24/05/2026
🕌🕌SADAƘAR FATUN LAYYAH🕌🕌
Ƙungiyar Izalah ta karamar hukumar Haɗejia ƙarƙashin Jagorancin Shugaba Sheikh Mu'az Idris Mua'az, ta kafa kwmt dazai tabbatar da nasarar tara sadakar fatun Layya, Ga kungiyar kamar yadda muka saba Zama Zakara a Duk Shekara.
Kwamatin ƙarƙashin Jagorancin sakatare na wannan ƙungiya Malam Aminu Hassan Hadejia. Na miƙa gdy ga dukkan Musulmai dake bawa wannan aiki gudummawa a kowace Shekara. Mussmman fadar maimartaba Sarkin Haɗejia Alhaji Dr. Adamu Abubakar Maje CON, Saboda gagaumar gudummawar su.
A bana an tsara ayyukan karɓar fatun kamar haka:
1- Dukkan Majalisai da Masallatan mu su tabbatar da karbar fata da kuma kula da sa mata gishiri kafin karɓa.
2- ƴan agaji masu kayan Sarki kaɗai aka yarda a bawa Fatu da aka tara a Majalisai da Masallatai.
3- Majalisai dake Lunguna su taimaka su kawo fatun su bakin T**i don saukin ɗauka.
4- Ana iya kawo Fata da ƙirgi kai tsaye a Babbar cibiyar Tattara fatu dake Babban Masallacin Izalah Unguwar Matsaro,Haɗejia.
5- A kula da masu Fiɗa saboda gudun asarar fatu kamar yadda aka samu hakan a bara. A samu wanda S**a iya kuma asa gishiri.
6- Akwai Risitai na gudummar Kuɗi musamman ga wanda basu samu yin layya ba. Akwai ₦100.₦500. Sai a kawo masallatai dake kusa.
Zaa iya tuntuɓar waɗannan Lambobi don karɓar Fatun Kamar haka:
07032669478
08138297994
08066001913
08063157445
07036122995
08033897966.
✒️✒️✒️✒️✒️
Abu-Humairaa
Jibwis Haɗejia
24/05/2026