Markazuttauhid Foundation

Markazuttauhid Foundation Kariya ga sunnah akan fahimta ta magabata na farko

*SANARWA SANARWA SANARWA* A madadin Kwamitin shirye shirye na Makarantar Sarkin Alhazzan Kabi dake cikin garin Argungu K...
13/12/2025

*SANARWA SANARWA SANARWA*

A madadin Kwamitin shirye shirye na Makarantar Sarkin Alhazzan Kabi dake cikin garin Argungu Kebbi State suna Gayyatar Kowa wajen WALIMAR ƊALIBAI da s**a sauke Al QUR'ANI MAIGIRMA (168) TAREDA MAHADDATA AL QUR'ANI MAIGIRMA (4)

*Rana: Gobe Lahadi da Misalin 9:00am 14/12/2025*

*Wuri: Harabar Makaranta dake FARIN TANKI AREA ARGUNGU.*

Allah yabada ikon Halarta.

Sanarwa daga Shugaban Shirye shiryen Gudanarda WALIMA: *Sheikh Bashiru Umar Argungu.*

RADDI ZUWA GA MALLAM ABDULLAHI UWAISU Da farko muna addu'a, Allah ya tabbatar damu akan daidai ya kiyaye mu zamewa.Yakam...
20/10/2025

RADDI ZUWA GA MALLAM ABDULLAHI UWAISU

Da farko muna addu'a, Allah ya tabbatar damu akan daidai ya kiyaye mu zamewa.

Yakamata Mallam uwaisu (bisa girmamawa)ya gane cewa idan yana so ya tabbatar da abinda malaman Musulunci (har da malaman da yake i'itimadi dasu) s**a raunana to dole ya kawo abinda ya dace da ilimi wajan inganta shi. Hakan kuma baze samu ba a wannan mas'ala.

Abu na biyu da Mallam ya kamata ya gane shine ba ko ina ake ilzami ba sannan ba ga kowa ake ilzami ba domin akwai ƙaa'ida wanda Ibnu Najeem Alhanafy wanda ya rasu 970 ya kawo a cikin littafinsa 'AL-ASHBAH WANNAZAA'IR' shafi na 125 inda yake cewa:
ما لزم من قول العالم فهو قوله ويلزم المنتمي لمذهبه
Abinda ya lazimci maganar malami shine maganarsa Sannan ze zama lazimi wa mabiyansa.

Haka ma Mallam Ashshaukany a cikin 'IRSHADUL FUHUL' 2/1057 yace:
ولو لزم من قول الإمام قول آخر فهو قوله ويلزم به أتباعه
Da a cikin maganar wani malami za'a samu wata magana da ta zamto lazimi gareshi, toh shine maganar sa kuma ze zamto lazimi (a iya yin ilzaminta) ga mabiyansa.

Tom wannan shine hikimar Mallam Lawan Triumph wajan kafawa yan dariku hujja da maganganun malamansu wajen kore abinda suke jinginawa zuwa ga Annabi s.a.w domin su mabiyane a wajan wadannan malaman.
Kaga kenan hujjojin Mallam Lawan Triumph suna lazimtar su Mallam uwaisu ne da sauran yan ɗariku ba shi Mallam Lawal Triumph ba. Domin Mallam Ashshaukany a cikin littafinsa 'IRSHADUL FUHUL' 2/1057 yana cewa:
وإن كان خصمك مقلدا لأحد الائمه جاز أن تلزمه بأقوال إمامه وبما يلزم منه
Idan abokin muhawararka ya kasance yana taqleedi wa daya daga cikin malamai, ya hallata kayi masa ilzami da daya daga cikin malamansa da abinda maganar malamin nasa zai dauka.

Musamman ma yanda su sufaye suke tsananin biyayya ga malamansu tare da yi masu taqleedi.

Tunda mas'alar da ake magana kanta ta hadisi ce, Shehu Muhammadu zakiyyu Ibrahim a cikin littafinsa 'A'ALAMUL MUWAƘƘI'EEN AN SUFIYYAH' shafi na 236 yace:
"وإذا كان الشيخ من الحفاظ المتقنين، جاز للمريد أن يأخذ بقوله في الحديث تصحيحاً وتضعيفاً، لأنه من أهل الاختصاص في ذلك"
Idan shehu ya kasance daga malaman hadisi da aka yarda da su, to ya halatta ga muridi yayi amfani da maganganun shehunsa wajen inganta hadisi ko raunanashi. Domin shi shehun yana daga cikin ma'abota keɓantuwa da hakan.

Haka zalika Shehu Abdullahi Surajuddeen a cikin littafinsa 'ALMANHAJUS SAWI FIT TASAWWUFI' shafi na 184 yana cewa:
"وللصوفي أن يقلد شيخه في الحديث إذا كان من أهله، لكن مع بيان الدليل عند الإمكان، فإن تعذر فلا حرج في التقليد مع الثقة"
Sufi zai iya yin taƙleedi wa shehinsa a cikin hadisi idan shehin nasa ma'abocin karatun hadisi ne. Sai dai tare da bayanin dalili idan akwai yiwuwar yin hakan. Idan kuma babu damar yin hakan to babu laifi yayi taƙleedi wa amintacce.

