19/04/2026
MUSLIM COUNCIL TA JIHAR GOMBE TA SASANTA TSAKANIN JIBWIS BANGAREN JOS DA FITIYANUL ISLAM A GARIN BIRIN FULANI, JIHAR GOMBE.
A kokarin tabbatar da zaman lafiya da hadin kai a tsakanin al’ummar Musulmi, Muslim Council ta Jihar Gombe ta samu nasarar jagorantar sulhu tsakanin bangarorin Kungiyar JIBWIS (Jos) da Kungiyar Fitiyanul Islam a garin Birin Fulani, dake Karamar Hukumar Nafada.
Wannan mataki ya biyo bayan hatsaniyar da ta faru a ranar 26 ga watan Ramadan, yayin gudanar da tafsiri, inda aka samu sabani tsakanin mambobin JIBWIS Bangaren Jos da wasu membobin Kungiyar Fitiyanul Islam. Lamarin ya janyo damuwa ga al’umma, wanda hakan ya sa Maigirma Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ba Muslim Council amanar shiga tsakani domin sulhunta bangarorin.
A yau Asabar 30/Shawwal,1447 wadda yayi dai dai da 18 ga Afrilu, 2026, Majalisar Muslim Council ya kai ziyara garin Birin Fuani, inda aka gudanar da zaman sulhu cikin kwanciyar hankali tare da halartar manyan jami’ai da shugabanni, ciki har da Shugaban Karamar Hukumar Nafada, Alhaji Babangida Adamu Jigawa, Mai Martaba Sarkin Nafada, Alhaji Muhammadu Dadum Hamza, Wakilin Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Gombe, DPO na Karamar Hukumar Nafada, hakimi, da sauran jami’an tsaro na farin kaya da Civil Defence.
Majalisar Muslim Council ya kunshi manyan malamai da shugabanni daga bangarori daban-daban, ciki har da:
Grand Khadi Baba Liman daga JNI (Shugaban Council)
Sheikh Hamza Adamu Abdulhamid (Shugaban Majalisar Malamai JIBWIS Jos)
Member
Sheikh Salisu Muhammad Gombe (Shugaban Kungiyar JIBWIS Kaduna)
Member
Sheikh Bashir Ladan (Shugaban Fitiyanul Islam, Gombe)
Member
Sheikh Naziru Idris (Fitiyanul Islam)
Member
Sheikh Adamu Girbo (JIBWIS Jos)
Member
Sheikh Abdulmumini Ibrahim Naibi (wakilin Sheikh Usman Isa Taliyawa)
Member
Farfesa Dahiru Inuwa Ibrahim (Sakataren Council kuma Babban Limamin Jami’ar Jihar Gombe)
A yayin zaman, an saurari jawaban dukkan jagororin da mahalarta taro, inda aka jaddada muhimmancin hakuri, yafiya, fahimtar juna da kuma zaman lafiya a tsakanin al’umma. Malaman sun yi kira ga al’umma da su kauce wa duk wani abu da zai haddasa rikici, da daukan doka a Hannu, tare da karfafa alaka ta addini da zumunci.
Alhamdulillah, an samu gagarumar nasara inda bangarorin s**a amince da sulhu, tare da rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a gaban hukumomi, ciki har da Shugaban Karamar Hukuma, Kwamishinan Yansanda da DPO na Karamar Hukumar Nafada.
Haka zalika, taron ya jawo hankalin matasa da iyaye kan muhimmancin tarbiyya ta gari da riko da koyarwar addini, domin gujewa duk wani abu da zai kawo barazana ga zaman lafiya.
A karshe, Majalisar Muslim Council ta mika godiya ta musamman ga Maigirma Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa hangen nesansa da kuma dacewar da ya yi na dorawa Council din wannan muhimmin nauyi, wanda ya haifar da daidaito da kwanciyar hankali a yankin.
Wannan sulhu na zama wani abin koyi ga sauran al’ummomi wajen warware sabani ta hanyar tattaunawa da fahimtar juna.
Salisu Muhammad Gombe
Sakataren Yada Labaru
Muslim Council Gombe State.
SULHU IZALA DA DARIKA BIRIN FULANI GOMBE STATE