08/11/2022
TAKAITACCEN TARIHIN ANNABI MUHAMMAD(SAW):
Kashi Na 01
Nasabarsar ta bangaren mahaifinsa: Muhammad(saw) dan Abdullahi, dan Abdul-Mutallib, dan Hashim dan Abdul-Manaf, dan Kusayyi dan Kilabi… nasabarsa(saw) madaukakiya tana tukewa zuwa ga Annabi Adam(as) a tsatson masu sujadah da tsarki.
Nasabarsa ta bangaren Mahaifiyarsa: Ita ce Aminah ‘yar Wahabi, dan Abdul-Manaf dan Zuhrata dan Kilabi… nasabarsa ta fuskar mahaifinsa da mahaifiyar tahadu wajen Kilab zuwaga Annabi Adam da Hauwa(as).
Wadanda s**a reneshi: Abdul-Mulib, Halimah As-Sa’adiyya, da Abu Talib.
Alkunyarsa: Abul-Qasim, Abu Ibrahim.
Lakabinsa: Al-amin, Al-mustafah…
Sunayensa da s**a zo a cikin Kur’ani mai girma: Khatamun-nabiyyin, Al-ummi, Al-muzzammil, Al-muddassir, An-nazir, Al-mubin, Al-karim, An-nur, Anni’ima, Ar-rahma, Al-abdu, Ar-ra’uf, Ar-rahim, As-shahid, Al-mubasshir, An-nazir, Ad’da’i…
Tarihin haihuwarsa: An haifi Monzon Allah(saw) a Ranar Jumu’ah, 17 Rabi’ul Auwal Shekarar Giwa (571 M) (bisa mash’hurin zance daga Ahlul-Bayt(as) (amma a wata ruwayar an haifeshi(saw) ranar Litinin 12 Rabi’u-auwal).
Inda aka haifesa: Makka.
Tambarin zobensa: Muhammadur-Rasulullah!
Tsawon rayuwarsa: shekaru 63.
Tsawon lokacin Annabtarsa: shekaru 23.
Aikoshi: An aiko shi a Makka, 27 Rajab; yana dan shekara 40.
Koyarwar sakonsa: ya zo don daidaito tsakanin dukkan halitta da ‘yan’uwantaka da rangwame, sa’annan ya kafa shari’a madaukakiya da dokoki na adalci da ya karbo daga wajan Allah(swt), su kuma Musulmi s**a karba daga gare shi.
Mu’ujizozinsa: Mu’ujizarsa madauwamiya ita ce Qur’ani, amma wadanda s**a faru a farkon Musulunci suna da yawa; ba zasu kirgu ba, misali, tsagewar wata.
Kiransa
Ya kira mutane zuwa ga Tauhidi a Makka a boye shekara 3, ya kuma kira su a bayyane shekara 10.
Hijirarsa:
ya yi hijira daga Makka zuwa Madina a farkon watan Rabi’ul Auwal, bayan shekara 13 daga aikosa, wannan ya faru ne sak**akon cutarwa daga kafirai; gare shi da kuma Sahabbansa.
https://youtube.com/channel/UCjESFp9bFn