First Aid Group Of Jibwis Kano

First Aid Group Of Jibwis Kano This group is meant to enlighten, educate, develop and uniting the KANO JIBWIS AIDERS

Allah Ya Taimaki Maigidanmu Maganin Kukanmu Allah Ya Karawa Rayuwa Albarka,Allah Ya Kawo Babban Rabo,Allah Ya Biya Bukat...
23/07/2026

Allah Ya Taimaki Maigidanmu Maganin Kukanmu
Allah Ya Karawa Rayuwa Albarka,
Allah Ya Kawo Babban Rabo,
Allah Ya Biya Bukata,
Allah Ya Ida Nufi,
Allah Ya Kara Lafiya,
Allah Ya Shiga Dukkan Lamuranka
AMEEN.

Sheikh, Gwani, Malam, Alaramma, Gangaran, Farfesa, Abdullahi Saleh Usman Pakistan JP
Jibwis Kano State 001

Sheikh Farfesa Abdallah Saleh Usman Pakistan JP Yana Gayyatar Daurin Aure Shugaban Kungiyar Izala Na Tarayyar Najeriya R...
22/07/2026

Sheikh Farfesa Abdallah Saleh Usman Pakistan JP Yana Gayyatar Daurin Aure

Shugaban Kungiyar Izala Na Tarayyar Najeriya Reshen Jihar Kano Sheikh Farfesa Abdallah Saleh Usman Pakistan JP yana gayyatar 'ya'yan Kungiyar a dukkan matakai musamman na jihar Kano daurin auren Malam Kamaldeen Adamu Gwarzo mataimakin Sakataren majalisar Agajin kungiyar izala ta kasa reshen jihar kano wanda zai gudana a ranar Juma'a 30/07/2026 a masallacin Izala na Karamar Hukumar Kura dake Jihar Kano da Misalin Karfe 1:00pm bayan sallar Juma'a.

Allah ya bada ikon halarta
Allah ya sanya Albarka.
AMEEN.

Tawagar Malaman Jibwis Ta chilla zuwa ƙasar Ghana domin gudanar da Da'awa na wasu kwanki. Allah ya dawo da su lafiya. Am...
12/07/2026

Tawagar Malaman Jibwis Ta chilla zuwa ƙasar Ghana domin gudanar da Da'awa na wasu kwanki. Allah ya dawo da su lafiya. Amin.

Sanarwa! Sanarwa!! Sanarwa!!!Insha Allah A Daren Yau Lahadi 05/06/2026 Da Misali Karfe 8:00pm Babban Malami Kuma Sakatar...
05/07/2026

Sanarwa! Sanarwa!! Sanarwa!!!

Insha Allah A Daren Yau Lahadi 05/06/2026 Da Misali Karfe 8:00pm Babban Malami Kuma Sakataren Kungiyar Izala Na Tarayyar Najeriya Sheikh Dr Muhammad Kabir Haruna Gombe Zai Gabatar Da Shiri Na Musamman A Gidan Talabijin Na ARTV KANO Dake Jihar Kano.

Allah Ya Karawa Rayuwar Malam Albarka.
AMEEN.

Abubakar Bello

Sanarwa Ga Jama'a 17 Muharram, 1448AH / 02 July, 2026.Daraktan Agajin Kano Na Gayyatar Daurin Auren Sakataren Tsare-Tsar...
02/07/2026

Sanarwa Ga Jama'a
17 Muharram, 1448AH / 02 July, 2026.

Daraktan Agajin Kano Na Gayyatar Daurin Auren Sakataren Tsare-Tsare Na Jihar Kano

Daraktan Agajin Kungiyar Izala ta kasa reshen jihar kano Malam Mukhtar Lawan Tudun Wada yana gayyatar yan Agaji da ilahirin al'umma musamman na jihar Kano daurin auren Malam Nura Suleiman Ungogo SakatarenTsare-Tsaren majalisar Agajin kungiyar izala ta kasa reshen jihar kano wanda zai gudana a ranar Lahadi 05/07/2026 a Garin Zaria dake jihar Kaduna.

Allah ya bada ikon halarta
AMEEN.

Sanarwa:
DSP A. Bello
Babban Jami'i,
Sashen Yaɗa Labarai Da Hulɗa Da Jama’a Na
Majalisar Agajin Izala Ta Jihar Kano.

KHUƊABAR 🕋JUMA'A DAGA MASJID 🕋ABIY AYUBAL🕋 ANSARIY DAKE R/LEMO 🕋YANKATAKO 🕋DALA L.G 🕋KANO🕋                              ...
27/06/2026

KHUƊABAR 🕋JUMA'A DAGA MASJID 🕋ABIY AYUBAL🕋 ANSARIY DAKE R/LEMO 🕋YANKATAKO 🕋DALA L.G 🕋KANO🕋

🕌 MAI TAKEN🕌
WAƘAFI TUSHEN KAWAR TA TALAUCI A CIKIN AL-UMMA.

