar juna tsakanin mutane; da kuma yin koyi da tanade-tanaden Yarjejeniyar Makka mai tarihi (Charter of Makkah) da ƙa’idojin da ta kafa na zaman tare da haɗin kan bil’adama; tare da fahimtar babban nauyin da ke wuyan shugabannin addini da masana wajen ƙarfafa zaman lafiya a cikin al’umma, zaman taron masana, tattaunawar manyan mutane, da babban taron shugabannin Musulmi da Kirista sun haifar da waɗannan matsaya da ƙuduri:
NA FARKO: ABUBUWAN DA AKA TABBATAR
1. Bambancin addini, ƙabila da al’adu hakika ne na duniya baki ɗaya. Gudanar da wannan bambanci cikin hikima yana daga cikin muhimman ginshiƙai na ƙarfafa haɗin kan ƙasa da gina al’umma mai ɗorewa da haɗin kai.
2. Addini a asalinsa saƙo ne na rahama da zaman lafiya. Shugabannin addinai suna da alhakin bayyana sahihan ƙa’idojin addinai da yin watsi da amfani da addini wajen tayar da rikici ko halatta tashin hankali da tsattsauran ra’ayi.
3. Zaman lafiyar al’umma ginshiƙi ne mai muhimmanci na tsaron ƙasa, kuma ba za a iya samunsa ba sai ta hanyar haɗin gwiwar hukumomin gwamnati, shugabannin addini, cibiyoyin ilimi, kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin farar hula.
4. Tattaunawar ƙasa mai haɗa kowa ita ce hanya mafi inganci wajen magance tushen tashin hankali, ƙarfafa amincewa tsakanin al’ummomin addinai da ƙabilu daban-daban, da haɓaka al’adar haɗin gwiwa domin hidimar ƙasa.
5. Akwai matuƙar muhimmanci wajen ƙarfafa tsaron tunani da kare al’umma daga kiraye-kirayen tsattsauran ra’ayi, son zuciya da ƙiyayya, tare da yaɗa matsakaicin tsarin koyar da addini wanda ya ginu a kan hikima, daidaito da tafarkin tsaka-tsaki.
6. Akwai buƙatar ƙarfafa matasa da mata tare da shigar da su cikin shirye-shiryen ƙasa da nufin haɓaka al’adar zaman lafiya, ƙarfafa kishin al’umma da nauyin zama ɗan ƙasa, da kuma tabbatar da kyawawan ɗabi’un zama ɗan ƙasa.
7. Cibiyoyin ilimi da na addini suna da muhimmiyar rawa wajen tarbiyyantar da sababbin ƙarni su mutunta bambance-bambance, su ƙarfafa dabi’un haƙuri da zaman tare, tare da kare asalin ƙasa, yayin da suke riƙe da kuma alfahari da asalin addininsu.
8. Cigaba mai ɗorewa ba ya rabuwa da zaman lafiyar al’umma, yayin da tsaro da kwanciyar hankali su ne muhimman abubuwan da ke samar da yanayin da al’umma za ta bunƙasa kuma ta samu cigaba.
NA BIYU: ƘUDURORI
1. Shugabannin addinai da s**a halarci wannan taro, waɗanda ke wakiltar addinai da mazhabobi daban-daban, sun bayyana aniyarsu ta cigaba da gudanar da tattaunawar hukumomi akai-akai, da ƙarfafa haɗin gwiwa a dukkan abubuwan da za su taimaka wajen haɗin kan al’umma da kare tsaro da zaman lafiyarta.
2. A kafa wata hukumar haɗin gwiwa ta shugabannin Musulmi da Kirista da cibiyoyinsu a Najeriya, tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (MWL), domin daidaita shirye-shiryen haɗin gwiwa da ƙarfafa shawarwari da haɗin kai kan abubuwan da s**a shafi muradun bai ɗaya.
3. A amince da shirin Mai Girma Sakatare-Janar na Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya, Sheikh Dr. Mohammed Al-Issa, mai taken “Nigerian Youth for Peace” (Matasa ’Yan Najeriya Domin Zaman Lafiya).
Shirin zai yi aiki kafada da kafada da hukumar da aka ambata a sama, ya gudanar da ayyukansa a dukkan shiyyoyin siyasa shida na Najeriya, sannan ya yaɗa sak**akon ayyukansa da abubuwan da aka cimma ga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa.
