Baye Niasse Production

Baye Niasse Production Wannan shafi an ginata ne domin samun labarai da karatu(video da audio) wadanda s**a shafi Dariqar Tijjaniyya da Musulunci gabadaya

Ka fadi wani abu akan wannan hoton❤️❤️
17/01/2024

Ka fadi wani abu akan wannan hoton❤️❤️

Wannan ne takalmin da Manzon Allah (saww), ya saka a lokacin rayuwar sa. Takalmin yana gidan ajiye kayan tarihi. Don All...
15/09/2020

Wannan ne takalmin da Manzon Allah (saww), ya saka a lokacin rayuwar sa. Takalmin yana gidan ajiye kayan tarihi. Don Allah kayi comment da Sallahu Alaili Wasallam, katurawa ↪ group 5 sannan kayi liking 👍wannan page

Allah ya yaye mana kuncin rayuwa don albarkan wannan takalmin. Amiin saboda ﷺ.

GARABASA ME TARIN YAWA DAGA BAKIN FIYAYYEN HALITTA. Daga Umar ChobbeDuk wanda ya manta da Allah to shima Allah zai manta...
15/09/2020

GARABASA ME TARIN YAWA DAGA BAKIN FIYAYYEN HALITTA.

Daga Umar Chobbe
Duk wanda ya manta da Allah to shima Allah zai manta da shi
ANNABI S. A. W. Yace duk wanda ka ganshi yana zaune yana jiran SALLAH ta zo ta same shi a masallaci ko a gidanta ta/ya yi Alwala yana jiran lokachin SALLAH yayi don yayi sallar.
ANNABI S.A.W yace irin wadannan mutanen koda ka gansu a waje suna aikata wani aiki na laifi to kayi musu uzuri maganar imani karka hada kanka da su domin sun fika imani,
Duba cikin "kitabul ta'allimun".
Duk wanda yace "Subhanallahy Wal Hamdu LILLAHY WA Laa Ilaaha Illallahu Wallahu Akbar" sau dari (100) da safe, Dari (100) da yamma za a gafarta masa zunubai guda dari, za a bashi ladan yayi sadaqah da jajayen rakumai guda dari (100) kuma za a rubuta cewa kowanne rakumi yana dauke da kayan abinci a kansa, sannan za a rubuta masa ya "yanta bayi guda dari (100) kuma darajar bayin ta kai darajar yayan Annabi Sulayman A. S.
ALLAHU TA'ALA Akbar kabeeran!
Allah bai sanya wannan GARABASA a ko ina ba sai a addinin musulunchi addini cikakke.
Allah ya bamu daman jiran lokacin Sallah a ko wani Rana Albarkan ANNABI S.A.W

SHUGABAN MAJALISAR SHURA TA DARIQAR TIJJANIYYA Khalifa Sheikh Kabiru Salga A Madadin Mai Martaba Sarkin Kano.  Alhaji Am...
15/09/2020

SHUGABAN MAJALISAR SHURA TA DARIQAR TIJJANIYYA

Khalifa Sheikh Kabiru Salga

A Madadin

Mai Martaba Sarkin Kano.

Alhaji Aminu Ado Bayero.

Na Gayyatar dukkanin Yan Uwa Musulmi Musanmman Yan Darikar Tijjaniyya

zuwa

GAGARIMIN ZIKIRIN JUMA'A DA YIWA QASA ADDU'A

kamar yadda aka saba duk Shekara....

Babban Bako

Mai Girma Gwamnan Jahar Kano.
Dr Abdullahi Umar Ganduje Da sauran Gwamnonin kasar nan.

Taron Zai hada da
- Manyan Shehunnai.
-Manyan Malamai.
-Muqaddamai.
-Limammai. Da
-Sarakuna.
Za'ai wannan Tarone kamar Haka............
*Juma'a 30,muharam-1442
Dai-dai da18-09-2020
*Lokaci 4:30 Na yamma.
* Wuri. Kofar kudu fadar mai martaba Sarkin Kano.

Sanarwa Daga
Sakataren Majalisar Shura.
Barr Habib Muhd Dan Almajiri.

Yadawa
SSA Broadcast
Alh Abubakar Balarabe kofar Na'isa

SUWAYE 'YAN DARIQAR TIJJANIYYA???'Yan Dariqar Tijjaniyya Wasu Mutane Ne Da:(1). Suke suna cikin Ahlus Sunnah wal jama'a ...
14/09/2020

SUWAYE 'YAN DARIQAR TIJJANIYYA???

