03/02/2026
Muna Taya Al'ummar Musulmi Murna Da Zagayowar Ranar Haihuwar Imam Mahadi Bn Hassan (Ajf), Khalifan Manzon Allah (Saww) Na 12 Kuma Na Ƙarshe🌹.
قال رسول الله صلى الله عليه وآله وسلم؛
افضل الأعمال الإنتظار الفرج.
Fassara......
Manzon Allah (Saww) Ya Faɗa Acikin Hadisi Cewa;
''Mafificin Ayukka Shine Jiran (Mafita), Wato Jiran Bayyanar Imam Mahadi (AJF)''.
An Haifi Sahibul Asr Wazzaman Imam Mahadi (Ajf), Ranar 15 Ga Watan Sha'aban Shekara Ta 255 Bayan Hijirah, a Daren Jumu'a, Sunan Mahaifinsa Shine Imam Hassan Al'askari (AS) Khalifan Manzon Allah (Saww) Na (11), Mahaifiyarsa Itace Sayyidah Narjis (AS).
Imam Mahadi (AJF) Shine Cikamakon Imamai 12 Bayan Manzon Allah (Saww), Kuma Shine Mai Ɗaukar Fansar Iyalan Gidan Manzon Allah (Saww), Imam Yayi Fakuwa Ƙarama (Gaibatus Sugra) Daga Baya Yayi Fakuwa Babba (Gaibatul Kubra) Saboda Ya Rasa Mataimaka a Lokacin, Kuma Bazai Dawo Duniya Ba, Sai Ya Samu Mataimaka 313, Kuma Annabi (Saww) Yace Idan Ya Bayyana Zaiyi Yaƙi Da Azzalumai Irinsu Dujjal (L), Kuma Shizaiyi Nasara Akansu Insha Allah, Kuma Wannan Zamanin Da Muke Ciki Zamaninsa Ne Kuma Shi Muke Jira, Domin Yadawo Ya Ƙwato Ƴancin Addinin Musulunci, Kuma Daga Cikin Sharaɗin Bayyanar Sa Sai Duniya Ta Cika Da Zalunci Da Fajirci, Sannan Ya Bayyana Ya Dawo Da Gaskiya Da Adalci a Duniya.
Muna Roƙon Allah (SWT) Yasamu Cikin Masu Jiransa Na Haƙiƙa🤲🏻.
Kuma Yau Yayi Daidai Da Ranar Da Aka Haifi Babban Mataimakin Imam Mahadi (Ajf), Shine Sheikh Ibrahim Yaqub Zakzaky (H), a Yau Yake Cika Shekara 75 a Duniya, Muna Taya Su Malam (H) Murna, Muna Roƙon Allah (SWT) Ya Ƙarawa Su Malam (H) Lafiya, Kuma Ya Cika Masu Burinsu Na Tabbatar Addinin Musulunci a Wannan Nahiyar Tamu, Mu Kuma Allah (SWT) Kasa Muna Cikin Mabiyansa Na Haƙiƙa🤲🏻.
@ Abubakar Nuhu T/Mafara.
@
@
@
@ .
15/Sha'aban/1447H.
03/February/2026M