12/07/2023
KUN LURA DA WANNAN BATU DA KYAU KUWA...?
Idan dayan su ya tashi neman Suna da Shuhura tsakanin al'umma a wasu 'Yan Shekaru da s**a gabata, to ya kan dirar da barikancinsa kan daya daga cikin jagororinmu kamar Maulanmu Sheikh Ibrahim Inyass (R.T.A) ko babban Almajirinsa Sheikh Dahiru Usman Bauchi (R.T.A) ta hanyar shirya kage, sharri da karya.
Amma cikin shekarun nan, akalar tunanin dukkanin masu neman suna da shuhura cikin Wahabiyya da wancenansu, ya karkato kachokam kan Maulana Prof. Ibrahim Maqari (H), kullum cikin bibiyar dukkanin motsinsa suke dan su samu abin kalaci a kiwonsu na neman aibobinsa...?
Hakan ya kasance ne saboda dalilai guda 2.
1- Irin Uslubin da Maulanmu Sheikh Ibrahim Inyass (R.T.A) yabi wajen isar da da'awowinsa, har milyoyi s**a amsa kiransa zuwa ga Addinin ALLAH, kwatankwacinsa Maulana Prof. yake Jaddadawa, sai ya zamo kullum yana samun karbuwa a zukatan dubban al'umma, wannan abin yana hassala su. Domin Uslubine na jaddada sunnonin MANZON ALLAH (S.A.W) a aikace ba a da'awa ba.
2- Babban abinda Wahabiyanci ta ginu akai shi ne, wargaza hadin kan Musulunci, ta hanyar zagin duk Musulmin da bai kungiyarsu da sunaye munana, kamar Kaf*rai, Mushrikai, Yan Bidi'ah da sauransu, sai ya zamo shi kuma Maulana Prof. yana kira zuwa ga hanyar hadin kai, fahimtar juna da kuma barin aibata juna, wanda su kuma hakan idan ya kau, to zasu rasa jarin da suke habbaka kasuwancinsu na cinikayyar dulmiyarwa da suke.
A hakika duk abinda suke yi, na nuni ne izuwa ga tsada, daraja da kuma daukakar da ALLAH yayiwa Maulana Prof. akansu da dukkan Malamansu, dalilin kyautata koyinsa da MANZON ALLAH (S.A.W) da kuma bayin ALLAH managarta, kuma haka zasu yi iya yinsu, ba tare da sun cimma sa ba da izinin ALLAH.
MUNA ROKON ALLAH YA BASHI KARIYA DA KARIYARSA, YA TSARE SHI DA KULAWARSA.
ALHAMDULILLAH