21/08/2026
MAZAN JIYA
Marigayi Sheikh Abbas Hamid Abbas BUK ya bar duniya yana da shekaru 86.
Sheikh yana daya daga cikin manyan malamai na Ahlus-Sunnah a wannan kasa wadanda s**a yi gwagwarmaya wajen karantar da Sunnah, musamman a karkashin wannan kungiya mai albarka: Jama'atu Izalatil Bid'ah Wa'ikamatis Sunnah, wadda hedkwatarta ke Jos, Nigeria.
Malam ya rasu a ranar Juma'a, 21 ga watan Nuwamba 2008 a birnin Kano, kuma a ranar aka yi masa Jana'iza.
Sheikh Abbas limamin Juma'a ne a babban Masallacin Juma'a na Jami'ar Bayero University Kano, BUK.
Kuma shine Shugaban Majalisar Malamai na kungiyar Izala ta Jihar Kano na farko kafin Marigayi Sheikh Jafar Mahmud Adam. Bayan Sheikh Jafar ya tafi karatu a Madina, sai aka sake bawa Sheikh Abbas ya rike wannan mukami har zuwa kafin rasuwarsa.
Sheikh wa'azinsa na karshe a matakin kasa da kasa shine Wa'azin Kasa da aka gudanar a filin Polo, a Maiduguri, Jihar Borno a shekarar 2008, shekarar da ya rasu. A lokacin yayi wa'azi sosai akan masu ra'ayin Boko Haram kuma da harshen Kanuri yayi wa'azin.
Asalinsa kabilar Shuwa ne, kuma dan karamar hukumar Kala/Balge ne a Jihar Borno. Dalilin neman ilimi ne ya kaishi Jihar Kano, har ya zama ya rike wadannan mukamai masu daraja.
Allah ya jikansa, ya gafarta masa, ya haskaka kabarinsa. Ameen.
Jibwis Internet Media Committee
JIBWIS National HQ Jos- Nigeria 🇳🇬
Friday, 21st August, 2026
[email protected]