Sawtul-hikmah-da'awar sunnah

Sawtul-hikmah-da'awar sunnah Karantarwa, Wa'azantarwa, Nasiha, Shawara, Fadakarwa, ta hanyar qur'ani da ingattattun hadisan Manzon Allah (S.A.W), da Maganganun magabata na kwarai

Zauren *��SAWTUL - HIKMAH��*

�Assalamu alaikum, Muna muku barka da zuwa Zauren
*DA'AWAR SUNNAH A SOCIAL MEDIA*

�(Shashen mu na WhatsApp�) _Akwai Sharuɗa (dokoki) da bayanan wannan zaure �_

*�MANUFAR ZAUREN�*

�Manufar bude wannan zauren shine yunkurin yada Addinin musulunci, bisa Qur'ani ta hanyar sunnar Manzon Allah (S.A.W), da fahimtar magabata na kwarai. Da kokarin yaƙar *Bidi'a* d

a aqidar *Shi'a* a ko ina a duniyar hausawa ta media.

*�Kuma mu Dalibai ne ba Malamai ba.*

*�BURIN MU�*

�Burin mu (manufa) shine yaɗa addinin Allah ta hanya mai kyau tare da:-
_�Nasiha_
_�Ilimantarwa_
_�Wa'azantarwa_
_�Shawara_
_�Fadakarwa_
_�Tarbiyya_

*�SHARUƊA/DOKOKI�*

1. *Admin kawai ke da damar post a wannan group, duk wanda yayi zamu cireshi.*

2. _Sannan ba mu bukatar:_
- *~Allah ya saka da alkhairi~*
- *~Huduba/karatu ya yi kyau~*
- *~Mashaa Allah~*
- *~Alhamdulillah~*
- *~Assalamu alaikum~*
- *~ko makamancin hakan~*

==> _Dalilin yin hakan shine domin kiyaye maganganun da basu dace ba a wannan (GROUP) ko nuna akidodin da basuyi dai-dai da koyarwar Qur'ani da Hadisi ba._

3. *Ba'a yin postings ko wane irine, Admin kadai keda dama.*

4. *Ba a sharhi ko ta'aliki. Mai tambaya ko karin bayani akan abinda aka kawo, ko gyaran wani kuskure ya tuntubi admin ta private chat.*

5. *Ba a yarda wani ya canza DP na group ba sai admin.*

*�BAYANAN ZAURE�*

*�Zaku iya samun sawtul hikmah a ɗaukacin social media da ke ƙasa: �*

�Telegram Channel: https://t.me/sawtulhikma

�Telegram Group: https://t.me/sawtul_hikmah

�WhatsApp Groups: https://wa.me/message/4GUWVLVQD6VNA1

�Telegram Number: https://t.me/2348060027244

�Shashen mu wasa kwakwalwa dake WhatsApp: https://chat.whatsapp.com/JxC0AU3THFN7bvJC2kJLuC

�Shashenmu na turanci Zalla:
https://chat.whatsapp.com/E2AHRkCV51zIXDfPj0HJlp

�Facebook: https://www.facebook.com/sawtulhikmah

�Websites:- http://www.sawtul-hikmah.simplesite.com

�Twitter: https://twitter.com/sawtulhikmah01

�Instagram:- https://www.instagram.com/invites/contact/?i=p6c0qk2nw7g7&utm_content=2gszye9

�Youtube: https://www.youtube.com/channel/UCR8FTsgUfLQZ3YUbACJ1YOg

�Our blogs: www.Sawtulhikmah.wordpress.com

�Email/Gmail:- [email protected] [email protected]

*�Muna Da Shashen MAKARANTA ONLINE don neman karin bayani sai a tuntubemu ta wnn link�*

https://t.me/2348032312988

� *Duk mai tambaya sai ya tura ta wannan numbers* ��
*(+233269748641)* ko *(+2348032312988)*
_(Akwai sharuda da s**a shafi turo tambaya.)_

_Amma bama amsa abunda ya shafi fassarar mafarki, rabon gado, macen da tayi planing. Wadannan mun musu iyaka!!_

*�Mai korafi kuma ya neme mu ta wannan number* �
� � *(+234832312988)*
_Koh ta_
*[email protected]* �

