26/05/2026
SAKO ZUWA GA ALHAZAI DA SAURAN AL’UMMAR MUSULMI BAKI DAYA
“Ina taya dukkan Alhazai murnar samun damar tsayuwa a filin Arfa, wuri mafi girma a cikin ibadun Hajji. Ina roƙon Allah maɗaukakin sarki ya karɓi ibadunsu, ya yafe zunubansu, ya dawo da su gida lafiya cikin rahama da gafara.
Ranar Arfa rana ce mai girma da falala. Rana ce ta yawaita azumi, addu’a, istigfari da ambaton Allah. Don haka ina kira ga sauran al’ummar musulmi da su ribaci wannan rana ta hanyar:
i. Yawaita istigfari da salati ga Annabi ﷺ
ii. Yin azumin ranar Arfa ga wanda ba Alhaji ba
iii. Yin addu’a domin samun zaman lafiya da ci gaban al’umma
iv. Nisantar sabo da ayyukan da ba su dace ba
Ina kuma kira ga al’ummar musulmi da su sanya ƙasarmu Nigeria cikin addu’a, domin Allah ya kawo mana zaman lafiya, ya kawo ƙarshen matsalolin tsaro da wahalhalun rayuwa, ya sanya albarka a cikin ƙasarmu da al’ummarmu baki ɗaya.
Mu ci gaba da kasancewa masu son juna, taimakon juna da kiyaye dokokin Allah domin samun rahama da nasara a duniya da lahira.
Allah ya sa mu dace da falalar wannan rana mai albarka, ya karɓi ibadunmu baki ɗaya.
Barka da Ranar Arfa.” - Sheikh (Dr.) Yakubu Musa Hassan Katsina (Sautus-Sunnah)