22/05/2026
ALQUR'ANI, LITTAFI MAI BAN MAMAKI
📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘📘
“Alqur'ani zancen Allah ne, Shi ne Ya fare shi ba tare da an san yadda Ya furta shi ba, kuma Ya saukar dashi ga AnnabinSa ta hanyar wahayi, kuma lalle ne tabbas Muminai sun gaskata shi, kuma sun sakankance da cewa haƙiƙa Zance ne na Allah (S.W.T.), ba halittaccen abu ba ne kamar zancen halittunsa, duk kuma wanda ya ji shi sa,an nan ya riya cewa zancen mutum ne, to, lalle ne ya kafirta....”
Wanda Ya saukar da shi (S.W.T.) Ya sifanta shi, inda Yake cewa:
وإنه لكتاب عزير * لا يأتيه الباطل من بين يديه ولا من خلفه تنزيل من حكيم حميد
"Kuma lalle shi, hakika, Littãfi ne mabuwãyi. ɓarna bã zã ta je masa ba daga gaba gare shi, kuma bã zã ta zo ba daga bãya gare shi. Saukarwa ce daga Mai hikima, Godadde. (Suratul Fussilat 41-42).
Kamar yadda Allah Mai bayyanannar Kudura Ya sifanta shi, Yana cewa:
كتاب أحكمت ءاياته ثم فصلت من لدن حكيم خبير
"Littãfi ne an kyautata ãyoyinsa, sa'an nan an bayyana su daki-daki, daga wurin Mai hikima, Mai Kididdigewa." (Suratu Hud: 1).
Lalle ne: Haƙiƙa ayoyin Alqur'ani mai tsarki suna cikin tabbataccen tsari matuka, da kuma cikakken bayani wanda Mai hikima Ya kyautata tsarinsu, sa'an nan Gwani Ya rarrabe su daki-daki, kuma haka wannan Littafi zai ci gaba da kasancewa gagara-koyo ta ɓangaren zurfin balaga, hukunce-hukunce, ilimi, tarihi da wasunsu, har zuwa lokacin da Allah zai gaji duniya da abinda ke cikinta, babu wani abu na canji da zai shigo masa komin kankantarsa, hakan na gaskata zancen Allah (S.W.T.) Cewa:
إنا نحن نزلنا الذكر وإنا له لحافظون
"Lalle Mu ne, Muka saukar da Ambato (Alqur'ãni), kuma lalle Mu, hakika, Mãsu kiyãyewa ne gare shi" (Suratul Hijr: 9)
ALLAH YA SANYA MU CIKIN MASU RIQO DASHI DA AIKI DA KARANTARWARSA, AMEEEN.