21/05/2026
Ɗan uwa ka kasance mai gaskata al'amarin Allah a Duk Inda kake a kowane zamani kake ciki.
Daga cikin karatun da Mawlanmu Khalifa Ibrahim Sheikh Aliyu Muhammad Bunza QS yake yi na litattafin da ke ɗauke da Majlisosan Shehu Aliyu QS yayi bayani akan wannan sifar kamar yadda Shehu Aliyu Bunza QS yayi ta ba'yani akan ta, wato Sifar gaskatawa.
Khalifa yace Shehu na yawan cewa baka taɓa jin Inda Allah yace ويل للمصدقين ba, ma'ana "Bone ya tabbata ga masu gaskatawa" sai dai yace ويل للمكذبين , wato " Bone ya tabbata ga masu ƙaryatawa". Shehu yana ƙarfafa wannan magana da hadisin Manzon Allah SAW inda yake cewa halaye guda ba abin da ya kai su Alkhairi, kyautata zato ga Allah da kuma kyautata zato ga bayin Allah, sannan halaye Biyu ba abin da ya Kai su Sharri, munana zato ga Allah da munana zato ga bayin Allah. A nan kyautata zato ga bayin Allah ya na ɗaukar Sifar gaskata su Idan su ka zo da wani Al'amari daga Allah, munana zato garesu kuma yana ɗaukar Sifar ƙaryata su ba tare da hujja ta bayyana gareka ba.
Khalifa yace, amfanin mai gaskatawa shine bazai dawwama cikin wannan halin nashi ba har sai ya gaskata abinda gaskiya ne daga Allah kuma wannan abin ya zama silar tsira gareshi, haka ma cutar da ke tare da yawan ƙaryatawa shine mutum bazai gushe yana ƙaryatawa har sai ya ƙaryata abun da zai zama Silar ta'ɓewa gareshi domin abinnan da ya ƙaryata al'amari ne Kuma gaskiya ce daga Allah.
Ƙaryatawa ne ya halakar da yahudawa da nasara, kuma shi ya taɓar da Ma'su ƙaryata waliyyai, ya sa yan ɗariƙar mu ta tijjaniya s**a tabka hasarar Rashin Yarda da failar Shehu Ibrahim, Hakanan ne da Yawan Yan uwan mu yan faila suke cikin hasarar Rashin Yarda da SIRRIN FAILA na halarar Qudsiyya.
Allah ya bamu Sirri da ruhi da zuciyar gaskata duk wani al'amari da ya fito daga gareshi. Ya samu a cikin SIDDIQAN BAYINSA.
Allah (taba'raka wa ta'a'la) yana cewa :
قَالَ ٱللَّهُ هَٰذَا يَوْمُ يَنفَعُ ٱلصَّٰدِقِينَ صِدْقُهُمْ ۚ لَهُمْ جَنَّٰتٌ تَجْرِى مِن تَحْتِهَا ٱلْأَنْهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدًا ۚ رَّضِىَ ٱللَّهُ عَنْهُمْ وَرَضُوا۟ عَنْهُ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْفَوْزُ ٱلْعَظِيمُ
Allah Ya ce: "Wannan ce rãnar da mãsu gaskiya, gaskiyarsu take amfãninsu. Sunã da gidãjen Aljanna, ƙõramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, sunã madawwama a cikinsu har abada. Allah Yã yarda da su, kuma sun yarda da Shi. wannan ne babban rabo mai girma."
Allah ka sa mu kasance a cikin su ta kowace Fuska a bisa kowace ma'ana.