Shiikh Imam Ali Aliyu Jp (Hafizahullahu wa ri'ahu) ne yagabatar da wanan khudba mai albarka.

🪻Malam ya bude khudbar ne da yabo ga Allah ta'ala mai sakko da ruwan sama cikin wasu kalmomi masu banƙayen saurare tare da salati da taslimi ga Annabi (S.A.W).

Malam yayi khubar ne karƙashin fadin Allah (S.W.T)
{ لَن تَنَالُوا۟ ٱلۡبِرَّ حَتَّىٰ تُنفِقُوا۟ مِمَّا تُحِبُّونَۚ وَمَا تُنفِقُوا۟ مِن شَیۡءࣲ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِهِۦ عَلِیمࣱ }
[Surah Āli-ʿImrān: 92]

🪻Malam ya fassara wanan Aya mai labarka da cewa: Baza ku samu nagartaba har sai kun ciyar da abin da kuke so..

🪻Malam ya zaburar da masallata mahimmancin fitar da dukiya domin Allah.

🪻Malam ya kara karanto fadin Allah
{ ٱلَّذِینَ یُنفِقُونَ أَمۡوَ ٰ⁠لَهُمۡ فِی سَبِیلِ ٱللَّهِ ثُمَّ لَا یُتۡبِعُونَ مَاۤ أَنفَقُوا۟ مَنࣰّا وَلَاۤ أَذࣰى لَّهُمۡ أَجۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ وَلَا خَوۡفٌ عَلَیۡهِمۡ وَلَا هُمۡ یَحۡزَنُونَ }
[Surah Al-Baqarah: 262]
Tare da jan hankalin masallata da su guji gori domin yana rusa ayyuka.

🪻Malam ya ja hamkalin masallah akan wadanan Ayoyi masu girma tare da takaice bayani sabo da lokaci

{ ۞ قَوۡلࣱ مَّعۡرُوفࣱ وَمَغۡفِرَةٌ خَیۡرࣱ مِّن صَدَقَةࣲ یَتۡبَعُهَاۤ أَذࣰىۗ وَٱللَّهُ غَنِیٌّ حَلِیمࣱ (263) یَـٰۤأَیُّهَا ٱلَّذِینَ ءَامَنُوا۟ لَا تُبۡطِلُوا۟ صَدَقَـٰتِكُم بِٱلۡمَنِّ وَٱلۡأَذَىٰ كَٱلَّذِی یُنفِقُ مَالَهُۥ رِئَاۤءَ ٱلنَّاسِ وَلَا یُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ وَٱلۡیَوۡمِ ٱلۡـَٔاخِرِۖ فَمَثَلُهُۥ كَمَثَلِ صَفۡوَانٍ عَلَیۡهِ تُرَابࣱ فَأَصَابَهُۥ وَابِلࣱ فَتَرَكَهُۥ صَلۡدࣰاۖ لَّا یَقۡدِرُونَ عَلَىٰ شَیۡءࣲ مِّمَّا كَسَبُوا۟ۗ وَٱللَّهُ لَا یَهۡدِی ٱلۡقَوۡمَ ٱلۡكَـٰفِرِینَ (264) }
[Surah Al-Baqarah: 263-264]
{ یَـٰۤأَیُّهَا ٱلَّذِینَ ءَامَنُوۤا۟ أَنفِقُوا۟ مِن طَیِّبَـٰتِ مَا كَسَبۡتُمۡ وَمِمَّاۤ أَخۡرَجۡنَا لَكُم مِّنَ ٱلۡأَرۡضِۖ وَلَا تَیَمَّمُوا۟ ٱلۡخَبِیثَ مِنۡهُ تُنفِقُونَ وَلَسۡتُم بِـَٔاخِذِیهِ إِلَّاۤ أَن تُغۡمِضُوا۟ فِیهِۚ وَٱعۡلَمُوۤا۟ أَنَّ ٱللَّهَ غَنِیٌّ حَمِیدٌ }
[Surah Al-Baqarah: 267].

🪻Malam yayi bayani akan me ake nufi da waƙafi tare da bayanin mahimancinsa ga alumma.

🪻Malam ya tunatar da yan uwansa malamai akan su rinka tunatar da mawata mahimmancin waƙafi a cikin alumma.

🪻Malam yace wakafi shine sadaukar da wata dukiya mara motsi ko mai motsi ga Alumma kamar gidan saukar baki rijiya, makarnta, daukar nauyin a bangaren ilimi,lafiya.. da niyyar samun lada.

