Khalifa Aliyu Alti

Khalifa Aliyu Alti الحمدلله

‎Muhimmancin Sadar da Zumunta (Silatur-Rahim).‎‎Sadar da zumunci yana nufin kyautatawa ga 'yan'uwa na jini (k**ar iyaye,...
10/01/2026

‎Muhimmancin Sadar da Zumunta (Silatur-Rahim).

‎Sadar da zumunci yana nufin kyautatawa ga 'yan'uwa na jini (k**ar iyaye, yayye, ƙannai, kawunnai, gwaggonni, da sauransu) ta hanyar ziyara, taimako, gaisuwa, da kyautata musu zato.

‎ALLAH (SWT) ya haɗa jin tsoronSa da kiyaye zumunci a wuri ɗaya don nuna girman al'amarin.

‎" وَاتَّقُوا اللَّهَ الَّذِي تَسَاءَلُونَ بِهِ وَالْأَرْحَامَ ۚ إِنَّ اللَّهَ كَانَ عَلَيْكُمْ رَقِيبًا.."


‎Manzon ALLAH (SAW) ya ce:
‎" مَنْ سَرَّهُ أَنْ يُبْسَطَ لَهُ فِي رِزْقِهِ، أَوْ يُنْسَأَ لَهُ فِي أَثَرِهِ، فَلْيَصِلْ رَحِمَهُ"

‎"Wanda yake son a yalwata masa a cikin arzikinsa, ko a jinkirta masa ajalinsa (a sanya albarka a rayuwarsa), to ya sadar da zumuncinsa."


‎A wani hadisin kuma, Annabi (SAW) ya yi gargaɗi:

‎" لاَ يَدْخُلُ الْجَنَّةَ قَاطِعٌ"

‎"Mai yanke zumunci ba zai shiga Aljannah ba."

‎Darussan da ke ciki:
‎•Hanyar Samun Arziƙi: Mutane da yawa su na neman kuɗi ido rufe, amma sun manta cewa kyautatawa 'yan'uwa makusanta yana ɗaya daga cikin manyan asiran buɗewar kofofin arziki.
‎•Haɗin Kai: Zumunci yana ƙarfafa soyayya da haɗin kai a cikin dangi.
‎•Tsoron ALLAH: Yanke zumunci babban zunubi ne da ke iya hana mutum shiga Aljannah, koda kuwa yana yawan sallah da azumi.

‎Ya ALLAH ka bamu ikon sadar da zumuntar mu, albarkar Annabi Sallallahu Alaihi Wa Sallam.

Mene ne ya k**aci wanda annoba ta faɗa a garin da yake?(Jumhūr) na Malamai: Makruh ne ma'ana; (Ba a so mutum ya shiga ko...
30/12/2025

Mene ne ya k**aci wanda annoba ta faɗa a garin da yake?

(Jumhūr) na Malamai: Makruh ne ma'ana; (Ba a so mutum ya shiga ko ya fita garin ba).

أَيْنَمَا تَكُونُوا يُدْرِككُّمُ الْمَوْتُ وَلَوْ كُنتُمْ فِي بُرُوجٍ مُّشَيَّدَةٍ ۗ وَإِن تُصِبْهُمْ حَسَنَةٌ يَقُولُوا هَٰذِهِ مِنْ عِندِ اللَّهِ ۖ وَإِن تُصِبْهُمْ سَيِّئَةٌ يَقُولُوا هَٰذِهِ مِنْ عِندِكَ ۚ قُلْ كُلٌّ مِّنْ عِندِ اللَّهِ ۖ فَمَالِ هَٰؤُلَاءِ الْقَوْمِ لَا يَكَادُونَ
يَفْقَهُونَ حَدِيثًا

"Duk inda kuka kasance, mutuwa za ta riske ku, ko da kun kasance a cikin manyan hasumiyoyi masu ƙarfi. Idan wani abin alheri/mai kyau ya same su, sai su ce: ‘Wannan daga ALLAH ne’; idan kuma wani abu mummuna ya same su, sai su ce: ‘Wannan daga gare ka ne.’ Ka ce: ‘Dukkaninsu daga wajen ALLAH ne....."

