18/05/2026
GOMAN FARKON ZHUL-HIJJA, MU JIƘA HARSHENMU DA AMBATON ALLAH (1)
An karɓo daga Abdullahi ɗan Umar Allah ya yarda da shi cewa, Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama ya ce: "Babu wasu kwanaki (yini) da s**a fi girma a wurin Allah, sannan kuma ayyuka a cikinsu (na alkhairi) s**a fi soyuwa a gare Shi sama da waɗannan kwanaki goma (goman farko na Zhul-hijja), dan haka ku yawaita a cikinsu daga Hailala da Hamdala da Kabarbari". Imamu Ahmad ya fitar da shi, 5446.
Daga cikin salon yin waɗannan zikirai:
*اللهُ أكبرُ اللهُ أكبرُ، لا إلهَ إلَّا الله، واللهُ أكبر اللهُ أكبر، ولله الحَمد.
* الله أكبر الله أكبر الله أكبر، لا إله إلا الله، الله أكبر الله أكبر الله أكبر ولله الحمد.
An rawaito cewa Abdullahi ɗan Umar da Abu Hurairah Allah Ya ƙara yarda a gare su, sun kasance suna fita kasuwanni a kwanaki goman farko na Zhul-hijja suna Kabarbari, sai mutane su yi Kabarbari sakamakon jin ta su. Dan haka mu tunatar da juna wannan alkhairi.
🖊Zainab Ja'afar Mahmud
1st Zhul-hijjah 1447A.H