🪻Malam ya karanto hadith wanda mazanon Allah (S.A.W) yace: Idan dan adam ya butu dukkanin ayyukansa sunyanke sai dai guda uku
1)Dadaƙa mai gudana ( Kamar waƙafi)
2)Ilimin da ake amfani dashi( yada ilimi da koyar dashi)
3)Ɗa nagari da yake masa Addu'a.
Da malam ya zo na ukun cikin hikma yai gargadi ga alumma da su zamo masu kula da tarbiyyar ỳaya.

🪻Malam ya ambaci wani hadith wanda ya kawo Abubuwa guda bakwai wadanda ake sadaƙa jariya dasu.

🪻Malam yayi bayani kan raba-raben waƙafi
Akwai amm wato
( Na gamagari ) akwai kuma kass (wato kebantacce wanda yana da shruda da ka idoji)
ina ya dauki waƙafi na Ahli yai bayani akai daga ciki yake cewa yana kara albarka ga ahli da son juna kuma yana rage barace barace acikin almmma kuma aiki ne da fadin Allah ta'ala
وَتَعَاوَنُوا۟ عَلَى ٱلۡبِرِّ وَٱلتَّقۡوَىٰۖ وَلَا تَعَاوَنُوا۟ عَلَى ٱلۡإِثۡمِ وَٱلۡعُدۡوَ ٰ⁠نِۚ
A karshe malam ya tunatar da masallata mahimmancin mallakar katin zaɓe (Ƙuri'a) tare da bada shara a mallaka dakuma bada dalilai da za su sa mutum yaje yayi daga ciki yace

1)Mallakar katin zabe yana kara habbaka yawan Musulmai.

2)Yana bada damar cin moriyar gwamnati domin suna saka sharɗi akai.

3) Yana bada damar cin nasara ga wanda kake so ya kasance shugabanka.

4) Yana bada dama ka daƙile wanda kake hamayya..

Malam ya rufe khubar da Adduoin alkhairi da salati da taslimi ga manzon Allah (S.A.W).

Muna rokon Allah ya sakawa Iyayenmu da Malamanmu da Alkhairi.

✍️Ghali Khamis Abubakar
26/6/2026.

Yan Agajin Izala Na Jihar Kano Sun Gudanar Da Aikin Tsaftace Babban Asibiti A Jihar Kano'Yan Agajin Izala na jihar Kano ...
23/06/2026

Yan Agajin Izala Na Jihar Kano Sun Gudanar Da Aikin Tsaftace Babban Asibiti A Jihar Kano

'Yan Agajin Izala na jihar Kano Karkashin Jagorancin Daraktan Agajin Kano Malam Mukhtar Lawan Tudun Wada sun gudanar da aiki tsaftace Babban Asibitin garin Tudun Wada a Karamar Hukumar Tudun Wada dake jihar kano Kamar yadda s**a saba gudanar lokaci bayan lokaci.

Aikin Agaji ba iya kula da Masallaci ko zuwa Wajen wa'azi ya takaita ba, 'yan Agaji kan dukufa wajen taimakawa al'umma musamman a bangaren addini da mu'amalar yau da kullum domin samun al'umma ta gari.

Izala Ikon Allah
Dan Agaji Bawan Allah

Abubakar Bello

Sanarwa Ga Jama'a 05 Muharram, 1448AH / 20 June, 2026Daraktan Agajin Izala na Jihar Kano ya mika sakon ta'aziyya ga Shei...
20/06/2026

Sanarwa Ga Jama'a
05 Muharram, 1448AH / 20 June, 2026

Daraktan Agajin Izala na Jihar Kano ya mika sakon ta'aziyya ga Sheikh Farfesa Pakistan

Daraktan Agajin Izala na Jihar Kano Malam Mukhtar Lawan Tudun Wada ya mika sakon ta'aziyya ga shugaban Kungiyar Izala na kasa reshen jihar kano Kuma tsohon Shugaban Hukumar aiki Hajji na tarayyar Najeriya Sheikh Farfesa Abdallah Saleh Usman Pakistan JP bisa rasuwar mai dakin shehin Malamin wato Hajiya Zainab sakamakon rashin lafiya.

Sakon ta'aziyyar da daraktan ya mika a madadin 'yan Agajin Izala na Jihar kano baki daya musamman ga 'ya'ya 'yan uwa da iyalan Shugaban Izala na kano Sheikh Farfesa Pakistan.

Daga karshe Daraktan Yayi Addu'ar neman samun Rahamar Ubangiji gareta.

Allah ya mata Rahma yasa Aljannah ce makoma gareta.
AMEEN.

Sanarwa:
DSP A. Bello
Babban Jami'i,
Sashen Yaɗa Labarai Da Hulɗa Da Jama’a Na
Majalisar Agajin Izala Ta Jihar Kano.

Address

Sheikh Ja'afar Mahmud Juma'at Masjid Tudun Murtala Kano
Kano
064

Telephone

+2348161616461

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when First Aid Group Of Jibwis Kano posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to First Aid Group Of Jibwis Kano:

Shortcuts

Share