Kano Muslims youth association-KAMYA

Kano Muslims youth association-KAMYA Inganta ilimin marayu da masu bukata ta musamman da taimakon marasa galihu.

15/08/2026

SAKON TA'AZIYA

Chairman Imam Muntaka Abdulmalik Yana Mika Sakon Ta'aziya ga Membobin mu Hajiya Hussaina Abdullahi Ahmad da Ahmad Abdullahi bisa Rasuwar Mahaifinsu.

Chairman Ya Bayyana kaduwa matuka da Jin labarin Rasuwar wannan Baba Namu Sannan Yayi Addu'ar Allah Yajikansa Yayi Masa Rahama da gafara.

Tuni Chairman Imam Muntaka Ya halarci Sallar Jana'izar Marigayin a yammacin jiya juma'a k**ar Yanda shari'ar Musulinci ta tanadar.

Haka Kuma Mataimakiyar shugabar Mata Hajiya Maimuna Abubakar ta wakilci shugaba Haj. Amira wajen jagirantar tawagar Mata zuwa ta'aziya a safiyar yau.

Signed state p.r.o Abbas umar Muhd

*KAMYA DISTRIBUTES FOOD AID TO ORPHANS*KAMYA has distributed food aid to orphans in Kano as part of its ongoing humanita...
07/08/2026

*KAMYA DISTRIBUTES FOOD AID TO ORPHANS*

KAMYA has distributed food aid to orphans in Kano as part of its ongoing humanitarian efforts.

The exercise, held on Thursday, was led by Chairman Imam Muntaka Abdulmalik who was represented by Treasurer Alh. Hamisu Abubakar. The donation, supported by well-meaning individuals, aimed to ease the impact of economic hardship on orphans and their families. Support was also extended to parents and guardians around the KAMYA office.

The Treasurer further reiterated that the welfare of orphans and the sponsorship of their education remain top priorities of the Association under the leadership of Chairman Imam Muntaka Abdulmalik.

KAMYA remains committed to supporting vulnerable children across Kano State.

Signed
State P.R.O
Abbas Umar Muhammad

KAMYA ta sake gabatar Rabon Tallafin Abinci ga Marayu a jiya Alhamis:Chairman Imam Muntaka Abdulmalik ne ya jagoranci ra...
07/08/2026

KAMYA ta sake gabatar Rabon Tallafin Abinci ga Marayu a jiya Alhamis:

Chairman Imam Muntaka Abdulmalik ne ya jagoranci rabon tallafin ga wasu daga cikin marayun kungiya k**ar dai yadda aka saba gudanarwa lokaci zuwa lokaci.

Chairman Wanda Yasamu wakilcin Treasurer Hamisu Abubakar ya miƙa tallafin tare da bayyana cewa gudummawar ta fito ne daga wasu bayin Allah tare da hadin gwiwar KAMYA domin rage radadin halin rayuwa da ake fama dashi.

Hamisu Abubakar Yace Har ila yau an Mika tallafin zuwa ga iyayen Marayu Dake makwabtaka da ofishin KAMYA

Taimakon Marayu tare da Daukar nauyin karatunsu Yana daga cikin manyan manufofin KAMYA Wanda chairman Imam Muntaka yake baiwa matukar kulawa.

SIGNED STATE P. R. O
ABBAS UMAR MUHD

SAKON BARKA DA SALLAH A madadin chairman Imam Muntaka Abdulmalik Muna Mika Sakon gaisuwar Sallah ga masu girma Iyayen ku...
27/05/2026

SAKON BARKA DA SALLAH

A madadin chairman Imam Muntaka Abdulmalik Muna Mika Sakon gaisuwar Sallah ga masu girma Iyayen kungiyar KAMYA, da Membobin Kwamitin zartarwa, Daraktoci, Membobi da daukacin Al'ummar Musulmi Baki daya.

Muna rokon Allah Yakarbi Ibadunmu Ya maimaita Mana Amin.

Eid Mubarak.

Signed state p.r.o Abbas umar Muhd

Chairman Imam Muntaka Abdulmalik ya naɗa Member Muhammad Umar Khalipha a matsayin Babban Mashawarci na Musamman ga ƙungi...
24/05/2026

Chairman Imam Muntaka Abdulmalik ya naɗa Member Muhammad Umar Khalipha a matsayin Babban Mashawarci na Musamman ga ƙungiyar KAMYA.

Naɗin ya zo ne cikin wata takardar k**a aiki mai ɗauke da sa hannun shugaban kwamitin Shurah, Jilani Isah Kofar Nassarawa, wacce Chairman ya miƙa wa Muhammad Khalipha yayin wata ziyara ta musamman a ofishinsa.

A yayin ziyarar, an tattauna hanyoyin samar wa ƙungiyar KAMYA guraben aiki a ƙarƙashin kamfanin Moniepoint, inda Muhammad Khalipha ke cikin manyan jami’an kamfanin.

