Kano Muslims youth association-KAMYA

Kano Muslims youth association-KAMYA Inganta ilimin marayu da masu bukata ta musamman da taimakon marasa galihu.

SAKON BARKA DA SALLAH A madadin chairman Imam Muntaka Abdulmalik Muna Mika Sakon gaisuwar Sallah ga masu girma Iyayen ku...
27/05/2026

SAKON BARKA DA SALLAH

A madadin chairman Imam Muntaka Abdulmalik Muna Mika Sakon gaisuwar Sallah ga masu girma Iyayen kungiyar KAMYA, da Membobin Kwamitin zartarwa, Daraktoci, Membobi da daukacin Al'ummar Musulmi Baki daya.

Muna rokon Allah Yakarbi Ibadunmu Ya maimaita Mana Amin.

Eid Mubarak.

Signed state p.r.o Abbas umar Muhd

Chairman Imam Muntaka Abdulmalik ya naɗa Member Muhammad Umar Khalipha a matsayin Babban Mashawarci na Musamman ga ƙungi...
24/05/2026

Chairman Imam Muntaka Abdulmalik ya naɗa Member Muhammad Umar Khalipha a matsayin Babban Mashawarci na Musamman ga ƙungiyar KAMYA.

Naɗin ya zo ne cikin wata takardar k**a aiki mai ɗauke da sa hannun shugaban kwamitin Shurah, Jilani Isah Kofar Nassarawa, wacce Chairman ya miƙa wa Muhammad Khalipha yayin wata ziyara ta musamman a ofishinsa.

A yayin ziyarar, an tattauna hanyoyin samar wa ƙungiyar KAMYA guraben aiki a ƙarƙashin kamfanin Moniepoint, inda Muhammad Khalipha ke cikin manyan jami’an kamfanin.

A jawabinsa, Malam Muhammad Khalipha, Shugaban M.K International Ltd kuma Babban Mashawarci na Musamman ga KAMYA, ya gode wa Chairman bisa wannan muƙami tare da alƙawarin bayar da gudunmawa gwargwadon iko.

signed state p.r.o Abbas umar Muhd

*AN RANTSAR DA IMAM MUNTAKA ABDULMALIK A MATSAYIN SHUGABAN KUNGIYAR MATASA MUSULMI TA JIHAR KANO (KAMYA) A KARO NA UKU 3...
10/05/2026

*AN RANTSAR DA IMAM MUNTAKA ABDULMALIK A MATSAYIN SHUGABAN KUNGIYAR MATASA MUSULMI TA JIHAR KANO (KAMYA) A KARO NA UKU 3:*

A yau lahadi 10/5/2026 Mai Shari'ah Yusuf Garba Tudunwada, PhD, Esq ya Jagoranci Rantsar da Sabbin Shugabannin kungiyar KAMYA Karo na Uku (3rd administration).

Wadanda S**a karbi rantsuwar sun hada da Chairman, da mataimakinsa da Sakatare janar da P.R.O da sauran Manyan shugabanni da daraktocin kungiyar a Matakin Jiha.

Maigirma Dagacin Ja'en Alhaji Isma'il Sa'ad shine ya Jagoranci wannan Taron Wanda Yasamu halartar sauran Manyan Baki k**ar Maigirma Alhaji Sabo Ringim da Maigirma Wakilin Shamakin Kano Alhaji Aminu Buwara da S.A Hon. Isma'il Alkassim da Majidadin Ja'en Engr. Auwal Balarabe da Sheikh Anas Aminu da Sheikh Mudassir Abdullahi da sauran Manyan Baki.

A jawabinsa Jim kadan bayan karbar rantsuwar k**a Aiki, Sabon shugaban KAMYA a Karo na Uku, Imam Muntaka Abdulmalik Ya zayyana wasu daga cikin muhimman ayyukan da kungiyar KAMYA take gabatarwa a kananan hukumomi 44 na Jihar Kano,

Signed state p.r.o Abbas umar Muhd

TARO YANA CI GABA DA TAFIYA MUNA GODEYA DA HALATTAR WANNAN  TARU ALLAH UBANGIJI YA SAKA DA ALKAIRI AMIN SIGNED STATE P.R...
10/05/2026

TARO YANA CI GABA DA TAFIYA MUNA GODEYA DA HALATTAR WANNAN TARU ALLAH UBANGIJI YA SAKA DA ALKAIRI AMIN

SIGNED STATE P.R.O ABBAS UMAR MUHD

GAYYATA !GAYYATA !!GAYYATA !!!KUNGIYAR MATASA MUSULMI TA JIHAR KANO KAMYA TANA FARIN CIKIN GAYYATAR AL'UMMA ZUWA TARON R...
09/05/2026

GAYYATA !

GAYYATA !!

GAYYATA !!!

