10/07/2025
MALLAM LAWAN TRIUMPH, GASKIYA DAYA CE: ABINDA YA FARU YAU A SHARI'A COMMISSION TA JIHAR KANO...
An samu wasu gungun mutane masu son tayar da hankalin al'umma, masu son nemawa Abduljabbar abokin mutuwa ta ko wane irin hali, s**a ta shi s**a tafi Shari'a Commission su ka kai korafi akan kazafi, sharri, da juya maganar da s**a yi wa Sheikh Lawan Abubakar Triumph. Kuma a karon farko Shari'a Commission ya dauki zafi akan lamarin bisa irin korafe-korafen da aka shigar mata. Wanda hakan ya sa su ka gayyaci Mallam din.
Bayan isar su Sheikh Lawan Triumph a wajen, an so a fara yin maganganu, sai Mallam Lawan Ya ce: "Kafin a yi nisa a cikin bayani, shin an saurari ainahin maganganun da ake magana a kansu?" Aka ce ba'a saurara ba. Sai aka ce to a kunna kowa ya ji.
Ana kunna Audio din Mallam Lawan, sai jikin kowa ya yi sanyi a wurin. Nan da nan kuma sai masu korafi s**a koma kame-kame da neman a zauna lafiya. Da alama ko dai su ma duk jita-jita su ka bi, ko kuma sun san ba haka abin yake ba, amma kawai so suke dole sai an shafa wa Mallam Lawan bakin fenti.
Bayan an kunna Audio din, sai wani jigo a Shari'a Commission, Mallam Ali Dan Abba, sau biyu yana tambaya ko akwai mai magana a cikin waɗanda s**a dauki zafi a hukumar a karon farko? Shiru, ya kuma tambaya, akwai mai tambaya ko neman karin bayani? Amma Shiru.
Kafin batun Shari'a Commission, muna da labarin an kira DSS an kai musu korafi su ma. Sannan ana cigaba da wasu kulle-kullen.
Abinda mu so ku sani shi ne:
1. A ko yaushe gaskiya ce take yin Nasara
2. Karya, sharri, kage, da kulle-kulle, ba hanya ce da za ta bulle wa magauta ba.
3. Da gaskiya mu ke yin addini, kuma da wayewa, mun fi karfin cin mutunci ko dauki dai-dai.
4. Kaunar Annabi SAW mu ke yi da gaske. Allah Ya kiyaye, da ace wani a cikinmu zai yi gangancin aikata laifin da makiya suke zargi a yanzu, da mu ne zamu fara yaƙarsa kafin kowa. Amma duk wanda za'a yi wa sharri a cikinmu, za ku kare shi da iyaka karfin da Allah Ya h**e mana, domin mu aka taba gaba.