28/05/2026
"Za ka ga waɗansu shafuffuka ba su da wani aiki sai antayo ashar da zage-zage da sauransu, kuma na san har wala-yau maƙiya sun shigo mana da wannan. Da jin wannan, mun san ƙwagilolin maƙiya ne.
Dama can abin da suke ta ƙoƙari shi ne su tabbatar da cewa a ƙasar nan sun haɗa mu rigingimu da juna. Su haɗa mu rigimar kudu da arewa; waɗannan a ce ko ƴan arewa ne, ƴan kudu suna muku kaza, ku kuma ƴan kudu ne, a ce ƴan arewa suna muku kaza. Ƴan kudu su dinga antayowa ƴan arewa zagi na fitar arziki cikin zagin, har da zagin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo (R). Su kuma ƴan arewa su ce ai ku kaza, ku kaza, miyagun maganganu.
Sannan kuma ƴan arewa sai a zo a ce ai ku ma Kirista da Musulmi ne. Su Musulmi su fara cewa Kirista kaza ne, su kira su da waɗansu sunannaki, sannan su ma Kiristan su rama, su kira Musulmi da wasu sunannaki; abin da ake so a yi faɗa. Sannan har wa yau kuma faɗan ƙabilu, a ce wannan ƙabilan kaza, wannan kaza. Wani abin mamaki ma shi ne wanda s**a zo da shi wai wasu suna kiran kansu Hausawa, wai suna faɗa da Fulani wai su ƙabila ne.
Mun san wannan aikin maƙiyanmu ne, wasu ne s**a zo mana da wannan, don a iyakar saninmu Hausa ƙasa ce, kuma ƙasar nan ta haɗa da ƙabilu daban-daban, har da addinai daban-daban. Ko lokacin da su Shehu Usmanu s**a tabbatar da daula Musulma, ba an ce kowa dole sai an mai shi Musulmi ba ne. Akwai waɗanda s**a riƙe addinansu na gargajiya, kuma ba a ce musu dole su bari ba, don ba a tilasta wa mutum dole ya yi addini".
—Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H)
11/Zul-Hijja/1447
28/05/2026