07/08/2026
Shugaban ƙungiyar Izala, Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau, a madadin kungiyar da haɗin gwuiwar kungiyar Haɗa kan Musulmai ta duniya (RABIƊATUL ALAMIL ISLAMIY, na gayyatar Al'ummar musulmi zuwa gagarumin taron ƙarawa juna ilimi mai taken 'BAMBANCE BAMBANCE TARE DA ZAMAN LAFIYAR JAMA’A”
Taron wanda 'HAƊIN GUIWA NE TSAKANIN KUNGIYAR HAƊA KAN MUSULULMAI TA DUNIYA, MAI CIBIYA A ƘASAR SAUDIYYA (RABIƊATUL ALAMIL ISLAMIY DA ƘUNGIYAR WA'AZIN MUSULUNCI TA KASAR NAJERIYA, JAMA'ATU IZALATIL BID'AH WA IKAMATIS SUNNAH.
-Za a buɗe taron conference ranar talata 11/August/2026 da misalin karfe tara na safe (9:00am) a kuma gama ranar laraba 12/August/2026 da rana 2:30pm.
-Za'a gabatar da Wa'azin kasa a harabar Masallacin JIBWIS dake helkwatar kungiyar a unguwar Utako dake birnin tarayya Abuja, daga yammacin laraba har zuwa daren alhamis.
-Safiyar alhamis 14/August/2026 kuma sai jama'a su koma garuruwansu.
Babban bako na Musamman, Shugaban ƙasar Najeriya, Alhaji Ahmad Bola Tunibu.
Uban Taro: Mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Abubakar Sa'ad
Sauran manyan Baki sun haɗa da:
Gwamnoni Ministoci, Yan majalisu na tarayya da na jahohi, Iyaye Maluma, Sarakuna, yan kasuwa da sauran yan uwa musulmi dake fadin Naijeriya da sauran ƙasashen ketare.
Ana sa ran halartar manyan bakin Malamai daga manyan ƙasashen duniya insha Allah.
Sanarwa daga Sakataren JIBWIS' na ƙasa Sheikh Dr Muhammad Kabir Haruna Gombe, ta ofishin kwamitin Labaru na babban taron....
Jibwis Nigeria