16/05/2026
ALLAH YANA GANI..
Ayatullahi Bahjati (RA) yana daga cikin Manyan Malaman Hauza Musamman a ɓangaran "Aklaƙ" wanda yake da Numfashi mai tsarki so sai, zantukansa yake ratsa zuciya, mutane suke tasowa daga Tehran zuwa Qom domin su samu Sallar jam'i a bayansa da sauran karamomi masu tarin yawa da yake dasu.
Wata rana zaiyi lecture ga Daliban Ilimi akan tarbiyyar Ruhi da kuma faɗakarwa kamar yadda ya saba, Ɗalibai sun taru kunnuwa suna jiran gwala-gwalan kalamanda zasu fito daga bakinsa, kowa yana shaukin ya bude baki yayi magana, bayan yayi bismillahi yayiwa Annabin Rahama da Ahlinsa tsarkaka Salati shine yace:
أَلَمْ يَعْلَم بِأَنَّ اللَّهَ يَرَىٰ
Shin Ɗan Adam bai san cewa tabbas Allah yana kallon sa bane?!
Ayatullahi Bahjati (RA) yace: an gama Karatun yau, kowa ya saka wannan ayar a zuciyarsa abinda zai faɗa da abinda zai rubuta da inda zaije da abinda zai gani da sauransu ya sani Allah yana gani kuma shine mafi iya Hukunci masu Hukunci, wassalamu alaikum.