A jawabinsa, Malam Muhammad Khalipha, Shugaban M.K International Ltd kuma Babban Mashawarci na Musamman ga KAMYA, ya gode wa Chairman bisa wannan muƙami tare da alƙawarin bayar da gudunmawa gwargwadon iko.

signed state p.r.o Abbas umar Muhd

*AN RANTSAR DA IMAM MUNTAKA ABDULMALIK A MATSAYIN SHUGABAN KUNGIYAR MATASA MUSULMI TA JIHAR KANO (KAMYA) A KARO NA UKU 3...
10/05/2026

*AN RANTSAR DA IMAM MUNTAKA ABDULMALIK A MATSAYIN SHUGABAN KUNGIYAR MATASA MUSULMI TA JIHAR KANO (KAMYA) A KARO NA UKU 3:*

A yau lahadi 10/5/2026 Mai Shari'ah Yusuf Garba Tudunwada, PhD, Esq ya Jagoranci Rantsar da Sabbin Shugabannin kungiyar KAMYA Karo na Uku (3rd administration).

Wadanda S**a karbi rantsuwar sun hada da Chairman, da mataimakinsa da Sakatare janar da P.R.O da sauran Manyan shugabanni da daraktocin kungiyar a Matakin Jiha.

Maigirma Dagacin Ja'en Alhaji Isma'il Sa'ad shine ya Jagoranci wannan Taron Wanda Yasamu halartar sauran Manyan Baki k**ar Maigirma Alhaji Sabo Ringim da Maigirma Wakilin Shamakin Kano Alhaji Aminu Buwara da S.A Hon. Isma'il Alkassim da Majidadin Ja'en Engr. Auwal Balarabe da Sheikh Anas Aminu da Sheikh Mudassir Abdullahi da sauran Manyan Baki.

A jawabinsa Jim kadan bayan karbar rantsuwar k**a Aiki, Sabon shugaban KAMYA a Karo na Uku, Imam Muntaka Abdulmalik Ya zayyana wasu daga cikin muhimman ayyukan da kungiyar KAMYA take gabatarwa a kananan hukumomi 44 na Jihar Kano,

Signed state p.r.o Abbas umar Muhd

TARO YANA CI GABA DA TAFIYA MUNA GODEYA DA HALATTAR WANNAN  TARU ALLAH UBANGIJI YA SAKA DA ALKAIRI AMIN SIGNED STATE P.R...
10/05/2026

TARO YANA CI GABA DA TAFIYA MUNA GODEYA DA HALATTAR WANNAN TARU ALLAH UBANGIJI YA SAKA DA ALKAIRI AMIN

SIGNED STATE P.R.O ABBAS UMAR MUHD

GAYYATA !GAYYATA !!GAYYATA !!!KUNGIYAR MATASA MUSULMI TA JIHAR KANO KAMYA TANA FARIN CIKIN GAYYATAR AL'UMMA ZUWA TARON R...
09/05/2026

GAYYATA !

GAYYATA !!

GAYYATA !!!

KUNGIYAR MATASA MUSULMI TA JIHAR KANO KAMYA TANA FARIN CIKIN GAYYATAR AL'UMMA ZUWA TARON RANTSAR DA SABBIN SHUGABANNIN TA KARO NA UKU WANDA ZA'AYI KAMAR HAKA:

RANA: LAHADI 10/05/2026
LOKACI: 9:00 NA SAFE
WURI: HARABAR JA'EN PRIMARY SCHOOL.

ALLAH YABADA IKON ZUWA AMEEN.

Signed state p.r.o Abbas umar Muhd

*THE INAUGURATION CEREMONY OF THE 3RD KAMYA ADMINISTRATION* *ON: SUNDAY 10/5/2026**BY: 9:00 A.M**AT: JA'EN PRIMARY SCHOO...
09/05/2026

*THE INAUGURATION CEREMONY OF THE 3RD KAMYA ADMINISTRATION*

*ON: SUNDAY 10/5/2026*

*BY: 9:00 A.M*

*AT: JA'EN PRIMARY SCHOOL, SHARADA PHASE 3.*

SIGNED STATE P.R.O ABBAS UMAR MUHD

*GIDAUNIYAR JINKAI TA MUTALLAB HUMANITARIAN & CHARITABLE FOUNDATION TA KARRAMA KAMYA DA SHEDAR GIRMAMAWA.*Chairman Imam ...
08/04/2026

*GIDAUNIYAR JINKAI TA MUTALLAB HUMANITARIAN & CHARITABLE FOUNDATION TA KARRAMA KAMYA DA SHEDAR GIRMAMAWA.*

Chairman Imam Muntaka Abdulmalik Wanda ya Samu wakilcin P.A Ibrahim Abdulhamid Gwani shine ya karbi Shedar Karramawar a madadin kungiyar KAMYA.

Ibrahim Gwani yagodewa Gidauniyar bisa wannan Karrama sannan ya bayyana cewa ayyukan kungiyoyin Biyu suna da alaka da juna.

Anasa jawabin Shugaban Mutallab foundation Comrade Yusuf Ahmad badawi Yace Kamya ta cancani wannan Karramawar duba da Dumbin ayyukan alheri datake gabatarwa a wurare daban daban .

A Watan Azumin Daya gabata ma dai kungiyar Mutallab ta Karrama Chairman Imam Muntaka Abdulmalik a Yayin Taron Lacca Wanda kungiyar take shiryawa.

Signed state p.r.o Abbas umar

Address

Kano

Telephone

+2347038993110

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kano Muslims youth association-KAMYA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share