'Yan Dariqar Tijjaniyya Wasu Mutane Ne Da:

(1). Suke suna cikin Ahlus Sunnah wal jama'a na sahun gaba.

(2). Mafi yawancin su suna biyar mazhabar malikiyyah ne, amma daga cikin su akwai masu biyar sauran mazhabobin fiqhu, kamar shafi'iyyah, da hanabila.

(3). Sun imani da Allah da manzon sa, da mala'ikun sa, da littattafan sa, da manzannin sa, da qadra ta alkhairi ko ta sharri, sun Kuma Yi imani da ranar qarshe.

(4). Sun shaida babu abun bautawa na gaskiya sai Allah, Kuma Annabi Muhammad manzon sa ne, suna yin sallah, suna bayar da zakka, suna yin azumin watan Ramadan, suna zuwa aikin hajji.

(5). Suna Kusantar Allah da abubuwan da ya wajabta musu, sannan suna yin qari da nafiloli domin samun qarin kusancin Allah.

(6). Suna kyautata zato ga dukkan musulmai, basa yiwa Allah da manzon sa shisshigi.

( 7). Basa kafirta musulmai, basa Kuma shiga tsakanin su da Allah, duk mai fadin la'ilaha illallahu musulmi ne a wajen su.

(8). Sun Yi imani da cewa duk Wanda ya Yi da'awar ya fi wani Annabi to wannan maqaryaci ne kafiri.

(9). Sun tabbatar da cewa salatul fatihi bata kai Alqur'ani ba b***e ta fi shi.

(10). Sun Yi imani da cewa Alqur'ani shine fiyayyen zance, Kuma harafi daya daga cikin sa baya zuwa dai dai da wani Abu ko menene.

(11). Sun Yi imani da cewa duk Wanda ya Yi iqirarin cewa manzon Allah boye wani Abu da Allah ya umurce shi ya Isar to wannan maqaryaci ne kafiri.

(12). Sun amince da cewa duk Wanda ya ce ana Yi masa wahayi ta kowace fuska to wannan maqaryaci ne kafiri.

(13). Sun Yi imani da cewa duk Wanda ya ce wani wuridi ya fi Alqur'ani to wannan maqaryaci ne kafiri.

(14). Sun tabbatar da cewa duk Wanda ya ce wani mutum ya fi sahabban manzon Allah to wannan batacce ne.

(15). Sun imani da cewa duk Wanda ya zagi sahabban manzon Allah ko ya tauye matsayin su to wannan kafiri ne.

(16). Suna son iyalan gidan manzon Allah da sahabban sa, basa banbance tsakanin su.

(17). Sun ambayon Allah a kowane hali, Kuma suna yin umurni da yin zikirin

(18). Sun tabbatar da cewa sahabban manzon Allah adilai duk, Kuma basa shiga cikin abun da ke faruwa a tsakanin su na rikici

(19). Basa Kiran sunan kowane sahabi har sai in Alkhairi zasu fadi a game da shi

(20). Kuma masadirut tashree'e wadanda aka Yi ittifaqi a kan su sune Alqur'ani da hadisi da ijma'in malamai, sune qaluluwar hujja a wajen su, sun yarda duk hujjar da ba wannan ba batatta ce

(21) Suna karanta Alqur'ani Suna hukunci da shi.

idan bakasan suwaye 'yan darika tijjaniya to yau kasani idan wani yatambayeka to ga amsa dazaka bachi

idan kaji dadin karanta wannan post to katurawa sauran groups din musulmai Suma su karanta su karu da kai

Allah duk wanda yatura wannan post zuwa cikin wani groups kabiyachi da kyautar gida Achikin Aljanna Alfarman Annabi ((muhammadu s,a,w))

idan baka cikin wannan page kayi like 👍 and following ✔

wannan rijiyan dakuke gani itaci rijiyan da manzan Allah yafara shan ruwanta agarin madina Allah sarki Dan Adam in kaji ...
14/09/2020

wannan rijiyan dakuke gani itaci rijiyan da manzan Allah yafara shan ruwanta agarin madina Allah sarki Dan Adam in kaji daadin ganin rijiyan kayi comment da (SAW) kayi Share a group 5 dan annabi saw

Dan allah kayi like wannan page👇

ALLAH AKBAR inamasu kishin Annabi Wannan shine makwancin daya daga cikin matayen manzon Allah SAW, Sayyada Maimuna. Loka...
14/09/2020

