Muslims Ummah NG

Muslims Ummah NG Assalamu-Alaikum! Yan'uwa MUSULMAI wannan Page munyi shi ne domin tunatar da yan uwanmu musulmai.

09/05/2017

18. TAMBAYA: Malam kayi bayani idan mutun ya fito daga makewayi(ban daki) anason yayi arwala?
AMSA: wannan haka yake, ya tabbata a hadisin da Imamu Ahmad ya ruwaito Manzon Allah yakasance idan ya fito daga bandaki(makewayi) yana yin arwala.

09/05/2017

17. TAMBAYA: To kuma karatun jiya kayi bayanin Manzon Allah yana aje kasko cikin daki da dare yayi fitsari ciki, to ya ya hukuncin wadannan hadisai?
AMSA: Imamul Albaniy yayi bayanin yanda zamu hada wadannan hadisai, shine, ba ason fitsarin ya jima ( ya dauki dogon lokaci ) cikin daki, ba’a zubar dashi ba, kenan idan safiya tayi za’aje a zubar dashi, idan ba’a zubar bane mala’ikun rahama basu shiga [ DUBA LITTAFIN
SILSILATUL SAHIHA HADISI 2517 ] .

09/05/2017

16. TAMBAYA: Malam kayi bayanin baya halatta barin fitsari a Daki, domin Mala’ikun Rahma basu shiga?
AMSA: Haka ne.

09/05/2017

15. TAMBAYA: Kenan malam bani taimama inyi sallar gawa?
AMSA: Matukar akwai ruwa kuma kana iya aiki dasu, to baya halatta, sai dai idan kayi tsalki daga baya kaje wurin kabarin kayi masa sallah, da sharadin kada ya wuce kwana talatin (30) cikin kabarinsa [DUBA FATAWAL-LAJANATID DA’IMA 4/177].

09/05/2017

14. TAMBAYA: Toh idan rakiya ce zaiyi zuwa kabari?
AMSA: Wannan babu laifi.

09/05/2017

13. TAMBAYA: Ko yana halatta mai janaba ya raki gawa idan yayi taimama?
AMSA: Idan Salla ce zaiyi gareta baya halatta.

09/05/2017

12. TAMBAYA: Shin ko yana halatta yin taimama saman dutsi ko shimfida?

AMSA: Na’am, idan akwai gasa saman su ya halatta, idan babu baya halatta.

09/05/2017

11. TAMBAYA: Idan mutun ya shafi al’aurarsa cikin wanka shin wajibi ne ya sake arwala?

AMSA: Shafar al’aura yana da magana biyu wurin malamai, amma Sheikh Islam Ibn Taimiyya yana cewa “idan mutum ya shafi al’aurasa domin sha’awa wajibi ne ya sake arwala, amma idan badon sha’awa bane to baya sakewa, Imamu Malik kuma yace naso ga wanda ya shafi al’aurarsa da ya sake arwala.

---wannan yana nuna shafar al’aura baya walwale arwala wurin imamu, kawai anso ne mutum yayi arwala, sabanin abinda muke karantawa cikin wasu littafai---

09/05/2017

10. TAMBAYA: Malam mutum ne sha’awa ta kamashi har yaji alamar fitowar maniyyi amma kuma sai bai fito ba shin akwai wanka gareshi?

AMSA: Wannan shi malamai ke kira (INTIQALIL MANIYYI) waton zaburowar maniyyi amma kuma bai fito ba, anan malamai sunyi sabanin fahimta, wasu s**a ce wajibi ne yayi wanka domin sha’awa ta kamashi, wasu kuma s**a ce wanka bai wajaba gareshi ba, domin maniyyi bai fito ba , wanna shine zance mafi inganci. Kamar yanda Sheikh Salihu Fauzan Da Ibn Baz da Sauran malamai s**ayi bayani.

09/05/2017

9. TAMBAYA: Idan mutun ya yi arwala sai s**a hada hannu da kafiri arwalarsa tana nan ko ta walwale?

AMSA: Wannan baya walwale arwalar mutum, kamar yanda Sheikh Bakar Abu Zaid da sauran malamai s**ayi bayani.

09/05/2017

8. TAMBAYA: Malam shin habo ( jinin da yake fitowa a hanci) yana bata Sallah?

AMSA: Duk abinda yake najasa , idan ya fito wani wuri bayan hanyoyi biyu,( ta al’aura ko dubura) to baya bata Sallah sai idan yazo da yawa sosai . kamar yanda aka ruwaito daga Ibn Abbas da Abu Huraira da Ibn Umar, da wasu daga magabata masu yawa. [ DUBA LITTAFIN LAJANATID DA’IMA 4/113]

---duk da malamai sunyi sabani akan jini najasa ne koba najasa bane, shi jinin haila duk malamai sun tafi akan najasa ne, amma wanda bashiba , da yawan malamai sun tafi akan ba najasa bane.---

09/05/2017

7. TAMBAYA: Mutum ne yana sallah sai Maziyyi ya fito masa ya matsayin sallar sa?

AMSA: Sallar ta bace tare da arwalarsa, sai yaje yayi tsalki ya sake arwala, sannan ya sake SALLAH.

Address

Tudun Wada
Jega

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muslims Ummah NG posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share