Majlisu Dullabil Ilmi Kebbi State

Majlisu Dullabil Ilmi Kebbi State This is an interactive group implemented to remind ourselves and others, discuss and share various i

An karbo daga nana Aisha yaardar Allah ta tabbata a gare ta Tace: Manzon Allah tsira da Amincin Allah SU TABBATA a gare ...
19/03/2025

An karbo daga nana Aisha yaardar Allah ta tabbata a gare ta Tace: Manzon Allah tsira da Amincin Allah SU TABBATA a gare shi ya KASANCE.
*Idan Goma na qarshe S**A shigo Yana Raya dare, Sannan Yana tada iyalin SA, Yana Qara dwagewa da yin IBADA, Yana Kuma Daure gyafto (Abun nufi Yana nisantar Iyali)*
Bukhari da Muslim S**a FITAR da hadisin.

Fa'idoji
1. Falalar Goman Qarshe na RAMADWANA
2. Kwadaitarwa domin Raya darurrakin Goma na karshe da ibada musamman Tsayuwar dare.
3. Nisantar Iyali Domin IBADA ta Qara karfi.
4. Umartar Iyali Da SU Raya dareN.

Wannan Hadisi Yana zo muku daga Majalisu Ulumudden Wattarbiyyatil Islamiyya Aleiro Estate Birnin Kebbi

https://chat.whatsapp.com/GiL40FHyJmAFvnVgZSbTsI

Fassara Daga
Mal. Surajo Ahmad Daura

Daga Abdullahi Umar R.A yace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata garesa yace: " Kada dayanku ya tayar da wan...
22/08/2023

Daga Abdullahi Umar R.A yace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata garesa yace: " Kada dayanku ya tayar da wani mutum daga mazauninsa sannan shi ya zauna a mazaunin, sedai ku buda ku yalwata ku gyara (don wani ya samu wurin zama), kuma Abdullahi dan Umar idan wani mutum ya miqemasa tsaye daga mazauninsa shiko baya zaunawa gurbin". Buhari da Muslimune s**a ruwaitosa

Fa'idodi
1. Allahu akbar! cikin kyauwon addinin musulunci komai ya kowar damu.

2. Sanar damu ladubban zama a wurin zama.

3. Kada wani ya tayar da wani shiko ya zauna wurin kila don ganin yafi shi.

4. Kai koda wani ya tashi ya baka wurinsa anfison kabar da wurinsa yafi lada.

5. Abinda yake mafi kyau agyara zama abuda idan ba takura wani ya zauna.

6. Allahu akbar! Abdullahi dan Umar saboda tsabar karantarwa ko wani ya tashi da kansa ya bashi wuri baya zaunawa.

KAICONMU! wallahi kwanaki anzo wa'azi da wani ya tada wani daga wurin zamansa, ba niba duk wanda yake wurin ranshi ya 6ace, saboda kwata-kwata ba tunani da kimantawa, na farko wanda aka tada baqone kuma babba tare da wanda ya gabatar da wa'azin yazo, na biyu: wanda ya tadashi dan garine, na uku: tayarwar da yayi masa ba qimantawa acikinta😢, na hudu ya 6ata ran kashi biyu bisa ukun na cikin masallacin!, yanada kyau muyi aiki da hadisi da karantarwa Annabi MUHAMMAD SALLALLAHU ALAYHI WASALLAM, ba'a samun girma ko daukaka da qarfi ko kaga kanayi kawar ka samu girman wallahi kallon wawa mutane keyima, daga qarshe kuma Allah yayi fushi da kai, ko ta k**a dalili na a tada wani toh aqimanta dan adam, don wallahi daga qarshe da aka fadi darajar wanda aka tada se kuma aka koma jin kunya.

Wannan Hadisi Yana zo mu ku daga Majlisu dullabi Ilmi, Kebbi State.

Fassara:
Mal. Nazeer Usman Adam Jega.

