08/06/2026
*_WANDA YA SHIRYA AURE DA WANDA YA KE KARATU WA ZAN ZAƁA???!_*
*TAMBAYA:*
Assalamu alaikum Wa rahmatullah wa barakatuh tambaya tah ita ce shekara ta 22 kuma sai na samu manema aure guda biyu duka suna da kyawawan dabi'u amma daya daga ciki mahaddacin alqur'ani ne matsalar shekarar shi 26 bai shirya aure bah sbd final year ya ke a university dayan kuma babba ne aiki ya ke ya shirya aure sai na yanke shawarar na jira mahaddacin alqur'anin har sai ya shiryah sbd shi mlm ne hakan da nai ya dace ?
*AMSA:*
wa alaikumus salam warahmatullah,
Muallima Rukayya Allah yayi miki albarka da zabi mafi alheri. Wannan tambaya tana da kyau, kuma zaɓar miji yana buƙatar a duba mai addini, ɗabi’a, sana'ar da Zai iya ɗaukar nauyinki.
Kasancewar mutum mahaddacin Alƙur’ani wannan abu ne mai girma kuma falala ce babba, amma bai kamata a ɗauki iya hakan shi kaɗai a matsayin dalilin zaɓar miji ba.
Annabi ﷺ ya umarce mu da mu duba mai addini da ɗabi’a. Haka kuma aure yana buƙatar namiji ya kasance yana da niyyar yin auren, ya shirya, kuma yana da ikon ɗaukar nauyin auren.
A yadda kikai bayani, Shi na farko yana da haddar Alƙur’ani, wannan Abu ne me kyau, sai dai kince bai shirya aure ba tukuna saboda yana karatu. Na biyu, kince yana da aiki kuma ya shirya aure.
To da farko dai Jiran na farko ba laifi ba ne idan, Kina da tabbacin yana da niyyar zai aure ki, ba wai kawai zato ba, wanda ni a fahimta ta, bana yarda da hakan kai tsaye. Saboda cases majority irin wannan a karshe abun baya yin dadi, bance baa samun masu amana ba, amma dai babu tabbas.
Na biyu, idan kin zabe shi, to ya zamto akwai magana mai kyau tsakanin iyayenki da iyayensa.
Na uku, ta zamto akwai wani lokaci da aka fitar, misali bayan ya kammala karatu Zaa yi auren, ko zuwa wani lokacin da zai iya ɗaukar nauyin Auren. Wanda bashi da tabbas akan goben sa, domin karatu ya ke yi, karatu a ƙasa irin tamu ta Nijeriya kuwa babu tabbas din wani aiki mai gwabi, kuma bashi da wata sana'a yanzu a hannu, saboda haka ba za ki rasa wata dama mai kyau ba saboda jiran abin da ba shi da tabbas.
Amma idan kawai kin zabe shi ne saboda “shi malami ne” "ko mahaddacin Qur'ani" alhali kuwa babu tabbacin shirin aurensa, ya kamata ki sake nazari. Mutum mai aiki kuma mai kyawawan ɗabi’u na iya zama miji nagari shima.
Saboda haka a nawa shawaran, Ki yi istikhara ki roƙi Allah ya zaɓa miki Alheri. Sannan Ki nemi shawarar iyayenki ko yan uwanki, Ki duba wanda zai fi taimaka miki wajen samun kwanciyar hankali da kusanci da Allah.
Allah Ya zaɓa miki mafi alheri, Ya sanya albarka a zabinki. 🤲
*📝Shashen Fatawa bisa Qur'ani, Sunnah, da maganganun magabata na kwarai*
_*🎙ZAUREN SAWTUL HIKMAH 🎙 (da'awar sunnah a social Media's) 🌎*_
*• Ga masu buqatar shiga Zauren Sawtul hikmah zasu iya bi ta links din da ke ƙasa👇*
08032312988
https://t.me/sawtulhikma
https://www.facebook.com/sawtulhikmah
https://t.me/sawtul_hikmah
https://twitter.com/sawtulhikmah01
*🎙️SAWTUL HIKMAH TAKU CE DOMIN YAƊA SUNNA💪*