09/01/2026
*FALLASASSHE A RANAR ALKIYAMA*
*Manzon Allah (S.A.W) ya ce: Shin kun san wanene fallasasshe? S**a ce: Fallasasshe a cikinmu shine wanda bashi da dirhami ko kayan more rayuwa, Sai ya ce: "FALLASASSHE daga al'umata shi ne wanda zai zo ranar alkiyama da Sallah, da Azumi da Zakkah, kuma zai zo alhali ya zagi wannan, ya yi ma wannan kazafi, ya ci dukiyar wancan, ya zubar da jinin wancan, ya doki wannan (duka), sai a ba ma wannan daga kyawawan ayyukanshi, wannan ma a bashi daga kyawawan ayyukanshi, idan kyawawan ayyukanshi s**a kare kafin a gama biyan abinda ke kanshi (zaluntan mutane da yayi), sai a dauko laifukansu a daura masa sannan a korashi wuta".*
*أَتَدْرُونَ ما المُفْلِسُ؟ قالوا: المُفْلِسُ* *فِينا مَن لا دِرْهَمَ له ولا مَتاعَ، فقالَ:* *إنَّ المُفْلِسَ مِن أُمَّتي يَأْتي* *يَومَ القِيامَةِ بصَلاةٍ، وصِيامٍ، وزَكاةٍ،* *ويَأْتي قدْ شَتَمَ هذا، وقَذَفَ* *هذا، وأَكَلَ مالَ هذا، وسَفَكَ* دَمَ هذا، وضَرَبَ هذا، فيُعْطَى *هذا مِن حَسَناتِهِ، وهذا مِن حَسَناتِهِ،* *فإنْ فَنِيَتْ حَسَناتُهُ قَبْلَ* أنْ يُقْضَى ما عليه أُخِذَ مِن *خَطاياهُمْ* *فَطُرِحَتْ عليه، ثُمَّ طُرِحَ* *في النَّارِ.*
*الراوي : أبو هريرة | المحدث : مسلم | المصدر : صحيح مسلم*
*~ Muslim*
*Kashedinka da zalumtar mutane, cin mutuncinsu, yi musu karya, daukan dukiyoyinsu, zubar da jinanansu da muzguna musu. Lallai za ka biya a ranar da dukiya da ‘ya’ya ba za su yi aiki ba. Kana ji kana gani za a rabar da ladan ayyukan ka in ma kana da su, in babu a lafta maka zunuban wadanda ka zalunta a yi wurgi da kai cikin jahannama! Allah ya mana tsari.*
Sambest Islamic Da'awa