*�BUQATAR MU�*

*Buqatarmu a gurinku shi ne Addu'a � da fatan alkhair daga gare ku, ku yaɗa saqonnin da'awar mu a ko ina a duniya, domin ana samun lada mai yawa, kuma yaɗa ilimi yana da daga cikin Abubuwan da suke kusan ta bayi ga Mahaliccinsu. Sannan duk inda aka ga kuskuren mu a tuntube mu, a kiyaye canza mana posts saboda amana ta ilimi.*

_idan an amince sai an fadi cikakken suna da address._

� Zauren *�SAWTUL - HIKMAH�* _Admins only!!_

*_WANDA YA SHIRYA AURE DA WANDA YA KE KARATU WA ZAN ZAƁA???!_*                                              *TAMBAYA:*As...
08/06/2026

*_WANDA YA SHIRYA AURE DA WANDA YA KE KARATU WA ZAN ZAƁA???!_*

*TAMBAYA:*

Assalamu alaikum Wa rahmatullah wa barakatuh tambaya tah ita ce shekara ta 22 kuma sai na samu manema aure guda biyu duka suna da kyawawan dabi'u amma daya daga ciki mahaddacin alqur'ani ne matsalar shekarar shi 26 bai shirya aure bah sbd final year ya ke a university dayan kuma babba ne aiki ya ke ya shirya aure sai na yanke shawarar na jira mahaddacin alqur'anin har sai ya shiryah sbd shi mlm ne hakan da nai ya dace ?

*AMSA:*

wa alaikumus salam warahmatullah,
Muallima Rukayya Allah yayi miki albarka da zabi mafi alheri. Wannan tambaya tana da kyau, kuma zaɓar miji yana buƙatar a duba mai addini, ɗabi’a, sana'ar da Zai iya ɗaukar nauyinki.

Kasancewar mutum mahaddacin Alƙur’ani wannan abu ne mai girma kuma falala ce babba, amma bai kamata a ɗauki iya hakan shi kaɗai a matsayin dalilin zaɓar miji ba.

Annabi ﷺ ya umarce mu da mu duba mai addini da ɗabi’a. Haka kuma aure yana buƙatar namiji ya kasance yana da niyyar yin auren, ya shirya, kuma yana da ikon ɗaukar nauyin auren.

A yadda kikai bayani, Shi na farko yana da haddar Alƙur’ani, wannan Abu ne me kyau, sai dai kince bai shirya aure ba tukuna saboda yana karatu. Na biyu, kince yana da aiki kuma ya shirya aure.

To da farko dai Jiran na farko ba laifi ba ne idan, Kina da tabbacin yana da niyyar zai aure ki, ba wai kawai zato ba, wanda ni a fahimta ta, bana yarda da hakan kai tsaye. Saboda cases majority irin wannan a karshe abun baya yin dadi, bance baa samun masu amana ba, amma dai babu tabbas.

Na biyu, idan kin zabe shi, to ya zamto akwai magana mai kyau tsakanin iyayenki da iyayensa.

Na uku, ta zamto akwai wani lokaci da aka fitar, misali bayan ya kammala karatu Zaa yi auren, ko zuwa wani lokacin da zai iya ɗaukar nauyin Auren. Wanda bashi da tabbas akan goben sa, domin karatu ya ke yi, karatu a ƙasa irin tamu ta Nijeriya kuwa babu tabbas din wani aiki mai gwabi, kuma bashi da wata sana'a yanzu a hannu, saboda haka ba za ki rasa wata dama mai kyau ba saboda jiran abin da ba shi da tabbas.

Amma idan kawai kin zabe shi ne saboda “shi malami ne” "ko mahaddacin Qur'ani" alhali kuwa babu tabbacin shirin aurensa, ya kamata ki sake nazari. Mutum mai aiki kuma mai kyawawan ɗabi’u na iya zama miji nagari shima.

Saboda haka a nawa shawaran, Ki yi istikhara ki roƙi Allah ya zaɓa miki Alheri. Sannan Ki nemi shawarar iyayenki ko yan uwanki, Ki duba wanda zai fi taimaka miki wajen samun kwanciyar hankali da kusanci da Allah.

