The Beauty of Islam

The Beauty of Islam "They intend to extinguish Allah's light wit their utterances: but Allah has willed to spread His light in all its fullness,...."
[Q:61:8]

29/12/2025

*🤝𝘽𝘼𝙍𝙆𝘼𝙉𝙈𝙐 𝘿𝘼 𝙎𝘼𝙁𝙄𝙔𝘼🤝*
Hakuri wani babban hali ne da ya kunshi juriya, natsuwa da kuma fahimta a cikin dukkan al'amuran rayuwa. Duk wanda Allah Ya azurta da karfin hakuri, to hakika an bashi wani babban arziki da ba kowa ke da sa'a ya samu ba. Hakuri shi ne ke hana mutum aikata kuskure a lokacin fushi, shi ne ke hana yanke kauna a lokacin tsanani, shi ne kuma ke tabbatar da cikar buri a cikin lokaci.

*AN KARBO DAGA ABU HURAIRA ALLAH YAKARA MASA YADDA YACE, MANZAN ALLAH S.A.W. YACE**"Za amiƙa haƙƙo ƙi ga ma abotansu ran...
04/11/2025

*AN KARBO DAGA ABU HURAIRA ALLAH YAKARA MASA YADDA YACE, MANZAN ALLAH S.A.W. YACE*

*"Za amiƙa haƙƙo ƙi ga ma abotansu ranar alkiyama, hatta tinkiya me ƙaho data tunkuyi mara ƙaho, sai anyi hisabi a tsakanin su.*

*Mutum yaji tsoron Allah, ranar alkiyama za a yiwa kowa adalci, ranar babu zalunci, dukkan abinda ka shuka shi zaka girba, dukkan wanda ka zalunta a wannan rana Allah saiya biyashi hakkin sa, ranar babu kudi, babu ikon biya, saidai aɗibi kyakkyawan ayyukan ka azuba masa, idan kuma baka da su, za adebo zunuban wancan azuba maka, yan uwa muji tsoron wannan rana, hatta tinkiyar data tunkuyi yar uwatta a gidan duniya saboda tafita karfi, Allah zai tsaida su agaban sa yace ta rama, idan aka gama musu sai ace duka su zama ƙasa, tokai dan adam ba kasa za ace ka zama ba, babbaka ka Allah zai yi awuta, Allah ka kiyayemu ameeen.*

03/11/2025

> يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا عَلَيْكُمْ أَنْفُسَكُمْ لَا يَضُرُّكُمْ مَنْ ضَلَّ إِذَا اهْتَدَيْتُمْ إِلَى اللَّهِ مَرْجِعُكُمْ جَمِيعًا فَيُنَبِّئُكُمْ بِمَا كُنْتُمْ تَعْمَلُونَ

Ya ku waɗanda kuka yi imani! Ku kula da kanku.
Ba wanda ya bata zai iya cutar da ku idan kun kasance kan hanya madaidaiciya.
Zuwa ga Allah ne wurin komawarku gaba ɗaya, sannan zai sanar da ku abin da kuka kasance kuna aikatawa.

Bayani (taƙaitaccen tafsiri):

Wannan aya tana umartar musulmi da su kula da kansu wajen bin gaskiya da bin umarnin Allah.

Idan mutum ya tsira ta hanyar bin shiriya, batawar wasu ba zai cutar da shi ba, matuƙar ya tsaya kan gaskiya.

Amma ba yana nufin a daina yi wa mutane wa’azi ba; malamai sun ce har yanzu wajibi ne a kira zuwa alheri da hani daga mummuna idan ana iya yi.

Allah ne zai hukunta kowa bisa ayyukansa a ranar ƙiyama.