وَأَنفِقُوا فِي سَبِيلِ اللَّهِ وَلَا تُلْقُوا بِأَيْدِيكُمْ إِلَى التَّهْلُكَةِ ۛ وَأَحْسِنُوا ۛ إِنَّ اللَّهَ يُحِبُّ الْمُحْسِنِينَ

Hadisin Usamatu bn Zayd (R.A):

عَنْ أُسَامَةَ بْنِ زَيْدٍ رضي الله عنهما، قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللَّهِ ﷺ:
إِذَا سَمِعْتُمْ بِالطَّاعُونِ بِأَرْضٍ فَلَا تَدْخُلُوهَا، وَإِذَا وَقَعَ بِأَرْضٍ وَأَنْتُمْ بِهَا فَلَا تَخْرُجُوا فِرَارًا مِنْهُ.
متفق عليه

Idan ku ka ji annoba ta bayyana a wata ƙasa, kada ku shiga cikinta. Idan kuma ta same ku alhali kuna a cikinta, kada ku fita domin guje ma ta.”

ALLAH ya tsare mu, albarkar Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam).

‎Shin Musulmi zai gaji gadon mahaifinsa wanda ba Musulmi ba?‎‎Malamai sun yarda cewa: Musulmi ba zai gaji dukiyar wanda ...
28/12/2025

‎Shin Musulmi zai gaji gadon mahaifinsa wanda ba Musulmi ba?

‎Malamai sun yarda cewa: Musulmi ba zai gaji dukiyar wanda ba Musulmi ba kai tsaye.

‎Hanya ɗaya ce kawai idan mahaifin ya yi wasiyya ga ɗansa Musulmi, kuma ba ta wuce 1/3 na dukiyar ba.

‎ كُتِبَ عَلَيْكُمْ إِذَا حَضَرَ أَحَدَكُمُ الْمَوْتُ إِنْ تَرَكَ خَيْرًا ٱلْوَصِيَّةُ لِلْوَٰلِدَيْنِ وَٱلْأَقْرَبِينَ بِٱلْمَعْرُوفِ ۖ حَقًّا عَلَى ٱلْمُتَّقِينَ


‎Wannan aya ta nuna cewa wasiyya ce kaɗai abinda musulmi zai iya karɓa daga abinda mahaifinsa ya bari na gado, idan mahaifin nasa ya zamo wanda ba Musulmi ba.


‎ وَلَا يَحْسَبَنَّ الَّذِينَ يَبْخَلُونَ بِمَا آتَاهُمُ اللَّهُ مِنْ فَضْلِهِ هُوَ خَيْرًا لَّهُمْ ۖ بَلْ هُوَ شَرٌّ لَّهُمْ ۖ سَيُطَوَّقُونَ مَا بَخِلُوا بِهِ يَوْمَ الْقِيَامَةِ ۗ وَلِلَّهِ مِيرَاثُ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۗ وَاللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ خَبِيرٌ


‎Hadisin Ibn ‘Abbas (RA):

‎" لَا يَرِثُ الْمُسْلِمُ الْكَافِرَ وَلَا الْكَافِرُ الْمُسْلِمَ"

‎“Musulmi ba ya gadar kafiri, haka nan kafiri ba ya gadar Musulmi.”


‎Amma Wasiyya:

‎" أوصى النبي ﷺ بألا يزيد في الوصية على الثلث"

‎“Annabi ( S A W) ya umarci cewa kada wasiyya ta wuce 1/3 na dukiya.”

‎Wannan yana nuna cewa idan kafiri ya yi wasiyya ga ɗansa Musulmi, kada ta wuce kashi ɗaya bisa uku na dukiya.

ALLAH ya datar damu.

Ka taɓa auna hakan a tunani da ƙwaƙwalwar ka?Annabi Alaihissam ya ce:"تَفَكَّرُوا فِي خَلْقِ اللهِ وَلَا تَتَفَكَّرُوا ف...
25/12/2025

Ka taɓa auna hakan a tunani da ƙwaƙwalwar ka?

Annabi Alaihissam ya ce:

"تَفَكَّرُوا فِي خَلْقِ اللهِ وَلَا تَتَفَكَّرُوا فِي اللهِ فتهلكوا"

“Ku riƙa yin tunani a cikin halittar ALLAH, kuma ka da ku yi tunani game da ALLAH ( ta ya ALLAH ya halicci kan sa), sai ku halaka.”