Allah Ya zaɓa miki mafi alheri, Ya sanya albarka a zabinki. 🤲

*📝Shashen Fatawa bisa Qur'ani, Sunnah, da maganganun magabata na kwarai*

_*🎙ZAUREN SAWTUL HIKMAH 🎙 (da'awar sunnah a social Media's) 🌎*_

*• Ga masu buqatar shiga Zauren Sawtul hikmah zasu iya bi ta links din da ke ƙasa👇*

08032312988

https://t.me/sawtulhikma

https://www.facebook.com/sawtulhikmah

https://t.me/sawtul_hikmah

https://twitter.com/sawtulhikmah01

*🎙️SAWTUL HIKMAH TAKU CE DOMIN YAƊA SUNNA💪*

01/06/2026

A cikin aljanna, ba za mu taɓa rabuwa ba. Ba za mu ƙara jin tsoron wani abu ba, imma mutuwa, ko yanayin rayuwa, ko tafiya ba. Babu kishi, barci, kuma babu gajiya. A cikin Aljanna, babu kuka, babu raunuka, babu hawaye, babu ciwo, babu damuwa, kuma babu wahala.
Babu ​Furfura, duhun da ke ƙarƙashin idanunmu, gajiyar tsayawa a makare, da kuma sha'awa duk za su mutu a can.

​A cikin Aljanna, za mu ga Allah da Manzonsa ﷺ ❤️.

ALLAH Ka Bamu Aljanna, kwatanta wannan Ni'ima ta Aljanna yana sa mu manta da wahalhalu da azaba da damuwa da muke ciki a wannan duniyar.

*✍️Abou Khadeejatu Assalafeey*

*🎙️SAWTUL HIKMAH MEDIA TV 🎙️*
08032312988

https://sirassalafeey.wordpress.com/mu-kula-da-wannan-a-ranar-arafah/Ku kula da wannan Ranar ta Arafah!Ba rana ce ta tsa...
25/05/2026

https://sirassalafeey.wordpress.com/mu-kula-da-wannan-a-ranar-arafah/

Ku kula da wannan Ranar ta Arafah!

Ba rana ce ta tsaftace gidaje ba, ba kuma rana ce ta siyayyan kayan salla kadai ba, ba kuma rana ce ta barci ba, ba kuma rana ce ta shakatawa ba.

Rana ce da Allah ya girmama ta, rana ce da Allah ya ɗaukaka ta, rana ce da Allah yake alfahari da mazauna Aljanna tare da mutanen Arafah.
Rana ce ta 'yantarwa daga Wutar Jahannama, rana ce ta biyayya da ƙoƙari a cikin ibada, kuma mafi kyawun addu'a ita ce addu'ar Ranar Arafah.

Ku yi ƙoƙari ku tabbatar da cewa kowane numfashi da kuka ɗauka yana cike da yin biyayya ko kuma wata ibada da za ta kusanta ku da Allah. Domin idan kun mallaki ɗaya daga cikin mafi kyawun kayan ado na duniya, za ku yi baƙin ciki da rashinta; to ta yaya za ku ɓatar da mafi kyawun rana ta shekara?!

Idan a watan Ramadan ba'a san wane dare ne Daren Alƙawari (Lailatul ƙadari) ba, to Ranar Arafah an san ta. Kuma idan mala'iku suna sauka a Daren Alƙawari (Lailatul ƙadari), to Allah Shi da KanSa zai sauko a Ranar Arafah. Don haka ku yi amfani da damar ku, ku yi iya ƙoƙarinku. Ga wani jadawali na Ranar Arafah mai kyau; ku sharing din shi da masoyanku. Rana ɗaya ce kawai a shekara ba biyu ba.

1. Ku yi barci da wuri a daren kafin Arafah don samun ƙarfi da bauta wa Allah sosai.

2. Ku tashi kafin fitowar alfijir don yin suhoor, da niyyar azumin wannan rana ta Arafah.

3. Sannan ku yi salla aƙalla raka'a biyu ko huɗu, ku roƙi Ubangijinku yayin da kuke sujada, kuna neman mafi kyawun duniya da lahira. Ku yabe Shi da ya ba ku damar isa ga wannan rana da rahama da gafara ke sauka a kanta.

4. Kafin fitowar alfijir, ku ɓatar da Lokacin ku kuna neman gafara domin a rubuta ku wurin Allah a matsayin ɗaya daga cikin waɗanda ke neman gafara a lokacin fitowar alfijir.