01/11/2025

HANYOYIN SAMUN YARDAR ALLAH GUDA ASHIRIN:

1. AKIDA: Yin imani da Allah shi kaɗai.

2. BIN SUNNAH:Bin koyarwar Annabi Muhammad ﷺ.

3. GIRMAMA SAHABBAI: Girmama abokan Annabi ﷺ.

4. YAWAN KARATUN ALQUR'ANI: Karanta Al-Qur’ani akai-akai.

5. KOYA WA MUTANE: QUR'ANI ’ani: Taimaka musu su koyi karatu.

6. YIN SALLAH AKAN LOKACI: Kada a jinkirta sallah.

7. SADA ZUMUNTA: Ziyarar ‘yan uwa da kyautata zumunci.

8. HAKURI: Jure wa jarabawa da godiya ga Allah.

9. KANKAN -DA-KAI: Gujewa girman kai da nuna tawali’u.

10. TARBIYYA: Kyautata hali da aikata nagarta.

11. FADAR GASKIYA: Kada a yi ƙarya.

12. RIKE AMANA: Cika alkawari da abin da aka ɗora maka.

13. YAWAN ISTIGFARI: Neman gafarar Allah da yawa.

14. YAWAN SALATIN ANNABI ﷺ : Yin salati gare shi akai-akai.

15. KIYAYE SIRRIN AURE: Kada miji ko mata su fallasa sirrinsu.

16. YAWAN NAFILFILU: Yin ƙarin ibada bayan farilla.

17. KIYAYE HAKKIN: makota Nuna alheri da tausayi ga makoci.

18. BIYAN BASHI DA WURI: Kada a jinkirta biya idan ana da hali.

19. RAKA GAWA: Halartar jana’iza da yin addu’a ga mamaci.

20. TUNANIN LAHIRA: Tunanin mutuwa da hisabi akai-akai.

Shaykh Muhammad Bin Uthman [hafizahullah]

22/10/2025
22/10/2025

قُلْ إِنَّمَا أَنَا بَشَرٌ مِثْلُكُمْ يُوحَىٰ إِلَيَّ أَنَّمَا إِلَٰهُكُمْ إِلَٰهٌ وَاحِدٌ ۖ فَمَنْ كَانَ يَرْجُو لِقَاءَ رَبِّهِ فَلْيَعْمَلْ عَمَلًا صَالِحًا وَلَا يُشْرِكْ بِعِبَادَةِ رَبِّهِ أَحَدًا

(Suratul Al-Kahf: 110)

Ma’anar Ayar (a Hausa):
Ka ce (Ya Muhammad ﷺ): Ni mutum ne kamar ku, sai dai ana yi mini wahayi cewa abin bautarku ɗaya ne — Allah. Saboda haka wanda yake fatan saduwa da Ubangijinsa, to ya aikata aiki nagari, kuma kada ya haɗa wani da shi a cikin ibadar Ubangijinsa.
Tafsirin Ayar daga Malamai:
• Ibn Kathir (رحمه الله) ya ce: Wannan ayar tana tabbatar da cewa Annabi ﷺ mutum ne, amma Allah Ya fifita shi da wahayi. Bai da wani iko na gaiba sai abin da Allah Ya sanar da shi.

• Al-Jalalayn ya ce: Manzon Allah (ﷺ) ana masa umarni ya bayyana cewa wahayi ne ke bambanta shi da sauran mutane, domin kada a ɗaukarsa a matsayin abin bauta.

• Ayar ta ƙarshe tana nuni da cewa babu karɓuwar aiki sai da niyya mai tsabta da bin tauhidi.
Darussa daga Ayar:
1. Annabi Muhammad ﷺ mutum ne kamar sauran mutane, amma an fifita shi da wahayi.
2. Tauhidi (bautar Allah shi kaɗai) shi ne ginshiƙin imani.
3. Aiki mai kyau ba ya karɓuwa sai da tsarkakakkiyar niyya.
4. Wanda yake fatan saduwa da Ubangiji, to ya tsarkake ibadarsa daga shirka.
5. Shirka tana lalata dukkan aikin nagari.
A takaice, ayar nan tana kiran mu da mu sani cewa Annabi ﷺ mai isar da saƙo ne daga Allah, kuma manufar rayuwa ita ce bauta wa Allah shi kaɗai cikin gaskiya da aiki nagari.

Address

Kiyawa
Jigawa

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when The Beauty of Islam posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to The Beauty of Islam:

Share