Ya ishe ka girman ALLAH; za ka ji ƙamshin turare ko ka shafa turare ka ɗauki tsawon lokaci ba ka yi amfani da shi ba amma a duk ranar da ka ji ƙamshin sa za ka ce 'wannan kalar turare kaza ne', kuma fa ba tare da ka yi ajiyar sa a cikin hancin ka ba.

Wane ne ya isa yayi hakan in ba ALLAH ba!

Ka zauna ka natsu, za ka san girman ALLAH ya wuce abinda zukata zasu ɗauka. Kar ka bari shaiɗan ya ruɗe ka.

ALLAH ya datar damu.

Hukuncin Jinin Istihāḍa ga mata, ( shin za a yi Sallah, ko azumi) a lokacin jinin Istihāda?‎‎Mace ta ga jini yana fita a...
23/12/2025

Hukuncin Jinin Istihāḍa ga mata, ( shin za a yi Sallah, ko azumi) a lokacin jinin Istihāda?

‎Mace ta ga jini yana fita amma ba jinin al’ada (haid) ba, waton jinin istihāda (jinin cuta).
‎Shin za ta yi sallah? Za ta yi azumi? Yaya tsarkin ta yake?


‎Jinin Istihāda jini ne da yake zuwa bayan kwanakin al’ada, ko ya zo ba a lokacinsa ba.
‎Yakan kasance mai laushi ko ja mai haske, ba baƙi mai kauri ba.

‎Hukunci a taƙaice:
‎•Istihāda ba ya hana Sallah
‎•Ba ya hana azumi
‎•Mace mai tsarki ce, amma tana buƙatar tsari na musamman.


-‎Hadisin Fatima bint Abī Hubaysh رضي الله عنها:

‎" إِنَّمَا ذَلِكِ عِرْقٌ وَلَيْسَ بِالْحَيْضَةِ، فَإِذَا أَقْبَلَتِ الْحَيْضَةُ فَدَعِي الصَّلَاةَ، وَإِذَا أَدْبَرَتْ فَاغْسِلِي عَنْكِ الدَّمَ وَصَلِّي"

‎Abin da mace mai istihāḍa za ta yi:

‎•Wanke jini: Dole ne ta wanke wajen da jinin yake fita kafin kowace sallah.
‎•Alwala ga kowace sallah: Za ta yi alwala ne kawai idan lokacin sallah ya shiga. Misali, ba za ta yi alwala kafin kiran sallar azahar ba; sai an kira sannan za ta yi.
‎•Kiyayewa: Ana son ta sanya auduga ko wani abu da zai tare jinin domin kada ya bata tufafinta ko wurin sallah.

‎Hukuncin Zubar da Ciki a Musulunci(‎الإجهاض)‎‎Zubar da ciki shi ne ƙarar da rayuwar jariri a cikin mahaifa da gangan ka...
22/12/2025

‎Hukuncin Zubar da Ciki a Musulunci
(‎الإجهاض)

‎Zubar da ciki shi ne ƙarar da rayuwar jariri a cikin mahaifa da gangan kafin haihuwa.

‎Annabi ( Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya ce:

‎" إِنَّ أَحَدَكُمْ يُجْمَعُ خَلْقُهُ فِي بَطْنِ أُمِّهِ أَرْبَعِينَ يَوْمًا نُطْفَةً، ثُمَّ يَكُونُ عَلَقَةً مِثْلَ ذَلِكَ، ثُمَّ يَكُونُ مُضْغَةً مِثْلَ ذَلِكَ، ثُمَّ يُرْسَلُ إِلَيْهِ الْمَلَكُ فَيَنْفُخُ فِيهِ الرُّوحَ"

‎Ana busa Ruhi (Rai) ne bayan kwanaki 120.

‎Khilāf (Saɓani) na Farko: Zubar da ciki kafin kwanaki 120 Halal ne da uzuri daga wasu daga malaman:
‎-Hanafiyya
‎-Malikiyya

‎‎Sharaɗin haka (Wanda zai sanya zubar da ciki):
‎Tabbatacciyar buƙata ta hakan wanda ya sanya dole sai an yi hakan (k**ar hatsarin lafiya) idan ba a yi hakan ba zai zama barazana ga lafiya, ba tare da cutar da uwa ba.