5. Ku shirya don yin sallar Asuba a jam'i. Tare da yin alwala cikakke don samun gafarar masu alwala.

6. Sannan ku karanta addu'ar bayan kammala alwala.

7. Ka yi sallar Asuba kuma ka kasance a cikin wurin sallar har zuwa mintuna 15 bayan fitowar rana.

8. Yin Takbir nan da nan bayan Taslim (sallar ƙarshe), kamar yadda na ambata a farkon wannan saƙon.

9. Yayin da kake cikin wurin sallar ka, har zuwa fitowar rana, ka karanta Alƙur'ani, ka ɗaukaka Allah, ka yabe Shi, kuma ka tuna da azkar din safe.

10. Yi sallar Raka'a biyu na Duha (sallar walaha) don samun ladan Hajji da Umrah tare da Annabi Muhammadu (ﷺ). Kada ka rasa wannan damar.

11. Yanzu kana da zaɓi: idan za ka iya kasancewa a farke duk rana, kada ka ɓatar da ko daƙiƙa ɗaya face dai kana cikin ambaton Allah da addu'a.

12. Ko kuma, ka yi barci na awa ɗaya da niyyar samun ƙarin ƙarfi don yin bauta ga Allah.

13. Sai ka tashi, ka yi alwala, ka yi salla aƙalla Raka'a huɗu na sallar Duha, ka dinga canza ayyukan ibada har sai ka gaji... Kai bai kamata ma ka gaji ba...

Ka yi takbiri (Allahu Akbar), zikri (Ambaton Allah), ka karanta (Alƙur'ani), kuma ka nanata fadin,

لاإله الا الله وحده لاشريك له الملك وله الحمد وهو على كل شئ قدير..

"Babu wani abin bautawa sai Allah, Makaɗaici, ba shi da abokin tarayya. Mulki da yabo nasa ne, kuma Shi ne mai iko a kan komai."

14. Ka yi sallar Azahar, ka yi takbiri, kayi tasbihi, sannan ka karanta wasu ayoyi daga cikin Alƙur'ani.

15. Ka saurari wa'azin Arafat da kyau kuma ka yi ƙoƙari ka sa amfani da koyarwarsa na wannan shekara ya fi na kowace, in Allah ya yarda.

16. Ka yi sallar La'asar a jami, anan ma ka yawaita takbiri sannan ka karanta addu'o'in maraice, Wato zikiri yamma.

17. Karanta Alƙur'ani har zuwa kimanin awa ɗaya kafin Maghrib. Toh a wannan lokacin sai Ka fara addu'arka Cike da tawali'u, ka tuna da tsayawarka a gaban Allah. Kada ka manta da yin addu'a ga 'yan'uwanka Musulmi maza da mata a ko'ina.

18. Ka yi addu'a ga Allah kada rana ta Arafat ta faɗi face sai ka kasance cikin waɗanda aka 'yantar daga Wuta.

19. Allah Ya shiryar da mu duka zuwa ga ayyukan alheri, kuma muna roƙon Allah Ya karɓe mu da kanmu da kuma a gare ku.

Ku tunatar da iyalanku da masoyanku game da wannan. Allah Ya sanya mu da ku a cikin waɗanda Ya 'yantar daga Wuta da kuma waɗanda ayyukansu s**a kasance karbabbu. Amincin Allah da albarkarSa su tabbata ga Annabinmu Muhammadu, iyalansa, da dukkan sahabbansa.

*✍️Abou Khadeejatu Assalafeey*
09/12/1447.
25/05/2026.

Daga Abdullahi ibn Amr ibn al-Aas (Allah Ya yarda da su duka), Manzon Allah ﷺ ya ce:"Mafi kyawun addu'a ita ce addu'ar R...
25/05/2026

Daga Abdullahi ibn Amr ibn al-Aas (Allah Ya yarda da su duka), Manzon Allah ﷺ ya ce:

"Mafi kyawun addu'a ita ce addu'ar Ranar Arafah, kuma mafi kyawun abin da ni da annabawan da s**a gabace ni muka fada shine:

لا إلَهَ إلَّا اللَّهُ وحدَهُ لا شريكَ لَهُ، لَهُ الملكُ ولَهُ الحمدُ وَهوَ على كلِّ شَيءٍ قديرٌ ".

Ma'ana:'Babu wani abin bautawa sai Allah, shi kaɗai, ba shi da abokin tarayya. Mulki da yabo nasa ne, kuma Shi ne mai iko a kan dukkan komai."

