Sheikh Zakzaky's Gallery

Sheikh Zakzaky's Gallery A New Official Page of Sheikh Zakzaky's Gallery Forum of the Islamic Movement In Nigeria

“Ya k**ata Musulmi su kasance tsintsiya madaurinki ɗaya, k**ar yadda maƙiyansu suke tsintsiya madaurinki ɗaya wajen fusk...
29/08/2026

“Ya k**ata Musulmi su kasance tsintsiya madaurinki ɗaya, k**ar yadda maƙiyansu suke tsintsiya madaurinki ɗaya wajen fuskantarsu. Don haka mu kasance masu haɗin kai;

Domin idan ba mu haɗu ba, ba mu yi wa juna taimako ba, za a samu babbar fitina da kuma ɓarna mai yawa. Lallai wajibi ne mu haɗa kanmu domin fuskantar abubuwan da suke tare da mu.”

Allah Maɗaukaki Ya ce:
وَالَّذِينَ كَفَرُوا بَعْضُهُمْ أَوْلِيَاءُ بَعْضٍ إِلَّا تَفْعَلُوهُ تَكُنْ فِتْنَةٌ فِي الْأَرْضِ وَفَسَادٌ كَبِيرٌ

[Suratul Anfal: 73]

▪️ Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) a wata hira da tashar Al-Alam.






29/08/2026

MUHIMMANCIN HADIN KAI, DA KUMA YI WA JUNA UZURI TSAKANIN MUSULMIDaga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)"Yanzu Maulidi da...
28/08/2026

MUHIMMANCIN HADIN KAI, DA KUMA YI WA JUNA UZURI TSAKANIN MUSULMI

Daga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

"Yanzu Maulidi dai insha Allahu mukan ce ya k**ata ya zama akwai 'theme' duk shekara yakan zama akwai 'theme' daidai wannan lokaci mun ta (yin) magana kan Hadin Kan Musulmi, su mutanen nan suna ganin k**ar Hadin Kan Musulmin nan k**ar yana nufin su bar abin da s**a fahimta ne su zo na wasu, su sun dauka haka ake ce musu; mu ka ce musu ba haka bane, kusanci ake so.

"Kun ga katangar karfen nan da aka sa tsakakin Musulmi da Musulmi har ya zama ba a fahumtar juna, mummunan abu ne. sai ayi ta gaya maka wani abu game da mutum, alhali ba haka bane, kai ba ka kusance shi ba-ka yi nesa da shi, shi ma ya yi nesa da kai.

"To in ku ka zo kusa wadannan abubuwan da ake fada kila ka ga ba haka bane, in ma haka nan ne ai ka ga za ka gani ko? ka ga sai ka ce masa me ya sa ku ke abu kaza ne? Kamar zagin sahabban nan, me ya sa ku ke kunduma musu ashar? Sun muku mene ne? To kila in ka matso za ka iya gane karya ake yi. To shi ya sa su ke ce maka kar ka matsa, su suna son abin da su ka gaya maka ne kawai ka tsaya a kai.

"To kusancin nan yana warware abubuwa da dama, don wadansu abubuwan mutum yana yin abu ne sai su bashi fassara, ko za su gani ne a hoto sai su ce to gashi nan yana kaza. To a bisa ka'ida na shari'a ba haka ake yi ba, ba in ka ga mutum yana abu sai ka ce kaza ba, a'a sai ka ce mene ne wannan? Ka tambaye shi mana, idan ya fada maka, ya fada maka hujjarsa, idan ka gamsu sai ka ce oho abin haka ne, idan kuma ba ka gamsu da hujjar ba sai ka masa uziri tunda shi haka yake gani, ko ba a lura ba?

"Akwai daga cikinsu da s**a yi adawa da wani Malaminsu da ya ce shi a wurinsa Maulidi bidi'a ne, kuma matsayarsa kenan a cewa Maulidi bidi'a ne, sai ya ce amma masu yi za su iya samun lada wajen Allah saboda sun yi ne saboda son Annabi. Haba! Ai (sai s**a rika cewa) to shi Annabi ne da zai fadi wannan? To amma Malaminku ne dai.

"Sai wasu kuma suna cewa wai ana cewa ya ce a yi Maulidi, ba a ce ya ce a yi Maulidi ba, shi bai ce a yi Maulidi ba kuma a wurinsa bidi'a ne, amma abin da ya yi yana bawa masu yi uziri ne, ko ba a lura ba? Mu kuma abin da mu ke nema daga irin ku kenan. Idan ku ka ga mutum ya na wani abu wanda ku a wurinku ba daidai bane, shi kuma sai ya ce ga hujjarsa, to ku yi masa uziri ko ba ku yarda da hujjar ba.

"To in muka yi magana irin wannan nan da nan sai su birkita mana magana. Na taba magana irin wannan sai (wani) ya ce ashe Kafirai ma sai a yi ta musu uziri, na ce Innalillahi Wa Inna Ilaihir Raji'un! Na ce ka yi ma Kafiri uziri? Ya yi Kafirci? Ko mai kisan kai yana kisan kai, sai ya ce ai dalilin da ya sa ya yi kisan kan kaza ne, sai ace oo dalilin kenan, sai ka yi masa uziri, haka na ce? Haka mu ka ce? To don me za ka dauki maganar ka kai shi wani wuri daban? Mu na cewa ne; shi wannan ya na yin abin nan da i'itiqadin akan cewa ibada ne ga Allah, kai kuma a wurin ka ba ibada bane, kai a wurinka bidi'a ne, kai a wurin ka babu nassi da ya ce a yi.

