22/05/2026
AKHLAQ 22/5/2026
Yadda aka gabatar da zaman Akhlaq a wannan satin ma an gabatar da zaman Alkhla ga daliban makarantar Ma’ahad Rasul Al-Akram(S) Kudan, wanda ake gabatarwa a kowace ranar Juma’a, Ta ƙarshen sati.
Malam Zaharadeen Ahmad: shi ne ya gabatar da Akhalaq a wannan satin inda ya yi magana akan mahimmancin, Biyayya ga iyaye. Yadda ya kamata mutum ya kasance mai biyayya ga iyayensa.
Ya yi bahasi sosai da jawabin akan mahimmancin Biyayya ga iyaye tare da ankarar da ɗalibai akan mahimmancin kulawa da biyayya ga iyayensu. Inda ya kawo wasu Misalai tare da wasu Hadisai da suke magana akan mahimmancin Biyayya ga iyaye.
A ƙarshe ya yi nasiha da jan hankali sosai ga ɗalibai akan su kula sosai wanjan kulawa da mahimmanci kulawa da iyayensu, Tare da dukkan wani abu da zai iya ɓata musu rai.
– Ma'ahadur Rasul Al-Akram - Nigeria
22/5/2026