4. A ƙaddamar da shirye-shiryen wayar da kan jama’a a ƙasa baki ɗaya waɗanda za su ƙarfafa kishin ƙasa da jin cewa mutum ɗan ƙasa ne, su haɓaka al’adar mutunta bambance-bambance, da yaƙi da kalaman ƙiyayya da dukkan nau’o’in rashin haƙuri.
5. A yi kira ga kafafen yaɗa labarai da cibiyoyin al’adu da su rungumi yaɗa saƙonnin da ke da alhaki, waɗanda ke inganta zaman lafiyar al’umma, yaƙi da jita-jita da kalaman da ke tayar da hankali, tare da nuna kyawawan misalan haɗin kai, zaman tare da fahimtar juna da ake samu a ƙasa.
6. A tallafa wajen samar da manhajojin karatu da shirye-shiryen horaswa waɗanda za su ƙarfafa dabi’un zama ɗan ƙasa, mutunta juna, tattaunawa da zaman tare, tare da ƙarfafa juriyar tunani da fahimtar matasa wajen fuskantar akidu masu haɗari.
7. A amince da tsarin aiki na haɗin gwiwa tsakanin hukumomin gwamnati, shugabannin addinai da ƙungiyoyin farar hula domin magance ƙalubalen zaman tare, ƙarfafa tsaron tunani da tabbatar da zaman lafiyar al’umma.
Haka kuma, a bibiyi sak**akon yarjejeniyoyin fahimtar juna (MoUs) da aka rattaba hannu a kansu a yayin taron, tare da daidaita shirye-shirye da ayyukan da za su samo asali daga gare su, domin tabbatar da aiwatar da su yadda ya k**ata da kuma cimma manufofinsu.
8. A ƙarfafa haɗin gwiwa a fannonin hana rikice-rikice, kare haɗin kan ƙasa da haɓaka amincewa da juna tsakanin al’umma.
9. A yaba wa ƙoƙarin Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (MWL) wajen inganta tattaunawa tsakanin mabiyan addinai da al’adu daban-daban.
Haka kuma, a yaba wa ƙa’idojin da ke cikin Yarjejeniyar Makka mai tarihi (Charter of Makkah) da kuma Yarjejeniyar Gina Gada tsakanin Makarantu da Mazhabobin Tunani na Musulunci (Charter of Building Bridges between Islamic Schools of Thought and Sects).
A kuma yi kira da a faɗaɗa shirye-shiryen ilimi, horaswa da kafafen yaɗa labarai na MWL ta hanyoyin da za su taimaka wajen haɓaka dabi’un matsakaici, haƙuri, da haɗin gwiwar ɗan Adam da na Musulunci.
A ƘARSHE
Mahalarta taron sun bayyana matuƙar godiya da yabo ga Mai Girma Shugaban Tarayyar Najeriya bisa karamcin da ya yi na ɗaukar nauyin kulawar taron.
Sun kuma nuna godiya ga Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya (MWL) da Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS) ta Najeriya bisa kyakkyawan tsari da shirya taron, da kuma ƙoƙarin gaskiya da s**a yi wajen tabbatar da nasarar taron da cimma manufofinsa.
Haka kuma, sun nuna godiya ga dukkan ƙungiyoyi da cibiyoyin Musulmi da Kirista da s**a ba da haɗin kai, bisa irin gudummawar da s**a bayar da kuma halartar da s**a yi wajen tabbatar da nasarar taron da yaɗa saƙonsa da manufofinsa.
Mahalarta taron sun kuma yaba da kyakkyawan yanayin da ya kasance a dukkan zaman taron, da kuma sahihiyar aniyar da mahalarta s**a nuna wajen ƙarfafa gadojin amincewa da fahimtar juna tsakanin al’ummomin addinai da al’adu daban-daban.
Sun tabbatar da cewa zaman lafiyar al’umma nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa, kuma sahihiyar haɗin gwiwa tsakanin shugabannin addinai, hukumomin gwamnati da ƙungiyoyin farar hula ita ce hanya mafi inganci wajen gina makoma mafi aminci, kwanciyar hankali da wadata.
Sun kuma tabbatar da aniyarsu ta ci gaba da haɗin gwiwa da daidaita ayyuka, tare da mayar da sak**akon wannan taro zuwa shirye-shiryen aikace-aikace da ayyuka masu ɗorewa waɗanda za su ƙarfafa zaman lafiyar al’umma, haɓaka al’adar tattaunawa, tallafa wa tsaro, kwanciyar hankali da cigaba a Najeriya da Afirka ta Yamma. Haka kuma, za su ba da gudummawa wajen gina duniya mai zaman lafiya, adalci da haɗin kai.
Jibwis Nigeria