Qur'ani Da Hadisi

Qur'ani Da Hadisi Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Qur'ani Da Hadisi, Religious Center, Kano.

Watan Ramalana ne wanda aka saukar da Alƙur'ani a cikinsa, shiriya ga mutane da hujjoji bayyanannu na shiriya da rarrabe...
17/02/2026

Watan Ramalana ne wanda aka saukar da Alƙur'ani a cikinsa, shiriya ga mutane da hujjoji bayyanannu na shiriya da rarrabewa. Wanda daga cikin ku ya halarci watan, sai ya azumce shi, kuma wanda ya kasance mara-lafiya ko kuma matafiyi, sai ya biya adadin daga wasu kwanaki na daban. Allah Yana nufin sauƙi gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani gare ku, kuma domin ku cika adadin, kuma domin ku girmama Allah a kan Ya shiryar da ku, ko kwa kasance masu godewa.
(Qur'ani: Suratul Baqara Aya ta 185)

.

An rawaito daga Abu Huraira:Manzon Allah (ﷺ) Ya ce:” Mai-ƙarfi ba shi ne wanda yake rinjayar mutane (doke mutane) da ƙar...
28/01/2026

An rawaito daga Abu Huraira:
Manzon Allah (ﷺ) Ya ce:
” Mai-ƙarfi ba shi ne wanda yake rinjayar mutane (doke mutane) da ƙarfinsa ba, amma mai-ƙarfi shi ne wanda yake iya kame kansa a lokacin fushi (wanda ya ke iya haɗiye fushinsa).”
[Bukhari da Muslim]

Manzon Allah (ﷺ) Ya ce: "Mafi cikakken mumini wajen imani shi ne wanda ya fi kowa kyawun ɗabi’a (halayya)."Sunan Abi Daw...
26/01/2026

Manzon Allah (ﷺ) Ya ce: "Mafi cikakken mumini wajen imani shi ne wanda ya fi kowa kyawun ɗabi’a (halayya)."

Sunan Abi Dawud 4682

Abdullahi bin Mas’ud ya ruwaito cewa Manzon Allah ﷺ Ya ce:“Mafi yawancin zunuban ’ya’yan Adam daga harshensu ne.”Al-Mu‘j...
07/01/2026

Abdullahi bin Mas’ud ya ruwaito cewa Manzon Allah ﷺ Ya ce:
“Mafi yawancin zunuban ’ya’yan Adam daga harshensu ne.”

Al-Mu‘jam al-Kabīr

25/12/2025

Anas ya ruwaito: Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce,

“Ku yawaita yin salati a gare ni a ranar Juma'a da daren Juma’a, Duk wanda ya yi mini salati sau ɗaya, Allah zai yi masa salati sau goma.”

[Sunan al-Kubra lil-Bayhaqi]

21/12/2025
Muna cikin daren juma'a, mu yawaita salati ga Manzon Allah (ﷺ).
27/11/2025

Muna cikin daren juma'a, mu yawaita salati ga Manzon Allah (ﷺ).

Kuma idan Allah Ya shafe ka da wata cuta, to babu mai yaye ta face shi, kuma idan Ya nufe ka da alheri, to, babu mai juy...
29/10/2025

Kuma idan Allah Ya shafe ka da wata cuta, to babu mai yaye ta face shi, kuma idan Ya nufe ka da alheri, to, babu mai juyar da falalarSa. Yana samun wanda Ya so daga cikin bayinSa da shi. Kuma Shi Mai gafara ne Mai jin ƙai.
[Qur'ani: Suratul Yunus, Aya ta 107]

Nana A’isha (R.A) ta ruwaito cewa idan wani daga cikin iyalan gidan Manzon Allah ya kamu da rashin lafiya, Manzon Allah ...
05/10/2025

Nana A’isha (R.A) ta ruwaito cewa idan wani daga cikin iyalan gidan Manzon Allah ya kamu da rashin lafiya, Manzon Allah (ﷺ) yana yi masa ruqya ta hanyar karanta Mu'awwizatan (Falaƙi da Nasi), kuma lokacin da Manzon Allah Ya ke jinyar ajali, ni kuma ina tofa masa ruqya (a tafin hannayen sa) kuma in shafe masa jikinsa da hannayen nasa saboda hannayen sa suna da albarkar waraka fiye da hannaye na.
[Sahih Muslim]

An rawaito daga Abu Huraira:Manzon Allah (ﷺ) Ya ce, "Arziki ba shi ne yawan dukiya ba, arziki na gaskiya shi ne wadatar ...
29/09/2025

An rawaito daga Abu Huraira:

Manzon Allah (ﷺ) Ya ce, "Arziki ba shi ne yawan dukiya ba, arziki na gaskiya shi ne wadatar zuci."
[Bukhari]

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Qur'ani Da Hadisi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share