23/01/2026
Day 2 Program Bible Study Section 1 & 2
**Binciken Littafi Mai Tsarki Na Daya (1)**
Kan Magana: Mu nemi Allah ta wurin mika hadaya, Zaka, da godiya. (AMOS 4:5)
GABATARWA
Da farkon fari Alherin Ubangijin mu, Yesu Christi wanda yake Shugaban bangaskigar mu ya kasance tare da mu kulayomi (Amin).
A zamanin mu, neman Allah yana da matukar muhimmanci, kuma daya daga cikin hanyoyin da muke iya neman shi ta bayar da hadayu, zaka, da godiya. A cikin Amos 4:5, an nuna mana cewa hadayun da muke kawo wa Allah suna da mahimmanci, domin itace hanyar bayyana dukkan abubuwa masu alheri da yayi mana, kuma ita ce hanyar da zai sa mu kusanci Allah da gina kyakkyawar alaka da shi, kamar yadda ya umurci mu cikin (Malakai 3:10) mu kai dukkan zaka a ma’ajiyarsa, haka Ubangiji yayi magana wa kankan mu Ibrahim ya umurci shi ya bada ɗansa domin hadaya (Farawa 22:1-2).
Rashi bin umurnin Ubangijinmu yana sa ya la’anci al’uman mu dukka kamar yadda a cikin (Malakai 3:9). Saboda haka yin godiya ga Ubangiji yana muhimanci sosai, shiyasa sarki Dawuda ya daukaka Ubangiji, cikin (Zabura 111:1:2)
Yayinda zamu shiga cikin tattaunawar mu, bari Ruhun Ubangiji ya bishe mu (Amin).
TATTAUNAWA
1. Me ake nufi da Zuwa Wurin Allah da hadaya, Zaka, da ?
2. A tattauna menene. (i) Hadaya (ii) Zaka (iii) Godiya
3. A tattauna Shin Zaka ne yafi godiya, ko kuma godiya ne yafi Zaka.
4. Wani Lokacine yakamata a yi Zaka?Godiya
5. Wani lokaci ne yakamata ayı godiya?
6. Tattauna manene muhimanci bada hadaya, zaka da godiya.
KAMALAWA
A karshe bare alherin Allahnmu da na kaunar Yesu Kiristi wanda tafi gaban fahimtar mu su kasance tare da mu har abada (Amin).
**Binciken Littafi Mai Tsarki Na Biyu 2**
Kan Magana: Mu nemi Allah ta wurin sake kunna wutar bishara (Ayukan Manzansi-1:8)
GABATARWA
Nemi Allah ta wurin sake kunna wutar bishara, yana na nufin falkas da masu bi daga sanyi cikin ruhu, ko kuma yin shiru da aikin Allah, su kuma gane cewa ba sa kan madaidaicin hanya sai su koma cikin hankalin su, misali na battacen ɗa (Luka 15:17:24).
kunna wutar bishara ba ta karfin mu ba, amma sai ta wurin mun koma gare shi, muka nemi Ubangiji ta wurin addu’a domin taimakon Ruhun sa, ta haka zamu sami karfi daga gare shi, sa’a nan mu iya gudanar da ayyukan da s**a dace.
Ekilisiyarmu ta yau, sun kasa cika umurnin da Yesu ya bamu bisa (matta 28:18-20). domin ribato rayukan mutane zuwa mulkinsa, saboda haka bari kowane mai bishara ya koma kan bagadin addu'a, da kyakkyawar dagantaka mai karfi da Allah, mu iya sake kunna wutar bishara, domin shine asirin samun gabagadin Manzo Bulus cikin aikinsa na bishara.
TATTAUNAWA
1. Mu tattauna manene aki nufi da sake Kunna Wutar bishara.
2. Ta yaya mai bi zai iya Sake kunna wutar bishara a rayuwansa? (Luka 15:17)
3. Ko addu'a tana da muhimman ci a rayuwan mai bishara? (Idan amsan "I" ayi bayani) (Idan amsa "a’a" ayi bayani)
4. Menene gabadin manzo Bulus Cikin aikinsa na bishara.
5. Me zamu yi domin karfafa Ekkilisiyar mu a yau domin cika umurnin (Matta 28:18-20)?
KAMALAWA
Bare alherin da Allah yayı mana ya taimake e mu domin mu sake kunna wutar bishara (Amin)