"To sai ka tambaye shi, sai ya ce eh shi yana da nassin ma, sai ya kawo maka nassin, sai ka ce a'a wannan a littafinku ne, mu kuwa a littafinmu bamu da wannan nassin. To ba sai ka bashi uziri ba? Ka ga a littafinsa akwai nassi ko? Naka kuwa babu ko? To ka ga ashe ba ya na yin bidi'a bane shi, ko ba a lura ba? Koda a wurin ka bidi'a ne amma shi ya na yin mene ne? Shi ya na da hujjar yin abin da yake yi, shi ne abin da mu ke cewa.

"Ba mu ce maka in mutum yanzu ya na barna, ko ya na abin da yake karara Allah Ya haramta sai ka yi masa uziri ba. Ba mu ce in mutum ya na kurban giya ya ce shi dalilin da ya sa ya ke kurban kaza ne ba, sai ka ce shikenan ka yi masa uziri ba, ba haka muka ce ba, abin bai kai haka nan ba, mu na maganar abin da yake yi ne na wani ibada wanda ya ke kuma shi ya na da dalili, amma kai ba ka gamsu da dalilin ba, sai ka yi masa uziri. Ba mu ce lallai ka yarda ba, amma a kalla ka yi masa uziri, uzirin da za ka yi masa ka ce to shikenan kai ma'azuri ne akan abin da ka ke yi.

"Irin wannan ne wani Malaminsu ya ce haka nan ai, ya ce; masu yi suna iya samun lada wajen Allah saboda sun yi ne saboda Annabi. To ka ga ya musu uziri ne ba ya ce a yi bane, ba kuma ya ce eh shi ya yarda a yi bane, ya yi ma masu yi uziri ne. To kuma wannan uzirin yana da kyau haka nan. Tsakaninka da dan'uwanka Mumini sai ka masa uziri shi a wurinsa yana da hujja, ta nan ne muka samu bambance-bambanen mazahib, sai ka ga wannan ya ce kaza ake yi, wancan ya ce kaza ake yi, sai mu yi ma mutum uziri koda ba mu yarda ba, akwai abubuwa da dama da mu ba mun yarda ne da dalilinsu ba, amma sun ce sunna ce, kuma suna da shi a littafinsu.

"To sai mu musu uziri, wata sunnar mun san ma ba sunna bane, wasu ma mun san wanda ya kirkiro sunnar, to amma shi bai san an kirkiro sunnar bane, wata sunnar tana nan an ce mata tana cikin sahihai, kuma mun san ba gaskiya bane, to kuma mun san ma wanda ya kirkiro sunnar, to amma shi yana bin kirkirarren abu ne? A iyakan fahimtar sa shi a wurinsa daidai ne, to sai mu masa mene? Yauwa sai mu masa uziri, sai ka masa uziri, illa iyaka in tafiya ta yi tafiya sai ka ce ku a wurinku haka ne, amma a wurinmu ba daidai bane, kuma ka ji namu dalilin.

"To na san komai yadda ka yi da mutanen nan, wasu s**an yi sassauci dan kadan amma ka san suna da magidanta, su fa suna ga magidantan nan nasu fa k**ar iyayen gijinsu ne, in s**a ce abu ko an shekara nawa ana cewa bashi da kyau, wata rana magidantan nasu suna dawowa su ce yana da kyau, sai kuma a dawo ace yana da kyau. Haka fa s**a ce attafau ba a ziyarar kabari shirka ne, s**a yi shakara da shekararu suna haka nan, sai kuma s**a zo s**a ce "Ziyaratul Kuburu Mashru'u" shari'a ta yarda da shi, sai kuma aka dawo (wai) ai mashru'i ne ana yi, amma kuma sai s**a ce banda mata, wai Annabi ya ce "La'anallahu Zaa'irat" Allah Ya sauwake, ka san suna da wasu fassarori da s**an ba wa wasu abubuwan nasu.

"Shikenan dai, mu dai mukan musu uziri, su ne basu mana ta kowane hali, sai a yi abinda su suke so. Ala ayya halin tafiya tana nan tana tafiya, ana nan ana samun samun sauyi, yanzu sakon Maulidi dama baya ga ainihin mukan kyale masu s**a, mukan ta yin abinda ya k**ata ne, mun dade muna sakon cewa a fahimci juna, a kusanci juna, a daina kyamar juna, a daina nesa da juna, a (matso) kusa-kusa a ji ta bakin kowa, don in ma ba ka yarda ba ka yi ma dayan uziri, to da haka nan zai yi kyau, to kuma suna ganin yana tasiri a wannan."

__Bangaren jawabin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) yayin ganawa da kwamitin Maulili a ranar Lahadi 30 Safar, 1447, wanda ya yi daidai 24/8/2025 a gidansa da ke Abuja.

— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky







28/8/2026

BAMBANCIN KIRANMU DA SAURAN KIRAYE-KIRAYEDaga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)“Kamar yadda mu ke cewa; abin da ya bamb...
27/08/2026

BAMBANCIN KIRANMU DA SAURAN KIRAYE-KIRAYE

Daga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

“Kamar yadda mu ke cewa; abin da ya bambanta kiran da mu ke yi da wanda sauran su ke kiraye-kiraye shi ne batun meye tabbatar addini? Da yawan mutane su ba sun damu da tabbatar addininbane., kuma ba abin da ya dame su. Su abin da s**a dauka kawai kasar nan da mu ka samu kanmu a ciki bature ne ya zo ya ci mu da yaki ya kafa mana kasa ya hada mu da wanda y hada mu, ya dankara mana harshe, da tsari da komai da komai. Kuma k**ar dole ne a tafi a haka nan. Kuma abin da ya dame su kawai wasu-in ma suna da kishin addini, shi ne a ce Musulmi ne ya ke rike da manyan muk**ai shikenan abin da ya dame su. Kuma in nasu ya samu, kuma suna si su kuma su samu, in nasu ya samu su ma su samu.

"Saboda haka kawai ana ta jan mutane akan cewa wannan rikici ne kawai na siyasa tsakanin ace wane ne shugaba? Ta ina ya fito? Shikenan abin da ya dame su. Saboda haka su mutanensu su shiga ciki su rayu a ciki, shikenan an gama. Zai yiwu a sauya wannan al'amari? Za su ce sam ba zai yiwu ba. Ba zai yiwu addini ya dawo ba? Sai su ce maka tarihi kenan, da can ya yi mulki amma yanzu ba zai yi mulki ba-ba zai yiwu ba, saboda mene? Za su ce ai saboda kasar ba Musulmi ne zallah ba, ko wani abu mai k**a da haka nan.

"To wannan abin dayawan mutane bai dame su ba, kawai abin da za su samu ne su sa a cikinsu, in rayuwarsu ta yi daidai, to addini ya yi daidai. To kuma mafi yawan mutane haka na suke, fadin Imam Husaini a ranar Karbala; Ya ce mutane bayin duniya ne, in addini ya biya bukatar duniyarsu to ya yi, in kuwa ya cutar da duniyarsu, to kadan ke yin addini. Sai ya zama su wadanda su ka zo kashe Imam Husaini su a wurinsu shi ya saba ka'idar addini ne, saboda bai bi sarki ba, wai sarki zai mulki. Shi (Imam Husaini) ne alamin addini, shi ne Magajin Manzon Rahama (S) ba kawai ta fuskar (Jini ba).

"Kun san mutane s**an cewa jikan Annabi, kawia su na tsammanin mujarradin shi jikan Annabi ne saboda jini, ba haka bane, ya wuce nan. Shi ne Magajin Annabi, shi Manzon Allah ya kaddamar da magajinsa ya ce bayansa (Imam) Ali za a bi, bayan Ali sai Hassan (dansa) bayan Hassan sai Husaini. To bin Ali bin Annabi ne, bin Hassan bin Annabi ne, bin Husaini bin Annabi ne.

"To su kuwa mutane sai s**a dauka a'a wanda ke da sarauta shi ne za a bi. To wane ne sarki zamanin (Imam) Husaini? Yazidu ne dan Mu'awiya. Su a wurinsu shi ne za su bi, kuma shi ne addini, shi ne ma su ke kiransa sarkin Musulmi, ba ma sun ce masa sarkin Musulmi bane (kawai) sun ce masa sarkin Muminai, Mumini kuwa ai a lamarin ma wato ka ga in ka ce Mumini ai kana nufin kenan mai cikar imani kenan, s**a dauka duk wanda ya ce ya yi imani da Allah sunansa Musulmi ne, ba shi ne ma'anar AmirulMuminina ba, ma'anar AmirulMuminina; a cikin Muminai to shi ne babbansu, ba wai Muminai ne gasu da yawa shi ne sarkinsu ba, ba abin da ya ke nufi ba kenan, ba ga Muminai ne shi kuma ga sarkinsu ba, a'a, wane ne mai k**alar Imani bayan Manzon Allah? Shi ne wannan (Imam Ali AS) shi ne ya zama Amir a Imani, ma'ana Amir a Imani, an fahimta ai.

"Wa ya kai shi Imani baya ga Annabi? Babu. To shi ne Amir a Imani, ba yana nufin ga wadansu mutane duk sunansu Muminina ne kuma shi ne sarkinsu ba, ba abin da ya ke nufi kenan ba, su kuwa sauran mutane abin da su ka dauka kenan, sun dauka sarkin Musulmi (shi) kaga ga Musulmi ga kuma sarkinsu, ko ba haka ba? Yauwa. Su Musulmin nan kowane iri ne suke, ga su dai ga sarki, yauwa.

"To shi Imam Husaini wajibi ne a masa da'a, wujuban lallai a masa da'a, amma su ba haka su ka dauka ba, wanda su ka biyo shi duu sun dauka shi ma zai zama sarki ne su kuma su samu mukami, da s**a ga abin yanzu ashe ba sarauta za a samu ba-za a fille wuya ne, sai su ka gudu, sai wadanda s**a san matsayin Imam Husaini su s**a tsaya tare da shi. S**a san shahada tare da shi nasara ne, ta haka nan sai ya gwada ma duniya cewa ba ana bin Azzalumai bane, ba a bin su, ko da za su tsinke wuya ne, ana tsayawa ne kyam a tafarki har mutum ya bada ransa.