Daga Abi Darda'i R.A, lailai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agaresa yace: " Babu wani abu mai nauyi akan...
18/08/2023

Daga Abi Darda'i R.A, lailai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agaresa yace: " Babu wani abu mai nauyi akan ma'aunin bawa mumini ranar lahira, fiye da kyawawan dabi'u, kuma lailai Allah yana qyamar mai lafasha (fasiki) mai batsa". Tirmizy ne ya ruwaitosa

Fa'ida
1. Kwadaitar damu akan kyawawan dabiu

2. Kyawawan dabiu abin koyi ne ga mutane shiyasa seda Allah yayi rantsuwa ya bamu tabbacin Annabi Muhammad SAW yana kan kyawawan dabi'u

3. Kyawawan dabi'u su nauyaya ma'aunin mumini ranar lahira

4. Allah baya son fasikai masu batsa

5. Ana alfahari da zama na qwarai ba zama na banza ba.

Ubangiji Ya Sanya mu cikin masu kyawawan Dabi'u.
Ameen Summa Ameen

Wanna Hadisi Yana zo muku daga Majlisu Dullabil Ilmi Kebbi State.

Fassara::Mal. Nazeer Usman Adam Jegaa

Daga Abi Huraira R.A daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agaresa yace: " Allah ya tumurmusa hancin, sann...
16/08/2023

Daga Abi Huraira R.A daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agaresa yace: " Allah ya tumurmusa hancin, sannan tumurmusa hancin, kuma ya tumurmusa hancin, wanda ya riski tsufan iyayensa, dayansu ko dukkansu, amma bai shiga aljannahba". Muslimune ya ruwaitosa

Fa'ida
1. Sanar damu darajja da matsayin iyayenmu Allah ya qara musu albarka

2. Yin mummunar addu'a ga duk wanda ya rayu dasu kuma bai samu aljannahba kaico!

3. Anfison akula dasu loqacin tsufansu sosai

4. Da yawan mutane suna gajiya da iyayensu loqacin tsufa loqacinda sunada buqata damu

5. Asarace mafi girma ka rayu da iyayenka baka kyautata musuba

6. Karantar damu kyautata musu da kula dasu har mu rabu dasu lafia.

Ubangiji Ya Sanya mu cikin kyautatawa da Magabanta mu.

Wanna Hadisi Yana zo muku daga Majlisu Dullabil Ilmi Kebbi State.

Fassara:: Nazeer Usman Adam Jega

Daga Ummi Kulsum yar Uqba dan Abi Mu'ait R.A tace: naji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agaresa yana cewa...
15/08/2023

Daga Ummi Kulsum yar Uqba dan Abi Mu'ait R.A tace: naji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agaresa yana cewa: " Ba maqaryacineba, wanda ya gyara tsakanin mutane ya kulla alkhairi, ko ya fadi alkhairi". Bukhari da Muslimune s**a ruwaitosa

Fa'ida
1. Falalar shirya mutunen da basa zama shiri

2. Matsayin sulhu tsakanin mutane

3. Halaccin yin qarya wurin shirya mutane

4. Duk munin qarya amma don yin sulhu Allah ya halatta ta

5. Kwadaitarwa akan son shirya tsakanin mutane ba qara hargitsasuba

6. Muni na rabuwar mutane, inata ga wanda shi ya rabasu.

Ubangiji Ya Sanya mu cikin masu kulla Alkhairi a Koda Yaushe.

Wanna Hadisi Yana zo muku daga Majlisu Dullabil Ilmi Kebbi State.

Fassara:: Mal. Nazeer Usman Adam Jega

Daga Abi Huraira R.A yace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata garesa yace: " Idan miji ya kira matarsa zuwa ...
12/08/2023

Daga Abi Huraira R.A yace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata garesa yace: " Idan miji ya kira matarsa zuwa ga shimfidarsa, taqi zuwa se ya kwana yana hushi da ita, mala'iku zasuyi ta tsinemata har se ta wayi gari". Buhari da Muslimune s**a ruwaitosa

1. Sanin haqqin miji akan matarsa.

2. Idan miji ya kira matarsa don ta biya masa buqatarsa, ta da namiji taqi biyamasa toh har gari ya waye mala'iku na yimata tsinuwa.

3. Wannan hadisine sananne kusan ko wane matashin duniya ya haddaceshi.

4. Yana da kyau yan uwa mata ku kula, duk laifin da miji yayi miki kar ki yarda kice wai zaki rama ta wannan hanyar, akwai tsinuwar Allah, sannan zaki iya jefashi zuwa ga fasadin da daga baya zakiyi da kesani.

5. Amma fa "wala hunna mislullazi alayhinna bil ma'aruf..." Suma fa sunada haqqoqinda idan baka basuba, Allah zai tsinemaka hasalima zaka tashi gobe qiyama da shanyayyen jiki.

