17/04/2023
Yazo a cikin littafin Kiyamu Ramadan na Sheikh Muhammad Nasiruddeen Albani, yana cewa: Daren Lailatul Kadri shine daren ashirin da bakwai ga Watan Ramadana, wannan itace magana mafi karfi daga dukkanin naganganun da malamai sukayi, kuma mafi yawancin hadisan da sukazo akan wannan haka suke nunawa, daga cikin wadannan hadisai akwai hadisin da aka rawaito daga Zurru bn Hubaish yace: An baiwa Ubaiyu dan Ka'ab (RA) labari, Abdullahi dan Masa'ud (RA) yana cewa: "Wanda duk ya mike a kowane dare cikin shekara yayi ibada, tabbas zai dace da Lailatul Kadri". Sai Ubaiyu (RA) ya ce: "Allah Ya jikan Abdullahi dan Masa'ud (RA) yana nufin ne kada yasa mutane suyi sakaci su kwanta suki fitowa s**e sai a ranar kaza zasu tashi suyi ibada, don haka ya bar musu wannan mas'ala a rufe, domin suyi ta ibada kawai. Yace na rantse da Allah wanda babu abin bautawa da gaskiya sai shi, Lailatul Kadri tabbas a cikin Watan azumin Ramadana take (mai ruwaya yace Ubaiyu bn Ka'ab rantsuwa yake baya yin ko togaciya), kuma yace na rantse da Allah, Ni nasan kowanne darene daren Lailatul Kadri, shine daren da Manzon Allah (SAW) Ya umarcemu damu tashi muyi ibada a cikinsa, shine daren da safiyar zata waye a ashirin da bakwai.
Falalar wannan daren mai girma ne, Saboda cikinsa aka saukar da Al-kur'ani wanda shine jagoran wanda yayi riko da shi zuwa ga hanyoyin daraja da karamci, kuma ya daga shi zuwa ga tsororuwan girma da dauwama.
Ya isa matsayi ga daren "Lailatul Kadir" cewa ya fi wata dubu alheri, da fadin Allah Ta'ala: "Hakika mu ne muka saukar da shi cikin lailatul kadari, menene ya sanar da kai abin da ake kira lailatul kadari, lailatul kadari yafi Alkhairi sama da watanni dubu. Mala'iku suna sauka da Ruhu (Jibrilu) cikinsa da izinin Ubangijisu da ko wane Umarni, Aminci ne shi har fitowar Alfijir". [Alkadr:1-5].
Kuma cikin lailatul kadir ake rarrabe Al'amura bayyanannu na hikima, da fadin Allah Ta'ala: "Lalle ne Mu muka saukar da shi a wani dare mai albarka. Lalle Mu mun kasance masu yin gargadi. A cikinsa (shi daren) ake rarrabe kowane al'amari da ake hukuntawa. Umarni ne daga wurinmu. Lalle mune muka kasance masu aikawa. Rahama daga Ubangijinka, hakika shine Mai ji Masani". [Addukhan: 3-6].
🔊TA YAYA MUSULMI ZAI NEMI LAILATUL KADRI:
Lalle wannan dare mai albarka wanda duk aka haramtawa an haramta masa alkhairi dukansa, kuma babu wanda za'a haramta masa alherin wannan dare sai ma shakiyi mara arziki. Saboda haka ake son Musulmi ya dage wajen biyayyar Ubangiji, ya raya dararen yana mai imani da kwadayin lada mai girma, idan ya aikata haka Allah zai gafarta masa abin da ya gabata na zunubansa. Da fadin Annabi (SAW) cewa: "Wanda ya sallaci daren Lailatul Kadri yana mai imani da neman lada za a gafarta masa abin da ya gabata na zunubansa." [Bukhari (4/217) Muslim (759)].
Kuma ana so a yawaita addu'a cikin daren, domin ya zo daga Nana A'isha (RA) tana cewa, "Na ce wa Manzon Allah (SAW) yaya kake gani idan na gane Lailatul Kadri me zan fada a ciki? Sai yace: ki fadi:
"ALLAHUMMA INNAKA AFUWWUN, TUHIBBUL-AFWA, FA'AFU ANNI"
Ma'ana: "Ya Ubangiji kai ne mai yawan Afuwa, Kana son Afuwa, Ka yi min Afuwa." [Tirmizi (3760) Ibn Majah (3850)].
🔊DAGA ALAMOMINTA:
Ka sani ya kai dan uwa cewa an wassafa safiyar daren Lailatul Kadri saboda musulmi su san wane dare ne ita, k**ar haka:
Daga Ubayyu (RA) yace: "Manzon Allah (SAW) ya ce: "Safiyar Lailatul Kadri rana 🌕 tana fitowa babu haske sosai, k**ar wata langar tasa ce har ta d**o sama." [Muslim (762)].
Daga Abu Huraira (RA) yace: "Mun yi Muzakarar Lailatul Kadri wajen Annabi (SAW) sai yace: "Waye daga cikinku zai tuna lokacin da wata 🌙 ya fito, yana k**ar yankin akushi?" [Muslim (1170)].
Daga Ibn Abbas (RA) yace: "Manzon Allah (SAW) yace: "Daren Lailatul Kadri dare ne mai walwala 🏡 a sake babu zafi babu sanyi, rana tana fitowa a safiyarsa mai rauni ja-ja ja-ja 🌇.
👉TAMBIHI:
Daga wadannan hadisai ne zamu gane cewa abubuwan da ake fada na cewa idan daren ya yi, ana ganin bishiyoyi 🌴🌴 sun kwanta, ko ana iya hango ka'aba, ko gidaje 🏠🏠 suna kwanciya da dai sauran abubuwan da ake fada wadanda basu da asali a addini, duk abubuwa ne da ya k**ata mu watsar, mu k**a wanda ya zo daga fiyayyen halitta (SAW) wanda ba ya fadar abinda yake son zuciya, duk abinda ya furta wahayi ne daga Ubangijin kowa da komai.
ALLAH (SWT) YA SA MU DACE, AMIN.