22/11/2021
*WANKAN GAWA DA YADDA AKEYINSA.*
*DON ALLAH MU KARANTA KUMA MU YI SHERING ZUWA 3 GA SAURAN ƳAN UWA MUSULMAI.*
SABODA YANZU ABUN YA ZAMA MATSALA TA WANNAN AL'AMMARIN, IDAN ANYI MUTUWA SAI KAGA AN RASA MAI YIWA WANNAN GAWAR WANKA, KO
KUMA KAGA MALAMIN DA ZAIYI
WANKAN YANA TA MULKI SAI LOKACIN DAYA GA DAMA ZAI ZO YAYI WANKAN.
ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI.
FALALAR WANKAN GAWA.
Al-Imam Hakim ya rawaito hadisi
Wanda Manzon Allah (S.A.W)
Yake cewa: ‘’Duk wanda ya wanke
mamaci, kuma ya rufa masa
asiri, Allah Zai gafarta masa sau
arba’in.’’
A wani hadisin kuma Manzon Allah
(S.A.W) Yace, ”Duk wanda ya
wanke mamaci kuma ya rufa masa
asiri, to Allah zai tufatar dashi daga cikin tufafin Gidan Aljanna Kwarra (wato Launin Tufafin).
SHARUƊƊAN WANKAN GAWA.
Daga cikin sharaɗan wankan gawa
sune:-
1. Ana buƙatar waɗanda zasu wanke
mamacin su zamanto makusantan sa (misali, Iyaye, ƙanne, yayye, ko ƴaƴa, da sauransu).
2. Ana buƙatar maza su jiɓinci wanke maza, suma mata su jiɓinci wanke mata (sai dai Miji zai iya wanke Matarsa hakama Mace zata iya wanke Mijinta).
3. Ba sharaɗi bane lallai sai anyi
amfani da ruwan zafi ba.
YADDA AKE YIN WANKAN GAWA
Ana yin wankan gawa mara-mara ne
(misali, Sau Uku(3) ko Biyar(5) ko Bakwai(7) ko Tara(9)).
Hakan ya tabbata daga Manzon Allah (S.A.W) a cikin hadisin Ummu Adiya(R.A).
Waɗanda zasu yi wa mamaci wanka su zasu yi la’akari suga wanka nawa ya dace suyi masa.
Da farko dai kafin a fara wankan
akwai abubuwa guda Uku(3) da za’a fara yi wa mamacin. Su ne kamar haka:-
1. Za’a cire masa suturar da take
jikinsa, amma za’a sami ɗan kyalle a rufe masa al’aurarsa.
2. Bayan anyi abu na sama, sai kuma ayi masa tsarki, na ɓangaren mafita biyu wato (Bawali da Gayadi).
3. Idan macace, za’a tsefe kitsan dake kanta, a wanke kan, sannan ayi Lallaɓi uku a kan ( wato Kalba guda Uku). Sai a kwantar da Kalbar tayi bayan kan nata.
Idan namiji mai kitso ne sai a warware kitson gaba ɗaya.
YADDA AKE WANKA SAU UKU (3)
Idan masu yiwa mamaci wanka sun