KUNGIYAR MATASA MUSULMI TA JIHAR KANO KAMYA TANA FARIN CIKIN GAYYATAR AL'UMMA ZUWA TARON RANTSAR DA SABBIN SHUGABANNIN TA KARO NA UKU WANDA ZA'AYI KAMAR HAKA:

RANA: LAHADI 10/05/2026
LOKACI: 9:00 NA SAFE
WURI: HARABAR JA'EN PRIMARY SCHOOL.

ALLAH YABADA IKON ZUWA AMEEN.

Signed state p.r.o Abbas umar Muhd

*THE INAUGURATION CEREMONY OF THE 3RD KAMYA ADMINISTRATION* *ON: SUNDAY 10/5/2026**BY: 9:00 A.M**AT: JA'EN PRIMARY SCHOO...
09/05/2026

*THE INAUGURATION CEREMONY OF THE 3RD KAMYA ADMINISTRATION*

*ON: SUNDAY 10/5/2026*

*BY: 9:00 A.M*

*AT: JA'EN PRIMARY SCHOOL, SHARADA PHASE 3.*

SIGNED STATE P.R.O ABBAS UMAR MUHD

*GIDAUNIYAR JINKAI TA MUTALLAB HUMANITARIAN & CHARITABLE FOUNDATION TA KARRAMA KAMYA DA SHEDAR GIRMAMAWA.*Chairman Imam ...
08/04/2026

*GIDAUNIYAR JINKAI TA MUTALLAB HUMANITARIAN & CHARITABLE FOUNDATION TA KARRAMA KAMYA DA SHEDAR GIRMAMAWA.*

Chairman Imam Muntaka Abdulmalik Wanda ya Samu wakilcin P.A Ibrahim Abdulhamid Gwani shine ya karbi Shedar Karramawar a madadin kungiyar KAMYA.

Ibrahim Gwani yagodewa Gidauniyar bisa wannan Karrama sannan ya bayyana cewa ayyukan kungiyoyin Biyu suna da alaka da juna.

Anasa jawabin Shugaban Mutallab foundation Comrade Yusuf Ahmad badawi Yace Kamya ta cancani wannan Karramawar duba da Dumbin ayyukan alheri datake gabatarwa a wurare daban daban .

A Watan Azumin Daya gabata ma dai kungiyar Mutallab ta Karrama Chairman Imam Muntaka Abdulmalik a Yayin Taron Lacca Wanda kungiyar take shiryawa.

Signed state p.r.o Abbas umar

*KAMYA ZATA SAKE TURA DALIBAI TALATIN (30) ZUWA MAKARANTAR COMPUTER DOMIN YIN KARATU KYAUTA.*Mataimaki na Musamman ga ch...
28/03/2026

*KAMYA ZATA SAKE TURA DALIBAI TALATIN (30) ZUWA MAKARANTAR COMPUTER DOMIN YIN KARATU KYAUTA.*

Mataimaki na Musamman ga chairman, Muhammad Osama Zakariyya ne ya Bayyana Hakan a Wata Sanarwa ta Musamman inda Yace chairman ya amince da tura Dalibai 30 zuwa makarantar mediwat computer science school Domin yin "program na Certificate da Diploma" kyauta.

Saboda haka duk member Dayake sha'awar shiga Cikin wannan shiri ko yake da Wani Wanda zaiyi (maza da mata) sai a tuntubi P.R.O Abbas umar Muhd (07034989177) ko Sakatare Ibrahim Ambasada (08032872112).

A Shekarar data gabata ma dai kungiyar KAMYA ta tura Dalibai 10 zuwa wannan makaranta inda sukayi Karatu kyauta.

Signed state p.r.o Abbas umar Muhd

With Muryar Al'ummar Rimin-Kebe Ungogo Lg. Kano-MARKUK – I just got recognised as one of their top fans! 🎉
17/03/2026

With Muryar Al'ummar Rimin-Kebe Ungogo Lg. Kano-MARKUK – I just got recognised as one of their top fans! 🎉

KAMYA Ungoggo______________Chairman Imam Muntaka Abdulmalik Ya Jagoranci rabon tallafin Kayan abinci ga Marayu da iyayen...
16/03/2026

KAMYA Ungoggo
______________
Chairman Imam Muntaka Abdulmalik Ya Jagoranci rabon tallafin Kayan abinci ga Marayu da iyayen Marayu a ofishin KAMYA reshen Karamar hukumar Kabo aranar Litinin.

Shugaban KAMYA na Karamar hukumar Ungoggo Malam Adamu koranchi Alkadiri shine ya wakilci chairman Imam Muntaka Abdulmalik a wajen wannan gagarumin taro a kauyen koranchi

Alkadiri ya bayyana cewa wannan Tallafin Kari ne akan abincin Buda Baki da suke rabawa Mabukata a ranakun juma'a da Asabar da lahadi a cikin wannan Wata Mai albarka .

Sannan Yace ofishin KAMYA na ungoggo ya dinkawa Marayu 12 Kayan Sallah Wanda za'a raba musu da zarar an kammala dinkawa.

Signed state p.r.o Abbas umar Muhd

Address

Kano

Telephone

+2347038993110

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kano Muslims youth association-KAMYA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share