ALLAH AKBAR inamasu kishin Annabi Wannan shine makwancin daya daga cikin matayen manzon Allah SAW, Sayyada Maimuna. Lokacin da Sayyada Maimuna zata bar duniya tayi wasika cewa idan ta mutu a birne gawar ta a daidai wurin da s**a yi daren farko da manzon Allah saw. Idan kai cikaken masoyin manzon Allah da iyalan gidansa ne kayi Comment da saw sannan kayi share a groups 5 kayi like ko followin wannan page

NEMAN ALBARKAR ANNABI S,A,W Dan Girman Annabi kayi share wannan Rubutu zuwa groupa 5An ruwaito daga Safiyyah bintu Najda...
10/09/2020

NEMAN ALBARKAR ANNABI S,A,W Dan Girman Annabi kayi share wannan Rubutu zuwa groupa 5

An ruwaito daga Safiyyah bintu Najdah (ra) cewa KHALID BN WALID (ra) ya kasance yana da wasu gashi daga cikin sumar Manzon Allah (saww) wadanda ya sanya acikin hularsa. Duk lokacin da zai fita wajen yaki yakan sanya wannan hular akansa.

Rannan sai hular ta fadi awajen wani daga cikin Yakokinsa. Sai KHALID din ya sanya aka koma aka ci gaba da yakin har sai da aka dauko wannan hular. Da sauran Sahabbai s**a tuhumeshi akan dalilin da yasa yayi Umurnin akoma wannan yakin, Sai Khalid yace musu "ACIKINTA AKWAI SUMAR MANZON ALLAH (SAWW) NE. SHI YASA NAYI KOKARI NA KOMA NA DAUKOTA. SABODA KAR TA FADA HANNUN KAFIRAI, NI KUMA IN RASA ALBARKARTA".
- Aduba cikin ASH-SHIFA ta Alqadhiy Iyaadh (rah) juzu'i na farko shafi na 619.

Wannan hadisin Hujjah ce akan halaccin neman albarkar MA'AIKI (saww). Da kuma halaccin rikon wani abu wanda yake da Alaqah da MA'AIKI (saww) domin neman albarkarsa.

Kwanakin baya ma mun kawo wani hadisi Sahihi wanda ya nuna cewar Sahabbai s**an tsoma gashin Manzon Allah (saww) acikin ruwa, sannan su sha ruwan domin neman waraka daga cututtuka.

Dan Allah idan baka cikin wannan page kayi like ko following kaciha kayi share a groups 5 dan annabi

Allah shi bamu albarkarsa (saww).🙏🙏🙏
Ameeen

Don Allah ware minti 1 kakaranta kayi share a groups 3 don hasken fuskar annabi Muhammad saw Aranar da za'a fita zuwa ya...
10/09/2020

Don Allah ware minti 1 kakaranta kayi share a groups 3 don hasken fuskar annabi Muhammad saw

Aranar da za'a fita zuwa yaqin badar, lokacin da Annabi (saww) ya sanar da Sahabbai cewa duk wanda yake da iko ya fito a tafi, wani baqon al'amari mai ban mamaki ya faru tsakanin Wani Sahabi mai suna Sa'adu bn Khaythamah da mahaifinsa Khaythamah bn Harith (Allah ya yarda dasu).

Yayin da sanarwar fita yaqin tazo kunnensu sai Khaithamah din ya kira 'dansa yace masa "Ya kai 'dana! Hakika ayau din nan sai 'dayan cikinmu ya fita, 'daya kuma ya zauna a gida ya kula da Mata da Qananan yara. Don haka ni zan fita (zuwa badar din) kai kuma ka zauna agida ka kula da Mata da Qananan yara".

Sai Sa'adu yace "Ya Babana! Wallahi wannan ba zai yiwu ba. Domin ni nafi ka kwadayin fita yaqin, Kai kuma kafi ni bukatuwa zuwa ga zaman gida. Don haka ni zan fita kai kuma ka zauna agida".

Sai Baban yace "Ya kai Sa'adu sa'ba mun zakayi? Wato ba zaka bi umurnina ba!!".

Sai Sa'adu yace "Hakika Allah ya riga ya wajabta mun fita Jihadi kuma ga Manzonsa nan (saww) yayi kirana. Shin kana so inyi maka biyayya kuma in sa'ba wa Allah da Manzonsa kenan?".

Sai Baban yace "Ya kai 'dana! Tunda dai babu makawa sai 'dayan cikinmu na fita, to ina so kayi hakuri ka barni ni inje".