"Don haka ya zama abin koyi ga dukkan wanda za su biyo baya, su sani cewa da ace 'surrender' ga azzalumai da bin sarakai shi ne addini, to da shi ya bi. To kuma abin mamaki za ka ga mutane suna nikan gari su je su ziyarci Imam (Husaini) su taka su kuma sa bakaken kaya su daddaki kirji su yi koke-koke, amma in kana magana da su sai su ga su za a bi waliyin zamaninsu ne. In ce to kai ba ka ma fahimci abin da ya sa kla zo nan ba kenan ko?

"In ka ga mutum yanzu yana bin Yazidun zamaninsa, to in da ya zo wancan zamanin ne ku na tsammanin me zai yi? Yazidu zai bi, da kila ma in dan Muljanata ya ce ya je su tsinko kan Imam Husaini, shi zai je ya tsinko kai din, suna ganin ana bin sarki ne mai mulki, yanzu ba a yayin sarki ana yayin shugaban kasa ne, in dai ka na tunanin cewa wanda ke da iko shi ake bi-in shi tunaninka kenan, to lallai da ka yi zamani da Yazidu da Yazidu za ka bi, don shi ke da iko, ba ma (Yazidu ba) koda zamanin Annabi Musa ka ke, to da Fir'auna za ka bi, saboda Fir'auna ke da iko.

"To kun ga lokacin su mutanen Fir'auna sai s**a ga cewa lallai Fir'auna keda gaskiya, saboda shi keda mulki, shi kuwa (Annabi) Musa ba shi da mulkin komai, to wa ake bi? A nasu tunanin wa ake bi? Mai mulki, yauwa, mai gwamnati. To amma mu kuwa a wajenmu in ka tambaye mu sai mu ce wanda Allah Ya ce a bi. To ka gaya min, Allah Ya ce a bi Fir'aunoni ne? In da (Allah) Ya na son a bi Fir'aunoni ba zai aiko Musa da sako ba tunda ga Fir'auna. Ba Fir'aunoni ake bi ba, ana bin wanda Allah Ya aiko ne.

"To bayan Allah Ya aiko ManzonSa na karshe, daga nan sai bin wanda ya khaliftar, wanda Manzon nan ya khaliftar, daga nan sai kuma wanda suke bin tafarkinsa, an fahimta ai. Wa ke ce ma mutane a bi Allah a bi Manzo? To shi ne za a bi kenan, ba wanda ya ke cewa shi ke da mulki a bi shi ba. Ka san s**an cewa dole duk inda ka ke dole ka bi dokar kasa, to wa ya ce muku dokar kasa ne? Ba dokar kasa mu ke magana ba, muna batun cewa dokar da ya saba ma na Allah shima za ka bi ne? Abin da ake cewa kenan, dokar da ya saba ma na Allah shima za ka bi ne? Kun san wasu suna cewa kenan ku na nufin ba za ku bi dokar kasa ba? Ka ji wawaye! To yanzu ance muku yanzu in muna tafiya a titin mota sai mu bi hagu-mu ba za mu bi dama ba! Mu ci karo, in mun ga an sa jan haske mu danna a guje mu bi! Wannan ku wawaye ba abin da mu ka ce ba kenan, mu na ce muku abin da ya saba ma na Allah bai hau kan mu ba. Dole ne ya zama doka ba za ta saba ma na Allah ba.

"Su kuma wadannan sun ce ba ruwansu ma da Allah din, su ba ruwansu, su ba ma suna batun Allah ba ne, su abin da ya dame su daban. Kuma in suna dokarsu ba su tunanin Allah Ta'ala Ya ce, ko Manzon Allah Ya ce.

"To komawa ga nizamin addini shi ne ya zama cewa; an zo da nizamin da ba zai taba saba ma na Allah ba, wannan kuwa zai yiwu, kuma shi ya sa ma su ke jin tsoron yiwuwar nasa din ai. Shi ya sa kuma ka ga tunda aka samu Jamhuriyyar Musulunci ta Iran duk s**a dunga kuntata ma wannan Jamhuriyyar, sai dai su za a bi su, su ka dunga kuntata ma Jamhuriyya din, su ka sha mamakin duk kuntatawan da su ke mata ta wanzu, shekaru arba'in yanzu da shida, to a wannan karon ne su ka yi mafarkin rusa ta, da su ka ce sai su ka dandana, da su ka dandana kuda sai su ka ce a'a'a, ashe su na da karfi ne haka? Yanzu su na nan su na sake shiri na kumaji za su koma, muna fatan randa su ka koma kuma Allah Ya dada muzanta su fiye da muzanta sun da ya yi a baya.”

— Ɓangaren jawabin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) yayin rufe IVC wanda aka yi a shekarar 1447/2025 a gidansa da ke Abuja.

— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky






14 Rabi'ul Auwal, 1448
27 August, 2026

MUHIMMANCIN HADIN KAI, DA KUMA YI WA JUNA UZURI TSAKANIN MUSULMIDaga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)"Yanzu Maulidi da...
26/08/2026

MUHIMMANCIN HADIN KAI, DA KUMA YI WA JUNA UZURI TSAKANIN MUSULMI

Daga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

"Yanzu Maulidi dai insha Allahu mukan ce ya k**ata ya zama akwai 'theme' duk shekara yakan zama akwai 'theme' daidai wannan lokaci mun ta (yin) magana kan Hadin kan Musulmi, su mutanen nan suna ganin k**ar Hadin kan Musulmin nan k**ar yana nufin su bar abinda s**a fahimta ne su zo na wasu, su sun dauka haka ake ce musu; muka ce musu ba haka bane, kusanci ake so.

"Kun ga katangar karfen nan da aka sa tsakakin Musulmi da Musulmi har ya zama ba a fahumtar juna, mummunan abu ne. sai ayi ta gaya maka wani abu game da mutum, alhali ba haka bane, kai baka kusance shi ba, ka yi nesa da shi, shi ma ya yi nesa da kai.

"To in ku ka zo kusa wadannan abubuwan da ake fada kila ka ga ba haka bane, in ma haka nan ne ai ka ga za ka gani ko? Ka ga sai ka ce masa me yasa ku ke abu kaza ne? Kamar zagin sahabban nan, me yasa ku ke kunduma musu ashar? Sun muku mene ne? To kila in ka matso za ka iya gane karya ake yi. To shi yasa suke ce maka kar ka matsa, su suna son abinda s**a gaya maka ne kawai ka tsaya a kai.

"To kusancin nan yana warware abubuwa da dama, don wadansu abubuwan mutum yana yin abu ne sai su bashi fassara, ko za su gani ne a hoto sai su ce to gashi nan yana kaza. To a bisa ka'ida na shari'a ba haka ake yi ba, ba in ka ga mutum yana abu sai ka ce kaza ba, a'a sai ka ce mene ne wannan? Ka tambaye shi mana, idan ya fada maka, ya fada maka hujjarsa, idan ka gamsu sai ka ce oho abin haka ne, idan kuma ba ka gamsu da hujjar ba sai ka masa uziri tunda shi haka yake gani, ko ba a lura ba?

"Akwai daga cikinsu da s**a yi adawa da wani Malaminsu da ya ce shi a wurinsa Maulidi bidi'a ne, kuma matsayarsa kenan a cewa Maulidi bidi'a ne, sai ya ce amma masu yi za su iya samun lada wajen Allah saboda sun yi ne saboda son Annabi. Haba! Ai (sai s**a rika cewa) to shi Annabi ne da zai fadi wannan? To amma Malaminku ne dai.

"Sai wasu kuma suna cewa wai ana cewa ya ce a yi Maulidi, ba a ce ya ce a yi Maulidi ba, shi bai ce a yi Maulidi ba kuma a wurinsa bidi'a ne, amma abinda ya yi yana bawa masu yi uziri ne, ko ba a lura ba? Mu kuma abin da muke nema daga irin ku kenan. Idan ku ka ga mutum ya na wani abu wanda ku a wurinku ba daidai bane, shi kuma sai ya ce ga hujjarsa, to ku yi masa uziri ko ba ku yarda da hujjar ba.

"To in muka yi magana irin wannan nan da nan sai su birkita mana magana. Na taba magana irin wannan sai (wani) ya ce ashe Kafirai ma sai a yi ta musu uziri, na ce Innalillahi Wa Inna Ilaihir Raji'un! Na ce ka yi ma Kafiri uziri? Ya yi Kafirci? Ko mai kisan kai yana kisan kai, sai ya ce ai dalilin da yasa ya yi kisan kan kaza ne, sai ace oo dalilin kenan, sai ka yi masa uziri, haka na ce? Haka mu ka ce? To don me zaka dauki maganar ka kai shi wani wuri daban? Muna cewa ne; shi wannan yana yin abin nan da i'itiqadin akan cewa ibada ne ga Allah, kai kuma a wurin ka ba ibada bane, kai a wurinka bidi'a ne, kai a wurin ka babu nassi da ya ce a yi.

"To sai ka tambaye shi, sai ya ce eh shi yana da nassin ma, sai ya kawo maka nassin, sai ka ce a'a wannan a littafinku ne, mu kuwa a littafinmu bamu da wannan nassin. To ba sai ka bashi uziri ba? Ka ga a littafinsa akwai nassi ko? Naka kuwa babu ko? To ka ga ashe ba yana yin bidi'a bane shi, ko ba a lura ba? Koda a wurin ka bidi'a ne amma shi yana yin mene ne? Shi yana da hujjar yin abinda yake yi, shi ne abinda mu ke cewa.

"Ba mu ce maka in mutum yanzu yana barna, ko yana abinda yake karara Allah Ya haramta sai ka yi masa uziri ba. Ba mu ce in mutum yana kurban giya ya ce shi dalilin da yasa ya ke kurban kaza ne ba, sai ka ce shikenan ka yi masa uziri ba, ba haka muka ce ba, abin bai kai haka nan ba, muna maganar abin da yake yi ne na wani ibada wanda yake kuma shi yana da dalili, amma kai ba ka gamsu da dalilin ba, sai ka yi masa uziri. Ba mu ce lallai ka yarda ba, amma a kalla ka yi masa uziri, uzirin da za ka yi masa ka ce to shikenan kai ma'azuri ne akan abin da ka ke yi.

