19/08/2026
Rundunar Hisbah Ta Kai Ziyarar Ta’aziyya Zuwa Ga Malama Fatsuma
Rundunar Hisbah Development Initiative ta Jihar Adamawa ta kai ziyarar ta’aziyya zuwa ga ɗaya daga cikin membobinta na Yola North Division, musamman a Wauru Jabbe Sub-Division, wato Malama Fatsuma, wadda take daga cikin iyaye mata da kuma Da’awah a ɓangaren mata na Rundunar Hisbah, bisa rasuwar mahaifiyarta.
A madadin Rundunar Hisbah Development Initiative ta Jihar Adamawa, muna miƙa saƙon ta’aziyyarmu ga Malama Fatsuma da iyalanta baki ɗaya bisa wannan babban rashi da ya same su.
Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya jiƙan marigayiyar, Ya gafarta mata kura-kuranta, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarta, Ya haskaka kabarinta, Ya kuma ba iyalanta da sauran waɗanda wannan rashi ya shafa haƙurin jure wannan babban ƙalubale.
Haka nan muna roƙon Allah Ya kiyaye mana sauran iyaye, Ya ba su lafiya da tsawon rai cikin biyayya da imani. Allah Ya sa idan tamu ta zo, mu cika da imani, Ya sa ƙarshenmu ya zama kyakkyawan ƙarshe.
إنا لله وإنا إليه راجعون
Allah Ya jiƙan mamaciyar, Ya gafarta mata. Amin Ya Rabbal Alamin.
E-sign
Hisbah Media team