01/06/2024
LABARINA📝
Episode one
Tunda sassafe bayan na gabatar da sallar asuba, ina cikin lazimi sai kawai naji zuciyata ta buga, nan take jikina yayi sanyi na fara ji a jikina kamar wani abu zai same Ni nan kusa. Sosai zuciyata take cikin fargaba. Na ɗaga hannuwana ina roqon Allah ina cewa" Allah ka sa wannan abin ya zamar min alkhairi ko ma minene" na shafa addu'a na tashi.
Na fito kofar ɗakinmu na saka silifas, ga cazbaha ta a hannuna, na shiga kitchen na kunna gas, na ɗora ruwan zafin wankana, na fito ba inda nayi burki sai dakin mamanmu. Na shiga na iske ta tana lazimi. Ta daga hannu tana addu'a nima na daga, Tana shafawa nima na shafa. Na gaishe ta, ta amsa da sakin fuska. Na ce mata" mama a kawo a sawo buredi da sauran kayan shayin don kar mu makara" kallona tayi tace min" ai dai idan kun makara ba laifina ba ne, wai kamar ku manya da ku, ana ganin mutuncinku, ku da ya kamata ace ana koyi daku amma wai kullum ku ne qarshen zuwa a makaranta, daga ku an rufe get, wallahi ku gyara wannan ba rayuwa ba ce" har zan fara magana ta katse Ni da cewa" amshi maza kaje ka sawo kayan karin kumallon" na karɓi 500 na fita fuu kamar zan tashi sama, wai Ni Sarkin zuciya, ina jin zuciyata na zafi saboda fadan da tai ma Ni, a haka na zura takalmana na fita naje shagon da zanyi siyayyar.
Bayan na gama siyayyar ne na fito, ina ta sauri domin bana so na makara, ga shi na ɗora ruwan zafi ina tsoron su ƙone. Tsaye nake ina kallon ababen hawa tunda sassafe yadda mutane s**a sadaukar s**a fito don neman abincinsu. Ina ta wannan tunanin na taho zan tsallako t**i, Ina rabawa tsakiya sai ga wani mai mota a guje, wai kafin in yi wani ƙwaƙƙwaran motsi har ya banke Ni, nayi sama ƙoli sannan na faɗo ƙasa tim! Nidai na ji ƙafata ta dama tayi nauyi, kuma sama sama naji ana cewa kuyi maza ku kai shi asibiti ya mutu. Daga nan kuma ban sake sanin ina kaina yake ba..........❗😰
Ku cigaba da bibiyata
Zan cigaba insha Allah.
Donated
By
@
Www.kalamuwaheeddataplug.com
Nerthir__Ahmerd