"Irin wannan ne wani Malaminsu ya ce haka nan ai, ya ce; masu yi suna iya samun lada wajen Allah saboda sun yi ne saboda Annabi. To ka ga ya musu uziri ne ba ya ce a yi bane, ba kuma ya ce eh shi ya yarda a yi bane, ya yi ma masu yi uziri ne. To kuma wannan uzirin yana da kyau haka nan. Tsakaninka da dan'uwanka Mumini sai ka masa uziri shi a wurinsa yana da hujja, ta nan ne muka samu bambance-bambancen mazahib, sai ka ga wannan ya ce kaza ake yi, wancan ya ce kaza ake yi, sai mu yi ma mutum uziri koda ba mu yarda ba, akwai abubuwa da dama da mu ba mun yarda ne da dalilinsu ba, amma sun ce sunna ce, kuma suna da shi a littafinsu.

"To sai mu musu uziri, wata sunnar mun san ma ba sunna bane, wasu ma mun san wanda ya kirkiro sunnar, to amma shi bai san an kirkiro sunnar bane, wata sunnar tana nan an ce mata tana cikin sahihai, kuma mun san ba gaskiya bane, to kuma mun san ma wanda ya kirkiro sunnar, to amma shi yana bin kirkirarren abu ne? A iyakan fahimtar sa shi a wurinsa daidai ne, to sai mu masa mene? Yauwa sai mu masa uziri, sai ka masa uziri, illa iyaka in tafiya ta yi tafiya sai ka ce ku a wurinku haka ne, amma a wurinmu ba daidai bane, kuma ka ji namu dalilin.

"To na san komai yadda ka yi da mutanen nan, wasu s**an yi sassauci dan kadan amma ka san suna da magidanta, su fa suna ga magidantan nan nasu fa k**ar iyayen gijinsu ne, in s**a ce abu ko an shekara nawa ana cewa bashi da kyau, wata rana magidantan nasu suna dawowa su ce yana da kyau, sai kuma a dawo ace yana da kyau. Haka fa s**a ce attafau ba a ziyarar kabari shirka ne, s**a yi shekara da shekararu suna haka nan, sai kuma s**a zo s**a ce "Ziyaratul Kuburu Mashru'u" shari'a ta yarda da shi, sai kuma aka dawo (wai) ai mashru'i ne ana yi, amma kuma sai s**a ce banda mata, wai Annabi ya ce "La'anallahu Zaa'irat" Allah Ya sauwake, ka san suna da wasu fassarori da s**an ba wa wasu abubuwan nasu.

"Shikenan dai, mu dai mukan musu uziri, su ne basu mana ta kowane hali, sai a yi abinda su suke so. Ala ayya halin tafiya tana nan tana tafiya, ana nan ana samun samun sauyi, yanzu sakon Maulidi dama baya ga ainihin mukan kyale masu s**a, mukan ta yin abinda ya k**ata ne, mun dade muna sakon cewa a fahimci juna, a kusanci juna, a daina kyamar juna, a daina nesa da juna, a (matso) kusa-kusa a ji ta bakin kowa, don in ma ba ka yarda ba ka yi ma dayan uziri, to da haka nan zai yi kyau, to kuma suna ganin yana tasiri a wannan."

__Bangaren jawabin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) yayin ganawa da kwamitin Maulili a ranar Lahadi 30 Safar, 1447, wanda ya yi daidai 24/8/2025 a gidansa da ke Abuja.

— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky




13/Rabi'ul Auwal/1448
26/August/2026

MANUFAR MAULIDI A SUNNA; SAƁANIN NA AL'ADA— Daga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)“To maulidi shi sai mu ka yi sa'a, sa...
25/08/2026

MANUFAR MAULIDI A SUNNA; SAƁANIN NA AL'ADA

— Daga Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

“To maulidi shi sai mu ka yi sa'a, sa'ar da mu ka yi shi ne; shi an san shi a nan bisa al'ada. Wanda aka sani bisa al'ada ba shi ne mu mu ke rayawa ba. Mu mu na raya na sunna ne-ba na al'adar ba, amma kasantuwar in an san abu a al'ada zai maka sauki, sai ka gina a kai, daga nan sai ka raba mutane da al'adun, ka dora su a kan sunna din.

“Dalilin da ya sa na ce masa al'ada; su kawai ana bikin ne a yi murna. Na san muna yara akwai wani maulidin da mu ke ce masa wai kwanan zaune, kawai ba a bacci ne, to kuma kowanne zai dan tafi da tanadin ko gyada, (saboda) koda ya dan ji bacci ya dan ci, ko wani abu maik**a da haka nan. Za a kwana ne dai a yi ta hanayinya, a ci abinci kawai a rarraba abubuwa, wadansu na raba irin nau'in masa da su ke ce ma sunasir, su yi wannan a rarraba, shi kenan kawai sai a ce ai an yi maulidi an gama shi kenan sai badi kuma. A yi biki kawai, karshensa can da wajen sallar subahi a yi addu'a a watse, an yi kwanan zaune. Wanda ya kan zo ya yi magana ma sai kawai ya yi ta al-marori, a yi ta bada dariya-a yi ta dariya.

