19/06/2023
KU BA DA FATUN LAYYARKU SADAKA:
Dr. Ibrahim Jalo Jalingo
1. Muna kira ga al'ummar musulmin Nigeria su ba wa kungiyar Izala ta Kasa sadakar fatun layyarsu domin ci gaba da manyan ayyukan Da'awah da Kungiyar ke yi ciki har da ginin jami'ar As-Sallam a garin Hadeja.
2. Sannan muna tunatar da limaman masallatanmu na juma'a da Idi, da masu pre-huduba na dukkan masallatan da cewa su fadakar da Al’umma muhimmancin ba da sadakar fatun layyarsu ga ita Kungiya.
3. Lalle fadakarwar masu pre-huduba tana da muhimmanci, saboda muhimmancin da ita kanta pre-hudubar take da shi; روى الامام الحاكم في المستدرك: ٦١٧٣ عن عاصم بن محمد عن ابيه قال: رايت ابا هريرة رضي الله عنه يخرج يوم الجمعة فيقبض على رمانتي المنبر قائما ويقول: حدثنا ابو القاسم رسول الله الصادق المصدوق صلى الله عليه وسلم. فلا يزال يحدث حتى اذا سمع فتح باب المقصورة لخروج الامام للصلاة جلس)). صححه المولف ووافقه الذهبي.
4. Allah Ya taimake mu. Ameen.