01/05/2017
WAJIBI NE MUSULMI YA TSAYA
INDA SHARI'A TA CE YA TSAYA:
Daga AshSheik Dr. Ibrahim Jalo Jalingo Hafizahullah
Ba daidai ba ne musulmi ya
wuce-gona-da-iri game zatin
Annabi mai tsira da amincin
Allah; saboda nuna kauna da
girmamawa a gare shi; Imamul
Bukhaarii ya ruwaito hadithi na
3,445, da Imamu Muslim hadithi
na 1,691 cewa Annabi mai tsira
da amincin Allah ya ce:-
(( ﻻ ﺗﻄﺮﻭﻧﻲ ﻛﻤﺎ ﺃﻃﺮﺕ ﺍﻟﻨﺼﺎﺭﻯ ﺍﺑﻦ
ﻣﺮﻳﻢ ﺍﻧﻤﺎ ﺍﻧﺎ ﻋﺒﺪ ﻓﻘﻮﻟﻮﺍ: ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻠﻪ
ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ)).
Ma'ana: ((kada ku wuce gona da
iri cikin yabona, kamar yadda
Kirista s**a wuce gona da iri
cikin yabon Dan Maryam, ni ba
kowa ba ne face bawa, ku ce:
bawan Allah kuma manzonSa)).
Ga dai abin da Annabi mai tsira
da amincin Allah ya ce wa
al'ummarsa na hana su wuce
iyakar Sahari'ah cikin yabonsa;
watau su yi wata karya game da
shi da nufin yabo da
girmamawa. Sai dai kuma abin
bakin ciki a nan shi ne kadan ne
kwarai daga cikin wannan
Al'ummah tamu suke yin amfani
da wannan gargadi na Annabi
mai tsira da amincin Allah.
Misali: Ya zo cikin littafin
Jawaahirul Ma'anii 1/147 nassi
kamar haka:-
(( ﺍﻭﻝ ﻣﺎ ﺧﻠﻖ ﺍﻟﻠﻪ ﺗﻌﺎﻟﻰ ﺭﻭﺡ ﻣﺤﻤﺪ
ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺛﻢ ﻧﺴﻞ ﺍﻟﻠﻪ ﻣﻨﻬﺎ
ﺃﺭﻭﺍﺡ ﺍﻟﻜﺎﺋﻨﺎﺕ ﺛﻢ ﻛﻮﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻣﻦ ﺟﺴﺪ
ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺃﺟﺴﺎﺩ
ﺍﻟﻤﻼﺋﻜﺔ ﻭﺍﻷﻧﺒﻴﺎﺀ ﻭﺍﻷﻗﻄﺎﺏ )).
Ma'ana: ((Farkon abin da Allah
Ya halitta shi ne ran Muhammad
mai tsira da amincin Allah,
sannan ya halitta sauran
rayukan halittu daga shi
(wannan ran) sannan kuma Allah
Ya halicci jikkunan Mala'iku da
Annabawa da Manyan waliyyai
daga jikin Annabi Mai tsira da
amincin Allah))!
Tabbas babu gaskiya cikin
wannan magana da ta zo cikin
wannan littafi na Jawaahirul
Ma'aniy; domin ijama'in
Musulmin kwarai ya kullu a kan
cewa Annabi mai tsira da
amincin Allah yana daga cikin
zurriyyar Annabi Adam ne ba
wai shi Annabi Adam din ba ne
yake daga cikin zurriyyarsa;
saboda Allah Madaukakin Sarki
Ya ce cikin Suratul Hijri aya ta
28-29 :-
(( ﻭﺇﺫ ﻗﺎﻝ ﺭﺑﻚ ﻟﻠﻤﻼﺋﻜﺔ ﺍﻧﻲ ﺧﺎﻟﻖ
ﺑﺸﺮﺍ ﻣﻦ ﺻﻠﺼﺎﻝ ﻣﻦ ﺣﻤﺎ ﻣﺴﻨﻮﻥ .
ﻓﺈﺫﺍ ﺳﻮﻳﺘﻪ ﻭﻧﻔﺨﺖ ﻓﻴﻪ ﻣﻦ ﺭﻭﺣﻲ
ﻓﻘﻌﻮﺍ ﻟﻪ ﺳﺎﺟﺪﻳﻦ )).
Ma'ana: ((A lokacin da
Ubangijinka Ya ce wa Mala'iku
lalle ne ni Mai halittan wani dan
adam ne daga wani irin laka
busashshe, daga wani irin bakin
tabo jirkitacce, to idan na
daidaita shi, kuma na busa raiNa
cikin shi, to sai ku fadi kuna
masu yi masa sujjada)).
Sannan kuma Ya ce cikin
suratus Sajdah aya ta 7-8 :-
(( ﺍﻟﺬﻱ ﺃﺣﺴﻦ ﻛﻞ ﺷﻲﺀ ﺧﻠﻘﻪ ﻭﺑﺪﺍ
ﺧﻠﻖ ﺍﻻﻧﺴﺎﻥ ﻣﻦ ﻃﻴﻦ. ﺛﻢ ﺟﻌﻞ ﻧﺴﻠﻪ
ﻣﻦ ﺳﻼﻟﺔ ﻣﻦ ﻣﺎﺀ ﻣﻬﻴﻦ)).
Ma'ana: ((Shi ne wannan da Ya
kyautata dukkan kome da Ya
halitta shi, sannan Ya fara
halittar jinsin mutum ne da laka,
daga nan Ya yi zurriyyarsa daga
wani irin daskararren jini da
kuma wani irin ruwa
kaskantacce)).
Allah Ya taimake mu Ya tsare
mana imaninmu. Ameen.