“Haka kuma sai ya zama irin wannan daga baya da wasu su ka fara kiran maulidodi, kowanne sai a kira wani mai maulidi, shi kuma sai ya bada wadansu labarurruka k**ar tatsuniyoyi, duk dai wani a yi dariya. Wani tarihi ne amma sai a maishe shi k**ar tatsuniya, wani ma ana kirkirowa ne-da ji ka san ana kirkirowa ne.

“Akwai wani da mu ka je mu ka samu ya na magana din na ce wannan amma ba ya ji labarin bane, ina tsammanin a lokacin da ya ke bada labarin ne ya ke kirkiro abinsa. Ya na bada labarin kwamawar da Sayyidi Ali ya yi da wani, sai ya na cewa sai ya ka ke jin wani ragwagwagwaf, ya na ta wani abu. Na ce ha'a, amma ina jin shi ya kirkiro labarin a yayin da ya ke yi, ya na ta fadan wadansu abubuwa wadanda wato kusan k**ar mutum yakan burge ne idan ya kawo labarin da ba a taba ji ba. Wani labarin wani Daƙayanusu, da wane labarin mene, duk su birkita labarin, kowanne dai ya na kokarin ya kawo wani labarin wata al-mara wanda ba a taba jin irin wannan al-marar ba.

“To in mutum ya lura cewa inda zai tattara a dunƙule ya ce mene ne maƙasudin maulidin al'ada? Meye hadafin maulidin al'ada? Entertainment ne? Wato ana jiyar da dai ne a yi nishadi? Sai ya ce eh ana yi, mutane su na murna ne kawai-suna murna ne cewa lokacin maulidin Annabi ya zagayo su na murna, illa iyaka. To in da za ka ce mene ne hadafin wannan bayanan da mutane su ke yi? Lallai zai ce bai da manufa, tunda kowa yana kokari ne ya zo da wani labari ma da ba a taba ji ba, a ce ai labari sai wane, wani kuma nan inda ya bar labarin nan a aka barshi, yauwa.

“To mu namu ba haka nan bane. Mu abin da mu ke fadi sai ya zama ya na da ma'ana ga mutane, mutane su na amfana da shi abin da ake gaya musu, mu mu na tunatar dasu ainihin abin da ya rataya a wuyansu ne a matsayinsu na musulmi, da kuma abin daya shafe su a yanzu din nan, ba mu na basu tarihi ne kawai ba, a'a mu na gaya musu su yanzu zancen nan da ake yi, to irin yadda aka rayar da addini a wancan lokacin shi ne ake so yanzu ya rayu, kuma rayuwar nan ya na rayuwa ne a jikkunan mutane-a zukatansu da jikkunansu, kuma mutum sai ya ga abin da ake fadi ya shafe shi ne.

“Ba ana bashi labari ne ba, in ka na bada labarin wani sarki Dakayanusu haka nan, sai ya ce wani sarki ne haka nan, ko kuma ma ka bada labarin Sayyidi Ali ya fafata da wani Kartagi, shi wannan mutumin ainihin wai ko za a tashe shi bacci ma sai an sa zuga-zugi masu yawan gaske an dunga hura wuta a hancinsa da kyar zai farka, wani ma aka ce ainihin cikin hancinsa ma har ana yin gona a yanko ciyayi da sauransu.

“To in mutum ya ji wannan labarin zai yi shiru ya ce to dai shi kenan. Meye amfanin labarin? Bai da wani amfani sam-sam-sam. Da wani wanda da ya yi wani haka ya zubar da jibinsa bayan su na yaki da Sayyidi Ali sai ga kawai irin bakaken kiyashin nan sun bayyana, asalinsu ma dai kenan (a cewar su) sai ga kiyasai su ka bayyana. Za ka ga ana ta bada labarin abubuwa wanda ya ke bashi da wani ma'ana, amma dai kuma shi kenan dai, kila dayake ana ta tayi sai ainihin mutane su yi ta jin dadi su yi ta dariya. Da labarin Zumbuli kakan marowata, to wato ainihi kawai kawai ana so a yi ta dariya ne kawai, k**ar kida da busa.

“Shi kuwa wannan (namu) sai ya zama ana magana ne (da) kai kan abin da ya shafe ka, in ma labarin Fir'auna za a baka, za a baka labarin Fir'auna ne ta yadda za ka gane yanzu akwai magajin Fir'auna din, za ka gane ashe ba da ne kawai aka yi Fir'auna ba-yanzu ma akwai, har ma za ka gano waye Fir'aunan. In kuma aka gaya maka labarin (Annabi) Musa za ka gane ashe ana nufin duk lokacin da aka samu Fir'auna sai an samu Musa ne, kuma har ka gano waye Musan zamaninka-in ka gano Fir'aunan zamaninka. Har sai ka ga abin kai ana magana da kai ne-ya shafe ka ne kai yanzu.

