06/06/2026
KATSINA STATE HISBAH BOARD,
BATAGARAWA DIVISION.
KWAMANDAN HISBAH YA ZIYARCI DUKKAN GIDAJEN SAUKAN BAƘI DA KE ƘARƘASHIN ƘARAMAR HUKUMAR BATAGARAWA
A ranar Alhamis, 4 ga Yuni, 2026, wanda ya yi daidai da 18 ga Zul-Hijjah, 1447AH, Kwamandan Hukumar Hisbah ta Ƙaramar Hukumar Batagarawa, DC Malam Sadiq Ibrahim Gyaza, ya jagoranci wata tawagarsa domin gudanar da ziyarar gani da ido a dukkan gidajen saukan baƙi (Hotels) guda tara (9) da ke faɗin ƙaramar hukumar Batagarawa.
Tawagar ta haɗa da Mataimakin Kwamandan (ADC Special Services), Mal. Kabir Umar Sani da Sakataren Hukumar, Malam Abdullahi Yusuf Dandagoro, tare da sauran jami'an gudanarwa da shugabannin Outposts na ƙaramar hukumar.
Gidajen saukan baƙin da aka ziyarta sun haɗa da:
1. Jakada Hotel
2. Shalele Hotel
3. Fa'eez Hotel
4. Hayat Hotel
5. Liyafa Palace Hotel
6. Green View Hotel
7. Jamvaali Hotel
8. Murjani Hotel
9. Kaita Guest Inn
A yayin ziyarar, Kwamandan ya tattauna da manajojin waɗannan wurare tare da jaddada muhimmancin bin dokoki da ƙa'idojin Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina. Haka kuma ya yi amfani da damar wajen tunasar da su nauyin da ke kansu na tabbatar da kyawawan ɗabi'u, tsaftar muhalli da kuma kare al'umma daga duk wani abu da zai iya zama barazana ga tarbiyya da zaman lafiya.
Kwamandan ya bayyana cewa Hukumar Hisbah za ta ci gaba da aiki tare da masu ruwa da tsaki domin gina al'umma mai nagarta, tsaro da kyawawan halaye, kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
A nasu ɓangaren, manajojin gidajen saukan baƙin sun nuna matuƙar farin ciki da wannan ziyara, tare da bayyana godiyarsu ga Hukumar Hisbah bisa ƙoƙarin da take yi wajen tabbatar da zaman lafiya da ingantacciyar tarbiyya a cikin al'umma.
Sun kuma sake tabbatar da aniyarsu ta ci gaba da ba hukumar cikakken haɗin kai tare da kiyaye dokoki da ƙa'idojin da s**a dace.
Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina tana kira ga daukacin al'umma da su ci gaba da bayar da gudunmawa da haɗin kai domin yaƙi da munanan ɗabi'u da duk wani nau'in ɓarna, domin samun al'umma mai cike da tsaro, zaman lafiya da ci gaba.
Allah SWT Ya ƙara wa Hukumar Hisbah ƙarfi da basira wajen sauke nauyin da aka ɗora mata na umarni da kyakkyawa da hani daga mummuna.
Abdullahi Salihu Almujawwid, ASH
ICT Unit, KTSHB Batagarawa Division
20 Dhul-Hijjah, 1447AH | 06 June, 2026