Sai 'dan yace "Ya babana! Da ache ba Aljannah ce take kiranmu ba, da na kyaleka kaje ni in zauna din".

Khaysamah (shi Mahaifin kenan) bai yarda ba har sai da s**ayi Quri'ah atsakaninsa da 'dan nasa, Sai 'dan yaci Quri'ar kuma ya fita zuwa Yaqin Badar.

Yayi yaqi sosai har sai da yayi shahadah a badar din. To yayin da Babansa ya samu labarin mutuwarsa yayi bakin ciki mai tsanani. Ba wai baqin cikin rabuwa da 'dansa ba. A'a bakin ciki ne bisa kansa. Cewa inama shine ya fita yayi shahadar nan!!. ALLAHU AKBAR !!!.

Yayin da ranar yaqin uhudu tazo, Khaythamah (radhiyallahu anhu) ya fito da shirin tafiya yaqin sai Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) bai bashi dama ba. (Watakil ko saboda tsufa ko kuma wani dalilin mai karfi).

Nan take sai ya fashe da kuka! Yace "Ya Rasulallahi hakika ban samu fita Yaqin badar ba, duk da cewa nayi kwadayin hakan. Saboda tsananin kwadayin fitan har sai da mukayi Quri'ah atsakanina da 'dana. Shi yaci Quri'ar ya fita kuma Allah ya azurtashi da samub shahadah. ..

To hakika a daren yau na ganshi acikin mafarkina yana ce mun "Taho garemu ka riskemu ka zama abokin tafiyarmu acikin Aljannah. Domin hakika mun samu duk abinda Ubangijinmu yayi mana alkawari cewa gaskiya ne".

To wallahi Ya Ma'aikin Allah hakika yau na wayi gari ina jin shauqin riskuwa dashi. Duk da cewa hakika shekaruna sub yawaita, kuma qashin jikina yayi rauni. Amma ina mutukar son gamuwa da Ubangijina".

To daga jin wannan sai Annabi (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya bashi damar fita wajen Yaqin Uhudu. Yaje ya nuna jarumtakarsa sosai. Yayi yaqi har sai da yayi shahadah. Qaton Kafirin nan mai suna Amru bn Abdu wuddin ne ya kasheshi. Shi kuma Sayyiduna Aliyu (Karramal Lahu Wajhahu) ya kashe wannan kafirin aranar yaqin Khandaq (yaqin gwalalo).

Allahu Akbar!! 'Yan uwa kunji fa irin halayen Sahabban Shugaba (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) wadanda s**a fifita mutuwa afagen daukaka addinin Allah, da kuma kare lafiyar Manzon Allah (saww) fiye da komai.

Sun bama Allah kyautar dukiyoyinsu da basirorinsu da Qarfinsu, karshe ma har rayukansu suke rige-rigen bayarwa domin Allah da Manzonsa (saww).

Ya Allah ka saka musu da alkhairi, ka Qara yardarka garesu, ka bamu albarkarsu, ka riskar damu zuwa garesu cikin aminci. Kada ka karbi rayukanmu har sai mun samu yardarka cikin falalarka da rahamarka Ya Mafi Karamci da Girman daraja! Ameen.

Dan girman Annabi idan kayi ido biyu da wannan rubutu Katurasu a groups 3uku Kuma idan baka cikin wannan page kayi like kaciga Dan Alfarman Annbi da alqur'ani

Dan girman Allah kadaka wuce bakayi like wannan page👈

Idan kana son Annabi Muhammad (S_A_W) katura zuwa groups guda goma (10)kacal domin 'Yan uwa Muslimi su Amfana, Idan s**a...
10/09/2020

Idan kana son Annabi Muhammad (S_A_W) katura zuwa groups guda goma (10)kacal domin 'Yan uwa Muslimi su Amfana, Idan s**a karanta wannan addu' ar👇👇
[Allahummah inni as'aluka minal khairi nabiyyuka wa habibuka Mohammadin (S_A_W) wa'a uzubika Minas'Sharri masta'azka minhum nabiyyuka wa habibuka Mohammadin (S_A_W)
Ka gaggauta tura wa 'Yan uwa Muslimi a groups dan ka samu Lada, Allah yabada Ikon turawa

AMEEN 🙏🙏

Address

Kano
BNP

Telephone

+2349036477710

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Baye Niasse Production posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to Baye Niasse Production:

Share