Naziru Musa

Naziru Musa Masoyin Annabi sallallahu alaihi wassallam

Sufanci itace mafita  a wannan zamanin  muddin  mutum ya riƙeta zai samu tsira  saboda Istigfari da hailala da salati an...
23/05/2026

Sufanci itace mafita a wannan zamanin muddin mutum ya riƙeta zai samu tsira saboda Istigfari da hailala da salati annabi sallallahu alaihi wassallam..

Domin yadda zamanin mu ta lalace ayyukan mu s**a munana idan bada tuba da neman kusanci da allah ba akwai babban matsala

Allah dai yasa muyi kyakyawan ƙarshe ameeen.

Gaskiya ce a harshen su, ya kamata ce a aikin su, nagarta ce a dabi'arsu, soyayya domin Allah ne muradinsu, Allah ya tsa...
23/05/2026

Gaskiya ce a harshen su, ya kamata ce a aikin su, nagarta ce a dabi'arsu, soyayya domin Allah ne muradinsu, Allah ya tsare su irin tsarewar da ke yiwa waliyansa, ya jiɓinci lamuransu irin jibintar da yake yiwa bayin da s**a koma zuwa gare shi, Allah ya daukaka ambaton su irin daukakawar da yake yiwa bayin da s**a bi shi....

Allah ka mana shaida da muna son su saboda kai, kasa wannan soyayyar ta mana anfani, ka sa mu zama na kusa da su a duniya da lahira...

Albarkacin Annabi da Alkur'ani.

Abul Abbas.

Kar ka zamto Dalilin fa'dawar wani cikin masifa,  don zai kasance tsawon rayuwarsa, da zaran  ya ji an ambaci labarinka,...
23/05/2026

Kar ka zamto Dalilin fa'dawar wani cikin masifa, don zai kasance tsawon rayuwarsa, da zaran ya ji an ambaci labarinka, sai ya fara maimaita: HASBIYALLAHU WA NI'MAL WAKEEL... Hakan zai zamto tamkar ya na aika wasu Boma-Bomai ne gareka.

Khairukum Man ta'allamal Qur'ana wa'allamahu!  Fiyayye a cikinku wanda yafiku Inji manzon Allah s.a.w. shine wanda yafik...
23/05/2026

Khairukum Man ta'allamal Qur'ana wa'allamahu!

Fiyayye a cikinku wanda yafiku Inji manzon Allah s.a.w. shine wanda yafiku Sanin Qur'ani. Mahaddata Qur'ani sune jagorori a cikin musulunci Randa manzon Allah s.a.w. zaiyi wafati cikin wasiyyoyinsa na karshe ga Abunda yake cewa : Ku rike malamai mahaddata Alqur'ani su suke dauke da Abunda Allah ya Aikoni dashi Ku girmamasu Ku sosu duk wanda ya girmamasu ya girmamani wanda ya sosu yasoni,

ya ƙara da cewa Ku girmama malaman Ilimi domin su suke bayanin Abunda Allah ya Aikoni dashi Inji manzon Allah s.a w. Jama'a maulana Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya samu daraja guda biyu na farko shi mahaddaci ne Original, na biyu malamin Ilimi ne cikakke.

Na rasa meke mun daɗi naje na kwanta tun da wuri amma na rufe ido na gagara bacci na tashi na zauna na gaji da zama na j...
23/05/2026

Na rasa meke mun daɗi naje na kwanta tun da wuri amma na rufe ido na gagara bacci na tashi na zauna na gaji da zama na jin ginu na gaji da jinginuwa na kwanta sai raina yana saka mun anya wannan kwanciyar in nayi dan tashine kuwa saboda yanayin yadda mutuwa ta kasance abu mai sauƙi yanzu daka rabu da mutum sai kaji ya mutu sai na fara saƙawa araina to ace yanzu na mutu me zanje nace wa ALLAH kokuma menene aikin da nayi kokuma mutane nawa na tai maka kokuma marayu nawa nake ciyarwa kokuma masu wa dawa nake alhairi shin inna mutu a wannan kwanciyar tawa suwaye zasu mun shedar kirki kokuma sheda ta kwarai ban tai maki yan unguwa ba ban tai maki yan gida ba ban taba ciyar da wani ba ban taba biya ma wani kudin makaranta ba,

