24/01/2026
https://www.facebook.com/share/p/1Khcne6WmC/
Ubayy bn Ka‘b ya ce yana yawan yin addu’a, sai ya ce wa Annabi ﷺ:
“Ya Rasulullah, ina yawaita yin salati a gare ka. Zan sanya kaso nawa daga addu’ata ya zama salati gare ka?”
Annabi ﷺ ya ce: “Yadda kake so.”
Ubayy ya tambaya:
“Idan na sanya kashi ɗaya bisa huɗu?”
Annabi yace: “Yadda kake so, idan ka ƙara yana da alheri gare ka.”
“Idan rabinsa?”
Annabi yace: “Idan ka ƙara yana da alheri gare ka.”
“Idan kashi biyu cikin uku?”
Annabi yace: “Idan ka ƙara yana da alheri gare ka.”
Sai Ubayy yace:
“To idan na sanya dukan addu’ata salati gare ka?"
Annabi ﷺ yace:
“To Allah zai wadatar maka damuwarka, kuma Ya gafarta maka zunubanka.”
Hadisi (Tirmidhi 2457 – Hasan Sahih).