‎‎Khilāf (Saɓani) na biyu: Haramun ne daga malamai irin su:
‎-Imam Malik
‎-Yawancin Hanabila
‎-Wasu daga Shafi’iyya

‎Sun dogara da ayar:

‎" وَلَا تَقْتُلُوا النَّفْسَ الَّتِي حَرَّمَ اللَّهُ"
‎(Al-An’am: 151)

‎Sun ce: rayuwa ta riga ta fara, ko da ba a busa ruhi ba.

‎Zubar da ciki bayan kwanaki 120

‎Ittifaqin Malamai 'HARAMUN' ne, kuma yana da hukuncin kisan rai.

‎Sai dai in:
‎Rayuwar uwa na cikin tabbataccen haɗari
‎Idan ba a zubar ba, uwa za ta iya mutuwa.
‎A nan:
‎Sai a ceci rayuwar uwa, saboda uwa asali ce, jariri kuma reshe ne.

‎Hukunci idan Zubar da ciki ya Faru:
‎-Diyya (Gurra):
‎Gurra a Fiqhu, musamman a mahallin zubar da ciki da diyya, yana nufin kuɗin da ake biya ga jariri da aka kashe kafin haihuwa, wato jaririn da aka zubar da cikin sa.

‎Annabi ( Sallallahu alaihi Wa Sallam) ya yanke hukunci:

‎" فِي الْجَنِينِ غُرَّةٌ"
‎“A kan jariri akwai diyya”


‎ALLAH ya datar da mu.

‎ Mene ne bambanci tsakanin Faskh (warware aure) da Khul’i (hul’i)?‎‎‎A Fiqhu, aure yarjejeniya ce da aka gina bisa gask...
21/12/2025

‎ Mene ne bambanci tsakanin Faskh (warware aure) da Khul’i (hul’i)?


‎A Fiqhu, aure yarjejeniya ce da aka gina bisa gaskiya da bayani (ṣidq da bayān). Idan aka samu cewa ɗaya daga cikin ma’aurata ya ɓoye wani aibi mai tsanani da zai hana cikar manufar aure, Shari’a ta ba wa wanda aka zalunta haƙƙin warware auren.

‎‎Faskh shi ne:

‎Rushe auren da alƙali ko hukuncin Shari’a saboda wani sharaɗi ko aibi da aka ɓoye tun a farko.
‎Ba namiji ya yi saki ba, kuma ba mace ta fanshi kanta ba.

‎Malamai sun ambaci aibobi masu tsanani da ke hana cikar rayuwar aure ko jawo ƙyama, cuta, ko wahala.

‎Daga ciki akwai:

‎1. Al-qarn (ƙaho a gaba) – wato wani abu da ke toshe gaban mace ya hana saduwa.

‎2. Wari mai tsanani a gaba da ba ya warkewa

‎3. Cutar da ke hana jima’i

‎4. Cutar da ake jin tsoron yaɗuwa

‎5. Hauka ko cutar hankali (idan ba a sani ba tun farko).
‎Idan ba a sanar da miji ba kafin aure, sannan ya gano daga baya, yana da zaɓi.


‎Malamai (Malikiyya, Shafi’iyya, Hanabila) sun ce:
‎•Namiji yana da haƙƙin neman Faskh
‎•Ana dawo masa da sadaƙi saboda:
‎ya biya ne bisa zaton lafiya.


‎An rawaito daga Sayyidina Umar (RA):

‎“Duk mace da aka aurar da ita alhali tana da aibin da aka ɓoye, to mijinta yana da zaɓin warware auren.”

‎Me ya sa za a dawo da Sadaki?

‎Saboda:
‎Ba saki daga mijin ba ne.

‎Khul’i shi ne:
‎rabuwa tsakanin miji da mata inda mace ke neman saki ta hanyar fansar kanta da dukiya (galibi mayar da sadaki).
‎Ana kiransa hul’i saboda mace tana cire kanta daga ikon aure k**ar yadda ake cire tufafi.