“To duk abin da mu ke yi hadafinsa duk abu guda ne, na neman raya addini din nan, dawo da addini ya gudana a zukata da jikkunan al'umma, shi ne ma'anar raya kasa bayan mutuwarta, raya kasa bayan mutuwarta k**ar yadda Allah Ta'ala Ya ke bada misali a Alkur'ani; Yakan bada shi ta yadda da abu 'madi' da mutane za su gane, k**ar in an yi ruwan sama busasshiyar kasa ta fidda tsirrai ka ga abu ya zama lif-lif ya yi kore, zuwa can ya kai ga lokacin girbi a samu natija.

“To da irin wannan sai a nuna cewa shi ma kazalik, in aka yi ruwan wa'azi ainihin mutane kuma masu busassun zukata su kuma sai su sha wannan ruwan wa'azi sai su rayu, sai ayyukan kirki duk su bayyana daga garesu, kuma sai girbi natijoji masu amfani a duniya kafin girban na lahira.

“To shi ne; manufa shi ne raya addinin nan, dawo da addinin nan ya zama ya rayu daram, ba tarihin addini ake bayarawa ba, ana raya addini ne ya zama tamkar yadda na farko su ka yi shi ne ake yi yanzu, ba ana jin labarin na farko ne kawai ba, ana yunkuri ne a aikata.

“To dole ne ya zama dukkanin kalaman da za a rika yi a maulidi duk ya zama bangare ne na wannan hadafin, in wasu da za ka tambaye su to meye hadafin wannan bayanin da ku ke yi? In ma da akwai, kila ma ba za su ce maka akwai hadafi ba, amma kila mutum shi zai ce maka ya na so ya burge ne, ya bada wani labari wanda ba a taba jin irin sa ba, ka ga don haka ne ma kullum sai ka ga su na ta tunanin labarurrukan da za su fada wanda ba su fada a baya ba.

“To mu ba mu na tunanin fito da wani abu sabo bane, in za mu yi ta maimaita abu guda, indai natijarsa shi ne rayuwa din-zai iya rayarwa Masha Allah, yauwa.

__Ɓangaren jawabin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a yayin jawaninsa ga Maulud Committee a ranar 19th October, 2014 a Husainiyyah Baqiyatullah Zariya.

— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky







12 Rabi'ul Auwal, 1448
25 August, 2026

“Lokacin da muke magana akan haɗin kai, kawo Annabi (S) a matsayin ramzi shi ne babban abu, saboda shi ne kyakkyawan abi...
24/08/2026

“Lokacin da muke magana akan haɗin kai, kawo Annabi (S) a matsayin ramzi shi ne babban abu, saboda shi ne kyakkyawan abin da za a yi koyi da shi domin haɗuwa akan abu guda. Mu haɗu mu ce: waye shugabanmu? Waye jagoranmu? Manzon Rahma (S).”

-Cikin Jawabin Sheikh Zakzaky (H) Na Mauludin Manzon Allah (S) a Abuja ranar 20/09/2024.






24-06-2026.

*Jagora (H) Ya Rufe Taron Daliban IVC, Ya Ƙarfafe Su Neman Ilimi Da Zai Amfani Al'umma*Daga Ofishin Jagora Shaikh Ibrahe...
22/08/2026

*Jagora (H) Ya Rufe Taron Daliban IVC, Ya Ƙarfafe Su Neman Ilimi Da Zai Amfani Al'umma*

Daga Ofishin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

Da safiyar yau Asabar, 22 ga Agusta 2026, Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya rufe taron ɗaliban Firamari da Sakandire na IVC a Abuja, wanda Dandalin Ɗaliban Harkar Musulunci ke shiryawa a duk lokacin hutun yara.

A jawabinsa, ya bayyana taron IVC a matsayin lokaci mai muhimmanci na shirya yara. Ya ce, yayin da a makaranta ana koyar da yara ilimi su san harshe, su iya karatu, rubutu ko zane da sauran su, amma "Idan aka zo IVC, ana ƙoƙari ne a gyara tunaninsa ya zama yana tunani sahihi, ya san addini sahihi, ya fahimce shi sahihi." Ya kara da cewa, “ƙwaƙwalwa tana buƙatar a rayar da ita da tunani mai kyau".

Da yake jan hankalin yaran kan ilimi, ya bayyana ilimi a matsayin abu mai muhimmanci, tare da ƙarfafa su neman ilimi saboda Allah da kuma ilimi mai amfanarwa. Ya ce, “duk karatun da zai amfane ka duniya da lahira, ya kuma amfanar da al’umma, ibada ne.” Ilimin kiwon lafiya ne, noma, kimiyya, sufuri da sauran su, duk ibada ne, sai idan ba don Allah aka nema ba.

A ƙarshen jawabinsa, ya bayyana ilimi a matsayin ɗaya daga cikin dalilan nasarar Iran a yau da tsayuwarta ga kafircin duniya. Ya ƙarfafi yaran da su dage da neman ilimin da zai amfane su da al’umma, tare da samar da mafita ga matsalolin al'ummar.




#𝐅𝐫𝐞𝐞𝐏𝐚𝐥𝐞𝐬𝐭𝐢𝐧𝐞


23/08/2026

Address

Maraba
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sheikh Zakzaky's Gallery posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share