📖 [Hadisi na Hasan (mai kyau), Sahih al-Tirmidhi (3585)].

✍️ Abou Khadeejatu Assalafeey

24/05/2026

Falalar Kwanaki 10 Na Farkon Dhul Hijjah | Zancén Hikmah Podcast










*🕯️KWANAKI NA YIN KYAWAWAN AYYUKAN ALKHAIRI🕯️* _Fita ta 2_🕯️Daga ciki akwai:- *AZUMI* An sunnanta yin azumi a ranar tara...
19/05/2026

*🕯️KWANAKI NA YIN KYAWAWAN AYYUKAN ALKHAIRI🕯️*

_Fita ta 2_

🕯️Daga ciki akwai:-

*AZUMI* An sunnanta yin azumi a ranar tara ga watan Zul-Hijjah, domin Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya kwadaitar da mu aikata kyawawan ayyuka a wannan lokacin, kuma Azumi na daga mafifitan ayyuka. Allah ya zabi Azumi domin kansa, kamar yadda ya zo a cikin hadisi qudsi: *"Allah yana cewa: 'Dukkan ayyukan dan Adam suna gareshi, banda azumi, wanda yake na wa ne kuma Ni ne zan saka masa. shi. ""* _(Bukhari ya ruwaito shi, 1805)._

🕯️Annabi (SAW) ya kasance yana azumtar kwanaki tara na farkon watan Zul-Hijjah. An karbo daga Hunayda bn Khalid daga matarsa, cewa daya daga cikin matan Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ta ce: *Annabi (SAW) ya kasance yana yin azumi a farkon tara da ranakun Zul-Hijjah da ranar 'Ashura', da ranaku uku a kowane wata (ayyamul bid), da azumin Litinin da Alhamis."*

_*🕯️Al-Nasa’i ne ya rawaito shi, 4/205 da Abu Dawood; hadisi ne saheeh inji Albani a cikin Saheeh Abi Dawood, 2/462.*_

_*🕯️Allah ka bamu ikon azumtar wannan kwanaki masu falala, ka biya mana buqatunmu*_

*✍️Abou Khadeejatu Assalafeey💞🕊️*
02/12/1442.
13/07/2021.

KWANAKI NA YIN KYAWAWAN AYYUKAN ALKHAIRI Fita ta 2Daga ciki akwai:- AZUMI An sunnanta yin azumi a ranar tara ga watan Zul-Hijjah, domin Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) ya kwad…

19/05/2026

*🕯️KWANAKI GOMAN FARKO NA WATAN ZUL-HIJJAH🕯️*

🕯️Ibnu Abbaas (Allah Ya yarda da shi tare da mahaifinsa) ya ruwaito cewa, Annabi (SAW) ya ce: *"Babu wani aiki mafi daraja a wurin Allah, kuma babu wani sakamako mai girma a wajen Shi, irin yin kyakkyawan aiki a cikin kwanaki goma na watan Hadaya. " An tambaye shi, "Har da ma jihadi saboda Allaah?" Ya ce, "Eh harda ma jihadi don Allah, sai dai a game da mutumin da ya fita yaki kuma ya ba da kansa da dukiyarsa saboda yakin baki ɗaya, sannan kuma ya dawo ba tare da komai ba."*

_*🕯️ (Al-Daarimi ne ya ruwaito shi, 1/357; isnadinsa hasan ne kamar yadda ya zo a cikin al-Irwaa ’, 3/398).*_

*✍️Abou Khadeejatu Assalafeey*
01/12/1442
12/07/2021

https://sirassalafeey.wordpress.com/kwanaki-goman-farko-na-watan-zul-hijjah/

19/05/2026

*_WAJIBI NE KADA A YANKE FARCE DA ASKI GA MAI LAYYA?!_*

*TAMBAYA*

Assalamu alaikum mlm inaimaka ftn alheri tambayata mlm shine yankan farce d aski idan watan zulhijja yakama wajibine kada kayenki idan zakai layya ko b wajibi bane

*AMSA*

Wa Alaikumus Salam. Shaykh ‘Abd al-‘Azeez ibn Baaz (Allah yayi masa rahama) yana cewa:

Duk wanda ke son yin layya, to watan Dhu'l-Hijjah yana farawa kuma saboda kwanaki talatin na watan Dhu'l-Qa'dah sun shude, to wannan mutumin haramun ne a gare shi ya cire wani abu daga gashinsa ko faratansa har sai ya yanka abin hadayarsa, saboda hadisin Umm Salamah (Allah Ya yarda da ita), wanda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Lokacin da kuka ga sabon wata na Dhu'l-Hijjah - a wani sigar daban yace, Lokacin da kwanaki goma (na Dhu'l-Hijjah) s**a fara - kuma ɗayanku yana son yin hadaya, to, ya daina (yankewa) gashi da gumbarsa. " Ahmad da Muslim ne s**a ruwaito shi.