Wanna Hadisi Yana zo muku daga Majlisu Dullabil Ilmi Kebbi State.

Fassara:: Mal. Nazeer Usman Adam Jega

Daga Abi Huraira R.A Lailai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata garesa yace: " Na rantse da wanda rayuwata ta...
11/08/2023

Daga Abi Huraira R.A Lailai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata garesa yace: " Na rantse da wanda rayuwata take hannunsa, haqiqa nayi niyar inyi umurni ayo itace, sannan inyi umurni da kiran salla, se insa wani mutum ya limanci mutane, sannan in maye wasu mazaje in qone gidajensu". Buhari da Muslimune s**a ruwaitosa

Fa'ida
1. Ba'a rantsuwa da kowa se ubangiji duba da yadda Annabi MUHAMMAD SALLALLAHU ALAYHI WASALLAM ya rantse da Allah.

2. Muhimmancin sallar jam'i da wajabcinta.

3. Azmar da Annabi yayi akan qona gidajen wadanda basu zuwa sallar jam'i, inata ga wanda baya salla kuma wai yana kiran kansa musulmi.

4. Umurni da akira salla sannan daga baya ayi iqama, wannan na nuna maka qarfin maganganun malumma akan muhimmancin kiran salla koda ko cikin daji kake.

5. Salla abace mai matuqar girma a musulunci, hasalima ginshiqice mai qarfin gaske wanda idan babu shi komai na iya faduwa.

Wanna Hadisi Yana zo muku daga Majlisu Dullabil Ilmi Kebbi State.

Fassara:: Mal. Nazeer Usman Adam Jega

Daga Anas dan Malik R.A daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata garesa yace: " Dabi'u uku duk wanda ya kasan...
09/08/2023

Daga Anas dan Malik R.A daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata garesa yace: " Dabi'u uku duk wanda ya kasance cikinsu, ya samu zaqin imani dasu: ya kasance Allah da Manzonsa sunfi soyuwa garesa daga duk abinda basuba, kuma yaso mutum ba dan komaiba se don Allah, kuma yana qyamar komawa cikin kafirci bayan Allah ya tsamar dashi daga gareshi (kafirci), k**ar yadda yake qyamar awurgasa acikin wuta". Buhari da Muslimune s**a ruwaitosa

Fa'ida
1. Sanar damu ashe imani har zaqi gareshi tamkar ya'yan itace ko zuma, amma se wanda ya dace ya samun zaqin.

2. Wadannan halayen uku duk wanda ya dace dasu tabbas zai samu zaqin imanin.

3. Dole se kafison Allah da Manzonsa sannama zaka samu imanin, kuma ba abakiba a aikace tare da aza kowane bagirensa Allah matsayinsa na Ubangiji, Annabi kuma matsayin na mafi girman halitta da daraja cikin halittun Allah.

4. Na biyun dabi'un duk wanda zakaso ka soshi don Allah, tirqashi akwai buqatar natsuwa, yanzu munada abokai da masoya barkatai, amma da zamu natsu muyi tunani muga wa mukeso don Allah, kawai zamu tabbata akwai aiki ba kasafai Allah ya bada wannan gara6asaba!.

5. Tsoron komawa cikin kafirci kawar yadda ko fiye da yadda kake tsoron wuta ta qonaka koda ko ta duniyace, Alhamdulillah mu anfemu cikin musulunci toh kaji tsoron komawa kafiri da hakan.

Wanna Hadisi Yana zo muku daga Majlisu Dullabil Ilmi Kebbi State.

Fassara:: Mal. Nazeer Usman Adam Jega.

Daga Abi Huraira R.A, Lailai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata garesa yace: " Tafiya wani yankine na azaba,...
25/05/2023

Daga Abi Huraira R.A, Lailai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata garesa yace: " Tafiya wani yankine na azaba, dayanku na hana kansa abincinsa da abin shansa da kuma kwanansa, idan dayanku ya qare biyan buqatarsa na tafiyar da yayi, to ya gaggauta komawa wurin iyalansa". Bukhari da Muslimune s**a ruwaitoshi

Fa'ida

1. Tafiya azabace, musamman idan ta hadu da jarabobi, shiyasa har a Alqur'ani Allah yasa matafiyi cikin wadanda za'a taimak**a dole, munji tafiyar Annabi Musa da Khidir.