shin bayan namutu abokaina zasuyi kukane kawai na wasu ɗan lokuta da za'a tambayi wani abokin dan me yake kuka sai yace dan ya rasa aboki da za a tambayi wani sai yace dan ya rasa wadda suke taɗi da za a tambayi wani sai yace ya rasa wadda suke zuwa makaranta tare da za'a tambayi budurwarka ko matarka sai tace ta rasa masoyi wadda yake ɗebe mata kewa

inalillah wa innailaihi raji'un ƴan uwa wannan waɗanda kuke tare kullun kowa yana kukane ma damuwarsa babu wadda yake kuka wa damuwarka ko yakema addua duk tunanin kowa damuwa akan abunda ta shafeshi bai taɓa tuna nin cewa shin kai daka mutu me zaka gaya wa ALLAH kokuma yaya mu'amalar ka da mutane kokuma yaya kyautar ka kokuma yaya sakin fiskar ka shin anya aikina zai kaini aljanna kuwa kokuwa wuta zai kaini, wannan bai dameshiba kuma wannan kukar da yake shima na kwana ɗaya ne zuwa biyu zuwa uku mai kokari kenan yayi sati yana jimamin rashinka daga nan ka tafi kenan ba labarinka kuɗin daka tara kabarsu gidan daka saya ka barshi motar daka saya ka barshi aikin da kake ka bari matar daka aura ka barta karatun boko kokuma result da duk wasu kyautar daka tara a duniya ka rabu dasu kenan ,

abun da daka tafi dashi daga kai sai halinka achanne za' tambayeka mawa ka taimaka wa ..

An yi rubuce-rubuce da dama akan tarihin Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama amma har yanzu kamar ba'a yi komai...
22/05/2026

An yi rubuce-rubuce da dama akan tarihin Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama amma har yanzu kamar ba'a yi komai ba, saboda idan har zaka yi magana akan Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama dole ya shafi Allah ubngijinsa, shi kuma Allah bai da farko bai da karshe subhanahu wata'ala.....

Sheikh Ahmad tijjani..

ALQUR'ANI, LITTAFI MAI BAN MAMAKI📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘“Alqur'ani zancen Allah ne, Shi ne Ya fare shi ba tare da an san yadda Y...
22/05/2026

ALQUR'ANI, LITTAFI MAI BAN MAMAKI

📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘

“Alqur'ani zancen Allah ne, Shi ne Ya fare shi ba tare da an san yadda Ya furta shi ba, kuma Ya saukar dashi ga AnnabinSa ta hanyar wahayi, kuma lalle ne tabbas Muminai sun gaskata shi, kuma sun sakankance da cewa haƙiƙa Zance ne na Allah (S.W.T.), ba halittaccen abu ba ne kamar zancen halittunsa, duk kuma wanda ya ji shi sa,an nan ya riya cewa zancen mutum ne, to, lalle ne ya kafirta....”

Wanda Ya saukar da shi (S.W.T.) Ya sifanta shi, inda Yake cewa:

وإنه لكتاب عزير * لا يأتيه الباطل من بين يديه ولا من خلفه تنزيل من حكيم حميد

"Kuma lalle shi, hakika, Littãfi ne mabuwãyi. ɓarna bã zã ta je masa ba daga gaba gare shi, kuma bã zã ta zo ba daga bãya gare shi. Saukarwa ce daga Mai hikima, Godadde. (Suratul Fussilat 41-42).

Kamar yadda Allah Mai bayyanannar Kudura Ya sifanta shi, Yana cewa:

كتاب أحكمت ءاياته ثم فصلت من لدن حكيم خبير

"Littãfi ne an kyautata ãyoyinsa, sa'an nan an bayyana su daki-daki, daga wurin Mai hikima, Mai Kididdigewa." (Suratu Hud: 1).