Bari nayi tambaya anan 😎. Shin Mallam ghazali beda ilimin hadisi kuma ba amintacce bane a wajanku? Idan ba malamin hadisi bane kuma ba amintacce bane ku fada mana sai mu gane abubuwa dayawa.

NA'AM MU DAWO CIKIN RADDI.
A masaa'il da ba na hadisi ba kuwa yan ɗariku ance su kure manejin biyayya su ga shehunansu.
Mallam umarul futi a cikin littafinsa 'RIMAHU' wanda aka jona da Jawahirul ma'ani fasali na 19 yace:
فالآداب التي تطلب من المريد في حق الشيخ أوجبها تعظيمه وتوقيره ظاهرا وباطنا وعدم الاعتراض عليه في شيء فعله ولو كان ظاهره أنه حرام.
Ladubba da ake nema daga wajen wuridi cikin hakkin shehu mafi wajabci shine girmama shi da ƙaunarsa da gudun yi masa musu cikin duk abin da ya aikata ko da zahirin wannan abun haramin ne.

Haka zalika ya ce:
وأن لا ينظر في أفعال الشيخ ولا يتعدى أمر شيخه ولا يتأول عليه كلامه بل يقف عند ظاهر كلامه ولا يطلب علة الأمر الذي يأمره به بل يبادر امتثال ما أمره سواء عقل معناه أو لم يعقل وليفعل ما أمره.
Kada yayi kallo cikin ayyukan shehu, kada ya tsallake umurnin shehu, kada yayiwa shehu tawilin maganarsa, kawai ya tsaya a zahirin maganar shehu, kada ya nemi dalili na wani umurni da shehu yayi masa, ya tafi kawai yayi riko da wannan umurnin ko ya fahimci ma'anar ko bai fahimta ba, ya aikata abun da aka umurce shi da shi.

A wani guri cikin fasalin yace:
ومن شرط المريد أن يكون بين يدي الشيخ كالميت بين يدي الغاسل.
Yana daga cikin sharadin muridi cewa ya zamto a gaban shehinsa kamar gawa a gaban mai wanke ta.

Daga karshe, idan Mallam Uwaisu ya dage dole sai Mallam Lawal Triumph ya karɓi duk abinda yazo daga waɗannan malaman kawai don ya kafa hujja da maganar su toh sai muyi ma Mallam uwaisu ilzami cewa😎😎:

Ilzami na farko: Mal Umarul futi ya kafa hujja da Ibnu Taimiyya da Ibnul ƙayyim a cikin 'RIMAHU', haka zalika Alhaji Ibrahim Inyas ya kafa hujja da Ibnu taimiyya a cikin 'ALBUDURUS SUƊA'I', kenan sai muce dole sai sun yarda da komai da yazo daga waɗannan maluman?

Ilzami na Biyu: Mallam Uwaisu yana bin mazhabar malikiyya kuma yana kafa hujja da maganar mawƙifin Imamu Ahmad, Meyasa be yarda da aƙeedar su ba game da siffofin Allah swt wanda ya saɓawa aqeedar ashaa'ira?

TOH WANNAN SHINE.

ALLAH YASA MUDACE YA TSARE MANA IMANINMU.

Idris Ilyasu Idris
20/10/2025

📚📚📚📚📚📚📚📚📚*KARATUN ZAURE NA (MUSDALAHUL HADITH)* CIKIN LITTAFEN:*NUKHBATUL FIKARI**Complete Karatun*Darasi na 1 zuwa na 2...
19/09/2025

📚📚📚📚📚📚📚📚📚

*KARATUN ZAURE NA (MUSDALAHUL HADITH)*


CIKIN LITTAFEN:

*NUKHBATUL FIKARI*

*Complete Karatun*
Darasi na 1 zuwa na 20

WALLAFAR
*Al Hafiz ibn Hajar Al Asƙalaniy Rahimahullah*

Tare da

*Malam Bashiru Umar Argungu (Hafizahullah).*

Website
https://darulfikr.com/s/201170

Facebook
https://www.facebook.com/profile.php?id=100025628496694

WhatsApp Group
https://chat.whatsapp.com/J2kozoegXCHG1oc2bLfTNo?mode=ems_copy_t

Telegram Channel
https://t.me/+X9-nnq0vR_E1MmQ0

Ayi sauraro lapiya

👇👇👇👇👇👇

Darulfikr.com is an Islamic website that provides a comprehensive resource for Muslims to deepen their understanding of Islam. It focuses on promoting the values of Islam and spreading the message of peace, love, and unity.

Address

Sokoto Road
Argungu
861412

Telephone

+2348140806030

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Markazuttauhid Foundation posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to Markazuttauhid Foundation:

Share