2. Komai gatanka, acikin tafiya wata rana zaka iya rasa abinci ko abinsha, shi kwana (bacci) wannan dolene ayi haqurinsa.

3. Annabi ya siffantamuna yadda mutum zai hanu da ci da sha da kuma bacci yadda ya saba, koda ko wani babban mutum ne, har qissa akwai ta wani bawan mai mulki da ya rasa ransa ahalin tafiya.

4. Gaggawar komawa wurin iyali bayan qare buqatarka na tafiya.

5. Hani ne mai girma da nuni akan cewa ba'ason ana nisa da iyali, wannan yasa da yawa wasu mata ke aukawa cikin zina😭, saboda wani yayi tafiya tsawon watanni bai dawoba, alhali tanada buqata ta daa namiji da kai bawan Allah, haba bawan Allah kai kanka zaka auk**a fitina, don ba qarfe kakeba kuma zaka gansu kala kala, toh kayi qoqari idan ka qare abinda ya kaika tafiyar, kayi gaggawar komawa cikin iyalanka domin biyawa juna buqatu na yau da kullun.

6. Suma wadanda basuda aure har su hadisin ya shafa, sedai ba k**ar masu iyaliba don kar wani gauro yace; ay bada suba hadisin ammne har kai bawan Allah, Allah kayima mafita.

Wanna Hadisi Yana Zo Muku daga Majlisu Dullabil Ilmi Kebbi State.

Fassara:
Mal. Nazeer Usman Adam Jega

Daga Abi Sa'id Alkhudriy R.A yace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya zauna akan mimbari, muk...
24/05/2023

Daga Abi Sa'id Alkhudriy R.A yace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya zauna akan mimbari, muka zauna gefensa, se yace: " Lailai yana cikin abinda nake jimuku tsoro bayana, abinda za'a budemuku na daga furannin duniya da adonta". Bukhari da Muslimune s**a ruwaitoshi

Fa'ida
1. Qaunar da ke tsakanin Annabi da al'ummarsa.

2. Tausayinmu yanayin da zamu shiga bayan wafatinsa.

3. Abinda Annabi Muhammad S.A.W yake jimuna tsoro.

4. Annabi baya jumuna tsoron talauci ko wani abu, amma yana jimuna tsoron fucewar imaninmu.

5. Jimuna tsoron malalomuna duniya da adonta, kawar dukiya, qawarta da shawowinta saboda fitinace mafi girma.

6. Duniya ta halakar da wadanda suke gabaninmu.

7. Samun duniya baya nuna arziki, kawar yadda da yawan mutane suke zato, don Allah ya anbaceshi matsayin fitina.

8. Yana cikin mafi girman abinda yake jimuna tsoro abamu duniya da adonta don jarabawace.

Ubangiji Ka Sanya mu Cikin Masu gudun Duniya da Sha'awowin Duniya.

Wanna Hadisi Yana Zo Muku daga Majlisu Dullabil Ilmi Kebbi State.

Fassara:
Mal. Nazeer Usman Adam Jega.

Daga Abi Huraira R.A: Lailai Manzon Allah tsira da amincin Allah yace: " Kada ku maida gidajenku maqabarta, lailai sheda...
23/05/2023

Daga Abi Huraira R.A: Lailai Manzon Allah tsira da amincin Allah yace: " Kada ku maida gidajenku maqabarta, lailai shedan yana gudu daga gidanda ake karanta suratul Baqara cikinsa". Muslimune ya ruwaitosa

Fa'ida

1. Duk gidanda ba'a karatun Alqur'ani, ba'a Nafiloli dashida maqabarta duk dayane.

2. Falalar karanta suratul Baqara.

3. Shedanun aljannu, kai hadda na mutane basa zama gidajenda ake karanta Alqur'ani.

4. Yana cikin raya gida yawaita ibada acikinsa.

5. Kashe gidane murus rashin yin ibada cikinsa.

Ubangiji Ya Sanya mu Cikin Masu Karatun Alkur'ani Dare da Rana.

Wanna Hadisi Yana Zo Muku daga Majlisu Dullabi Ilmi dake Jahar Kebbi Nigeria.

Fassara:
Mal. Nazeer Usman Adam Jega.

Address

Birnin-Kebbi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Majlisu Dullabil Ilmi Kebbi State posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to Majlisu Dullabil Ilmi Kebbi State:

Share