Lalle ne: Haƙiƙa ayoyin Alqur'ani mai tsarki suna cikin tabbataccen tsari matuka, da kuma cikakken bayani wanda Mai hikima Ya kyautata tsarinsu, sa'an nan Gwani Ya rarrabe su daki-daki, kuma haka wannan Littafi zai ci gaba da kasancewa gagara-koyo ta ɓangaren zurfin balaga, hukunce-hukunce, ilimi, tarihi da wasunsu, har zuwa lokacin da Allah zai gaji duniya da abinda ke cikinta, babu wani abu na canji da zai shigo masa komin kankantarsa, hakan na gaskata zancen Allah (S.W.T.) Cewa:

إنا نحن نزلنا الذكر وإنا له لحافظون

"Lalle Mu ne, Muka saukar da Ambato (Alqur'ãni), kuma lalle Mu, hakika, Mãsu kiyãyewa ne gare shi" (Suratul Hijr: 9)

ALLAH YA SANYA MU CIKIN MASU RIQO DASHI DA AIKI DA KARANTARWARSA, AMEEEN.

An Sanyawa Wani Layi Sunan Shehu Ibrahim A Amuruka A nan ɗaya ne daga cikin jikokin maulanmu Shehu Ibrahim Inyass ke tsa...
22/05/2026

An Sanyawa Wani Layi Sunan Shehu Ibrahim A Amuruka

A nan ɗaya ne daga cikin jikokin maulanmu Shehu Ibrahim Inyass ke tsaye akan layi mai suna Barham street a Detroit Michigan a ƙasar Amuruka...

Mai girma dayane kuma mai girman daraja Dan amina zababben Allah fiyayyeDuk wadda yayi riko DA annabi yashabulala ta fil...
22/05/2026

Mai girma dayane kuma mai girman daraja Dan amina zababben Allah fiyayye

Duk wadda yayi riko DA annabi yashabulala ta fili da badini daya zabi son manzan Allah

Wadda duk yayi riko DA annabi daka komai ya ture tundaya zabi son manzan allah saw

Ga ranan mahsher babu wane sai manzan Allah s a w

Allah ya jikan fadar begen annabi s a w

Baitin diwanin shehu ibrahim عَلَى هَيْكَلٍ يَفْرِي الْبَرَى وَحَنِينُهُ حَنِينُ عِشَارٍ أَوْ لَكَالْبَرْقِ يَرْعُــدُمَ...
22/05/2026

Baitin diwanin shehu ibrahim

عَلَى هَيْكَلٍ يَفْرِي الْبَرَى وَحَنِينُهُ
حَنِينُ عِشَارٍ أَوْ لَكَالْبَرْقِ يَرْعُــدُ

مَرَرْتُ بِبَدْرٍ بِالْقَلِيــــبِ تَذَكُّـــرًا
لِقَائِــدِنَا الْأَعْلَى الْمُقَفَّى وَأَمْجَدُ

أَيَسْمَحُ سَوَّاقِي فَأَدْنُــــو مُعَاتِبًــا
لِأَهْلِ الْقَلِيبِ الْكَافِـرِيـــنَ أُنَــدِّدُ

وَأَسْأَلُـهُـمْ مَاذَا لَقَوْا حِينَ هَيَّجُوا
الْمُقَفَّى بِجَيْشٍ دَرَّبُوهُ وَجَنَّـدُوا

أَبُو جَهْلٍ الْعَاتِي وَلِيدٌ وَشَيْبَـــةٌ
كَذَا عُتْبَةٌ إِذْ قَلَّدُوهُمْ وَأَوْفَـــدُوا

لِقَاءٌ بِبَدْرٍ قَــــــدْ أُسَـــــرُّ بِذِكْـــرِهِ
فَكُـــــلٌّ قَتِيـــــلٌ أَوْ أَسِيــــرٌ مُقَيَّــدُ

أُعَفِّرُ خَدِّي عِنْدَ مَمْشَـــــى مُحَمَّـــدٍ
وَلِي جَانِبَيْ هَرْشَى طَرِيقٌ مُمَهَّـــدُ

عَلَيْــــكَ صَــــلاَةُ اللّٰهِ ثُــــمَّ سَلاَمُـــهُ
مِنَ الْعَبْدِ فِي رَكْبٍ وَرَوْضَكَ يَقْصُدُ

