17/12/2023
13th December, 2023.
TAKARDAN GODIYA GA ME GIRMA IYAN ZAZZAU.
Assalamu Alaikum Warahmatullah
Da farko muna yiwa Allah godiya bisa rayuwa da Imani da yayi mana baiwarsa, tsira da aminci Kuma su Kara tabbata ga Annabi Muhammad S.A.W da alayensa da sahabbansa da sauran muminai.
Bayan haka muna mika godiya ga RT Hon. Abbas Tajuddeen Iyan Zazzau Kuma speaker na majalisan tarayya ta kasa a madadin limanan masallatanmu da sauran Al'ummar mu na zaria bisa raba tallafin shinkafa domin rage radadin halin da ake ciki.
Kungiyar Fityanun Islam Gundumar Kwarbai A da aka daura wa alhakin tattaro sunayen masallatan Kwarbai A bangaren Darika, tayi yi iya kokarinta Kuma wadanda sunansu ya fito a jadawalin sunayen da aka bata duk ta Mika musu hannu da hannu tare da sa hannu na shedar karba.
Masallatai 95 ne aka bamu a jadawali za aga Me Alfarma Sarkin Zazzau Malam Ahmad Nuhu Bamalli na mika jadawalin a hoto da na sanya. Duk da cewa Wadannan Masallatai ba su kenan ba a Kwarbai A, amma hausawa na cewa duk kirkinka baka iya kewaye kasuwa da gaisuwa. Amma mun mika korafinmu ga Wakilan Me girma iyan Zazzau na masallatan da rabon tallafin be riskesu ba, Kuma muna da tabbaci za a dubasu in Sha Allah.
Godiya ta musamman ga Hon Engr. Jamil Deputy Chief of staff, Hon. Ilyasu Balarabe Jagaban Iyan Zazzau bisa jagorantar raba wannan tallafi a gurare daban-daban bisa umarnin megirma Speaker. Muna Addua yadda kuka isar da amana, Allah ya amintar da ku daga duk wata sharri.
Muna Mika godiya ta musamman ga Shugabanmu, Chairman Fityanul Islam Zaria, manbobi na wannan Kungiya ta Fityanu, Yan agaji da sauran jami'an tsaro da S**a temakemu wannan tallafi ya isa hannun masu shi ba tare da wata matsala ba.
Muna Addua, Allah ya kare mana Me girma Speaker, ye Masa jagora. Ya Kare mana Zazzau Kaduna da najeriya daga duk wata fitina, ameen ya rabbal alameen.
Mallam Yahuza Sani
Chairman Fityanu,
. Gundumar Kwarbai A Zaria