A wata ruwayar kuma, “Kada ya cire wani abu daga gashinsa da faratansa har sai ya miƙa abin hadaya.”

Idan mutum ya yi niyyar yin layyarsa to tun a lokacin farkon kwanaki goma na Dhu'l-Hijjah, ya kamata ya dena wannan tun daga lokacin da ya yi niyyar, kuma babu laifi a kansa ga wani abin da ya yi kafin ya ƙirƙira ita niyyar (kamar da bai da niyyan ko ikon layyan sai daga baya kuma ya riga da ya yanke faratansa ko gashi, to bb laifi), watau dai babu laifi idan mutum yayi aski ya yanke farce kafin ya nufi niyyar cewa zai yi layya, wala'alla saboda bai sami kudin ba sai daga baya.

Dalilin wannan haramcin shi ne don wanda ke son yin hadayar ya shiga cikin mahajjata a wasu ayyukan ibadar Hajji - wato kusantar Allah ta hanyar yanka hadayar - to shima ya kasance tare da su a wasu siffofin ihraamin, wato ya guji aske gashi da sauransu.

Wannan hukuncin zai shafi wanda zai yanka hadayar ne kawai. Bai hau kan da wanda aka yi layya a madadin sa ba, saboda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama cewa yayi: *"Idan dayanku yana son yin hadaya."* Bai ce, “… za a yi hadayar da aka yanka a madadinsa ba.” Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana yin sadaukarwa a madadin mutanen gidansa, kuma ba a ruwaito cewa ya gaya masu su guji hakan ba (yin aski da farce da sauransu).

Dangane da wannan, ya halatta ga dangin mutumin da zai yi hadaya su cire abubuwa daga gashinsu, faratansu da fata a cikin kwanakin farkon goma na Dhu'l-Hijjah.

Idan wanda ke son yin hadayar ya cire wani abu daga gashinsa ko farce to lallai ne ya tuba zuwa ga Allah kuma kar ya sake hakan, amma ba lallai ne sai ya yi kaffara ba, kuma yin hakan ba zai hana shi yin hadayarsa ba kamar yadda wasu daga cikin mutane gama gari suke tunani ba. Idan ya aikata ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan saboda mantuwa ko jahilci, ko kuma wani gashi ya faɗi da gangan, to babu laifi a kansa. Idan yana buƙatar cire shi to yana iya yin hakan, kuma babu laifi a kansa, kamar idan ƙusa ya fasa masa kai kuma zaa cire ta, don haka ya iya aske shi, ko kuma idan gashi ya rufe masa idanunsa sai ya cire shi, ko yana buƙatar yanke gashin kansa don kula da rauni da makamantansu. ”

Allah Ne Mafi Sani.

*✍️Shashen Fatawowin Musulunci Bisa Qur'ani Da Ingantacciyar Sunna*

06/10/1441.
29/05/2020.

https://t.me/sawtulhikma

https://www.facebook.com/sawtulhikmah

_*🎙ZAUREN SAWTUL HIKMAH 🎙* (da'awar sunnah a social Media's) 🌎_
_*🎙ZAUREN SAWTUL HIKMAH 🎙 (da'awar sunnah a social Media's) 🌎*_

*• Ga masu buqatar shiga Zauren Sawtul hikmah zasu iya bi ta links din da ke ƙasa👇*

08032312988

https://t.me/sawtulhikma

https://www.facebook.com/sawtulhikmah

https://t.me/sawtul_hikmah

https://twitter.com/sawtulhikmah01

*🎙️SAWTUL HIKMAH TAKU CE DOMIN YAƊA SUNNA💪*

Address

Markazul Imamul Bukhari, Gwarzo Road
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sawtul-hikmah-da'awar sunnah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to Sawtul-hikmah-da'awar sunnah:

Share