‎Sharuɗɗan Khul’i:
‎•Yarda daga bangarorin biyu
‎•Akwai fansar kai (ʿiwaḍ) – yawanci sadaki
‎•Aure yana nan kafin hul’i
‎•Ana yin sa da lafazin Khul’i ko ma’anarsa

‎Mafi yawan malamai sun ce:
‎•Khul’i ba saki na raj’i ba ne
‎•Yana k**a da talāq bā’in

‎Idda bayan Khul’i
‎Malamai sun yi saɓani:
‎-Mafi rinjaye: Idda (haila guda ɗaya)
‎-Wasu: k**ar iddar saki (haila uku)

‎Sadaki a Khul’i
‎-Mace ce ke mayarwa
‎-Bai k**ata miji ya karɓi fiye da abin da ya bayar ba.

ALLAH ya datar damu.

Duk wanda ya jinkirta Sallah har zuwa lokacin darurin ta, ba tare da wani uzuri ba; ya aikata saɓo.Ikhtiyār: lokacin da ...
18/12/2025

Duk wanda ya jinkirta Sallah har zuwa lokacin darurin ta, ba tare da wani uzuri ba; ya aikata saɓo.

Ikhtiyār: lokacin da ya fi dacewa a yi sallah.
Darurī: lokacin da aka bar wa mai uzuri ya yi Sallah kafin lokaci ya ƙare gaba ɗaya.

Mene ne uzurin da Shari'ah ta bayar ga mutum idan ya jinkirta Sallah bai zama mai saɓawa ba?

Uzurai:

" الحيض، والنفاس، والكفر، والصبا ، والجنون، والإغماء، والنوم، والنسيان"

" Haila (ga mata), jinin biƙi ( ga mata), da kafirci, da ƙuruciya (ga yara), da hauka (mutumin da hankalin sa ya gushe), da suma ( har sai idan mutum ya watstsake ya dawo hayyacin sa), da bacci, da kuma mantuwa."

Waɗannan su ne abubuwan da idan sun faru ga mutum har ya jinkirta Sallah to ba shi da laifi, saɓanin haka kuma ya saɓa.

ALLAH ya datar damu.

Shin wanda ya bayyana aya ɗaya ko biyu a inda ake asirtawa, mene ne hukuncin sa (Qabli ko Ba'dhi)?(Jumhūr) ɗin malamai:S...
16/12/2025

Shin wanda ya bayyana aya ɗaya ko biyu a inda ake asirtawa, mene ne hukuncin sa (Qabli ko Ba'dhi)?

(Jumhūr) ɗin malamai:

Sallarsa ingantacciya ce, amma ya bar abin da ya fi dacewa (khilāful-awlā) ko kuma makruhi ne idan ya yi hakan da gangan, ba sai yayi Qabli ko Ba'dhi ba.

قال النووي:
“لو جهر في موضع الإسرار أو أسرّ في موضع الجهر صحت صلاته، لكنه خالف السنة.”

Imām Nawawī ya ce: Da mutum zai bayyana karatu a wuraren da ake asirtawa, ko ya yi sirranta a inda ake bayyanawa, sallarsa ta inganta, sai dai ya saɓa wa Sunnah.

•Mazhabar Hanafiyya

Hukunci:
Idan ya karanta aya ɗaya ko biyu kawai a bayyane a sallar da ake asirtawa, babu komai, sallarsa tana nan.

Maganar Ibn ‘Ābidīn (رحمه الله)

“ولو جهر بآية أو آيتين في الظهر أو العصر لا تفسد صلاته.”

"Ko da mutum ya karanta aya ɗaya ko biyu a bayyane a Azahar ko La’asar, sallarsa ba ta ɓaci ba."

ALLAH ya datar damu, Shehi muna godiya da ziyarar ku.

13/12/2025

"جددوا ايمانكم اكثروا من قول لا اله الا الله"

Annabi Alaihissalam yana cewa:"Ku riƙa sabunta imanin ku da yawaita faɗar Lā ilāHa illalLaHu."

10/12/2025

ALLAH ya bamu zaman lafiya mai ɗorewa, albarkar Annabi ( Sallallahu Alaihi Wa Sallam).

ALLAHU Akbar.ALLAH ya gafarta ma Shehi, albarkar Sayyiduna RasululLaHi ( Sallallahu Alaihi Wa Sallam).
27/11/2025

ALLAHU Akbar.
ALLAH ya gafarta ma Shehi, albarkar Sayyiduna RasululLaHi ( Sallallahu Alaihi Wa Sallam).

Address

Bakori Road
Funtua
831220

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Khalifa Aliyu Alti posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share