عَلَيْـــكَ صَــــلاَةُ اللّٰهِ ثُــــمَّ سَلاَمُـــهُ
فَلَمْ أَكُ فِـــي دَرْكِ الْمُنَــــى أَتَـــرَدَّدُ

عَلَيْـــــكَ صَــــلاَةُ اللّٰهِ ثُــمَّ سَلاَمُـــهُ
وَمِنْ وَالِدِي شَيْخِي وَمَا زَالَ يُحْمَدُ

عَلَيْــــهِ مَعَ الْآلِ الْكِرَامِ وَصَحْبِــهِ
تَطِيبُ حَيَاتِى ثُمَّ فِي الْقَبْـــرِ أُسْعَــدُ.

TAMBAYA DA AMSA DAGA MAULANA SHEHUDAHIRU BAUCHI R.A.)1. Menene MA'ARIFA kuma wanene ARIFI?2. Menene Dangantaka da kuma b...
20/05/2026

TAMBAYA DA AMSA DAGA MAULANA SHEHU
DAHIRU BAUCHI R.A.)
1. Menene MA'ARIFA kuma wanene ARIFI?
2. Menene Dangantaka da kuma bambancin dake tsakanin "MA'ARIFA da kuma WUSULI?
•Ma'arifa a harshen Larabci tana nufin sani, amma a wajen sufaye wannan kalma ba a amfani da ita sai dan a bayyana ma'anar sanin Allah, wato sani na haƙiƙa da sufarsa da sunansa da zatinsa.
•Arifi kuwa a wajen SAHIBUL FAIDHATI shine
wanda ya ƙare (fana'i) sau daya a zati, ya ƙare sau biyu ko sau uku a suna, ya ƙare sau daya a sufa, ya tabbatar da samuwa cikin Haƙiƙoƙi guda uku to nasan dai kafin mutum ya gane zaurancen nan sai dolensa yayi azkarut tarbiyya ya samu WUSULI sannan ya samu mai tarƙiyantar da shi har sai ya san ma'anar zati, sufa da kuma suna,

yasan kuma yadda fana'i a cikinsu yake tabbata har ya iya ganin samuwa duka ta koma cikin ukun nan da suke sune
gurbinta na asali:
ﻛﻔﺎﻧﻲ ﻓﻲ ﺳﻴﺮﻱ ﺍﻟﻌﻨﺎﺀ ﻭﻗﺎﺩﻧﻲ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﺬﺍﺕ ﻻ ﻧﺠﺪ
ﺃﺭﻯ ﺃﻭ ﺣﻀﻴﺾ
Amma batun dangantaka da ka tambaya
tsakanin MA'ARIFA da WUSULI to sai ince wusuli tsani ne ko kuma hanya zuwa riskar Ma'arifa, amma ba shine Ma'arifar ba kamar yadda shehu Ibrahim niass rta yake fada:
ﻭﻟﻴﺲ ﻫﺬﺍ ﻫﻮ ﺍﻟﻤﻌﺮﻓﺔ ﻭﺇﻧﻤﺎ ﻫﻮ ﺑﺎﺏ ﻟﻠﻤﻌﺮﻓﺔ ﻭﻻ ﺑﺎﺏ
ﻟﻠﻤﻌﺮﻓﺔ ﺍﻻ ﻫﻮ
cewa yake wusuli da mutum yake samu inyayi
tarbiyya ba shine Ma'arifa ba wannan ƙofa kawai ya iso ta Ma'arifa, ba kuma wata ƙofa ga Ma'arifa in ba ita ba. Dan haka wannan magana ta nuna cewa Ma'arifa birni ce na sanin Allah,
•Wusuli kuma shine qofar shiga wannan birni.
Allah ya tabbatar damu Akan wannan tsanin
Bijahi sallallahu alaihi wassallam
Allah ya Kara jaddada rahma ga maulana sheikh albarka annabi Sallallahu alaihi Wasallam

Address

Bappajo Road Bauchi
Bauchi

Telephone

+2347081662546

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Naziru Musa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share