Sheikh Zakzaky's Gallery

Sheikh Zakzaky's Gallery A New Official Page of Sheikh Zakzaky's Gallery Forum of the Islamic Movement In Nigeria

"Za ka ga waɗansu shafuffuka ba su da wani aiki sai antayo ashar da zage-zage da sauransu, kuma na san har wala-yau maƙi...
28/05/2026

"Za ka ga waɗansu shafuffuka ba su da wani aiki sai antayo ashar da zage-zage da sauransu, kuma na san har wala-yau maƙiya sun shigo mana da wannan. Da jin wannan, mun san ƙwagilolin maƙiya ne.

Dama can abin da suke ta ƙoƙari shi ne su tabbatar da cewa a ƙasar nan sun haɗa mu rigingimu da juna. Su haɗa mu rigimar kudu da arewa; waɗannan a ce ko ƴan arewa ne, ƴan kudu suna muku kaza, ku kuma ƴan kudu ne, a ce ƴan arewa suna muku kaza. Ƴan kudu su dinga antayowa ƴan arewa zagi na fitar arziki cikin zagin, har da zagin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo (R). Su kuma ƴan arewa su ce ai ku kaza, ku kaza, miyagun maganganu.

Sannan kuma ƴan arewa sai a zo a ce ai ku ma Kirista da Musulmi ne. Su Musulmi su fara cewa Kirista kaza ne, su kira su da waɗansu sunannaki, sannan su ma Kiristan su rama, su kira Musulmi da wasu sunannaki; abin da ake so a yi faɗa. Sannan har wa yau kuma faɗan ƙabilu, a ce wannan ƙabilan kaza, wannan kaza. Wani abin mamaki ma shi ne wanda s**a zo da shi wai wasu suna kiran kansu Hausawa, wai suna faɗa da Fulani wai su ƙabila ne.

Mun san wannan aikin maƙiyanmu ne, wasu ne s**a zo mana da wannan, don a iyakar saninmu Hausa ƙasa ce, kuma ƙasar nan ta haɗa da ƙabilu daban-daban, har da addinai daban-daban. Ko lokacin da su Shehu Usmanu s**a tabbatar da daula Musulma, ba an ce kowa dole sai an mai shi Musulmi ba ne. Akwai waɗanda s**a riƙe addinansu na gargajiya, kuma ba a ce musu dole su bari ba, don ba a tilasta wa mutum dole ya yi addini".

—Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H)



11/Zul-Hijja/1447
28/05/2026

UpdateSheikh Ibraheem Zakzaky (H) has offered Qurban after observing Eid Adha at his Abuja residence.      10/ZulHijja/1...
27/05/2026

Update

Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) has offered Qurban after observing Eid Adha at his Abuja residence.






10/ZulHijja/1447
27/05/2026

Hausa

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), ya yi layya yau Litini 10 ga Dhul Hijja 1447, wanda yayi daidai da 27/05/2026, a gidansa dake Abuja.






10/ZulHijja/1447
27/05/2026

"Ranar layya, a yayin da mutum yake yanka Rago, to ya halarto da zuciyarsa da tunanin cewa, shi mai sadukarwa ne, a shir...
27/05/2026

"Ranar layya, a yayin da mutum yake yanka Rago, to ya halarto da zuciyarsa da tunanin cewa, shi mai sadukarwa ne, a shirye yake ya yi duk abin da Allah ta'ala ya umurce shi koma menene, Ko ba da ransa ne, ko na ƴa’ƴansa ko dukiyarsa, sai gigarau, ya gigarama Rago wuƙa. Da wannan niyya ɗin, idan ya yi wannan to shi ne ainihin.

Allah yana kallon zuciya ne, kamar yadda Allah (T) yake cewa: "Jinainai na abin yanka da kuke yankawa, da nama na abin da kuke yankawa ba ya zuwa wajen Allah, abin da yake zuwa wajen Allah (taƙawa) ne daga wajenku". Ina taƙawa yake? A zuciya, da wacce niyya ka yi layya?”

-Shaikh Zakzaky (H) jim kaɗan da kammala Sallar Babbar Idi da aka gudanar a muhallin Husainiyyah Bakiyyatullah, Zariya. A ranar Asabar ɗin 10 ga watan Zulhijjah, 1435 (4/10/2014).

's Gallery




10/DhulHijja/1447
27/05/2026

SANARWA:Daga Ofishin Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ  اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُح...
26/05/2026

SANARWA:

Daga Ofishin Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ

وَمَا كَانَ الْمُؤْمِنُونَ لِيَنفِرُواْ كَآفَّةً فَلَوْلاَ نَفَرَ مِن كُلِّ فِرْقَةٍ مِّنْهُمْ طَآئِفَةٌ لِّيَتَفَقَّهُواْ فِي الدِّينِ وَلِيُنذِرُواْ قَوْمَهُمْ إِذَا رَجَعُواْ إِلَيْهِمْ لَعَلَّهُمْ يَحْذَرُونَ.

Muna sanar da ƴan'uwa tashar ABS ta koma sabon frequency:

Eutelsat 16est/Amos17 Frequency 10928/H/30000

Sannan an samar da sabon channel na YouTube:

https://youtube.com/?si=O3OMAak_JQwucQy5

Wassalam






09/DhulHijja/1447
26/05/2026

'LAYYA MU A WURIN MU WAJIBI NE, MATUƘAR KANA DA HALI...'- Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) yace:"Layya mu a wurin mu wajibi n...
26/05/2026

'LAYYA MU A WURIN MU WAJIBI NE, MATUƘAR KANA DA HALI...'

- Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) yace:

"Layya mu a wurin mu wajibi ne, wajibi ne matuƙar kana da hali dole kayi layya, ba sai kaga dama ba. In kana da Rago ko kuɗin sayan Rago to layya ya zama wajibi gareka, to kuma karka ce min ba ka da kuɗin Rago in kana da abin da zai sayi Rago kamar kana da salula (Phone) wanda yake an sashi a kasuwa ya kai dubu talatin alhali kuma na dubu goma ma ya isa buga waya to kana da Rago.

Ko kana da waɗansu tafka tafkan wanduna da ba za ka cutu ba in ka barsu, ko wasu tarkacen da ba zaka cutu ba in ka rabu dasu to kana da hali kenan. Ba wai sai kana da tsaban kuɗi ba, ai kana da abin Kuɗi, saboda haka in dai kana da abin layya to layya ya zama wajibi a gareka."

-Cikin Jawabin Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) A shekarun baya.




26/06/2026

"Azumi ranar Arfa, ranar tara (9) ga wata ga wanda bai je hajji ba, shi aka ce azuminsa yana dai dai da wanda yayi azumi...
25/05/2026

"Azumi ranar Arfa, ranar tara (9) ga wata ga wanda bai je hajji ba, shi aka ce azuminsa yana dai dai da wanda yayi azumin shekara (70) ne a lada. To, duka dai dararen ranakun tara (9) duk ana azumi, ranar goma ga wata kuma na zulhijjah ana jinkirta cin abinci har sai bayan an yi Idi, bayan in mutum zai yi layya sai bayan yayi layya ana so ya fara cin daga abin da ya yanka. Ba a ce masa azumi jinkirta cin abinci ake, dan ranar ba azumi ake ba".

-Cikin Jawabin Jagora Shaikh Zakzaky (H) A shekarun baya.




25/06/2026

“ABIN DA BASU SO SHI NE SU GA MUN TSAYA KYAM A KAN ABIN DA MUKE YI.”“Abin da yake bata musu rai kenan: su ga mun tsaya k...
25/05/2026

“ABIN DA BASU SO SHI NE SU GA MUN TSAYA KYAM A KAN ABIN DA MUKE YI.”

“Abin da yake bata musu rai kenan: su ga mun tsaya kyam a kan abin da muke yi. Su yi ta ihu, su yi ta ihu, amma kar a daka tasu. Har ma wani lokaci nake cewa: ‘Kar ku damu da haushin karnuka.’

“Wannan na sani tun 1980. Wani lokaci nake cewa abin da muke so ga ’yan’uwa shi ne: kada mutum yana tafiya da kai, ya maka baƙar magana, kai kuma ka ce za ka rama. Ka ƙyale shi, ka ci gaba da tafiyarka. Domin misalinsa kamar kare ne da yake haushi. Yanzu idan za ka wuce, sai kare ya maka haushi: wan-wan-wan-wan, sai ka tsaya kai ma ka ce: wan-wan-wan! To, ka zama mene kenan? Wa’iyāzu billāh. Ai sai ka wuce; abin da baya son ka yi kawai, ka yi shi, shi kenan ka huta.”

“Abin da baya so shi ne ka yi abin da kake yi ba tare da ka tsaya kana masa raddi ba. To, mun san mun ɗan musu irin wannan a wannan waƙi’ar. Sun yi tsammanin za a daina abin da ake yi, sai s**a ga ana ta yi ne kawai, ana ta yi ba ƙaƙƙautawa. Ba abin da basu yi ba, amma aka yi biris da su, aka ci gaba da abin da ake yi. Har ma nake cewa: da ace a ƙasar nan, duk wanda aka yi wa wani abu zai yi shiru, to za a ce banda su wane; su idan an musu wani abu, ba a jin tsit. Sun tsaya kyam a kan abin da suke yi.”

— Sheikh Ibrahim Yaqoub Zakzaky (H) Cikin jawabin da ya yi ga ’yan’uwa na Cameroon
09/06/2022

’s Gallery

24/05/2026

SHAHID MUHAMMAD TURI (RH)A tarihin gwagwarmayar Musulunci, akwai mutanen da ba za a taba mantawa da su ba saboda sadauka...
24/05/2026

SHAHID MUHAMMAD TURI (RH)

A tarihin gwagwarmayar Musulunci, akwai mutanen da ba za a taba mantawa da su ba saboda sadaukarwa, biyayya da tsayin daka wajen kare addini. Daya daga cikin irin wadannan jarumai shi ne Shahid Muhammad Mahmud Turi (RH).

Shaikh Turi ya kasance mutum mai tsananin biyayya ga Jagora (H), mai son addini da kishin al’umma. Tun kafin Shahadarsa, an san shi da sha’awar Shahada da kuma kokarin haddace duk wani hadisai da s**a shafi falalar Shahidi.

A lokacin Waki’ar Buhari da akayi a Zaria ta 2015, ya nuna jarumta da sadaukarwa wajen kare Jagora da ‘yan uwa. Duk da tsananin harbe-harbe, ya ki ja da baya. Har ma ya kasance yana karfafa gwiwar ‘yan uwa tare da tunatar da su alkawarin da s**a dauka na kare Jagora da addini.

Kafin Shahadarsa, ya sha fada kan Jagora (H) cewa: “Nafsi bi nafsikumul fidha” Wato: “Rayuwata ta zama fansa ga rayuwarku.”

Shaikh Turi ya kasance mai karamci, gaskiya da kyakkyawar mu’amala da jama’a wanda ba iya yan uwa na hatta al'ummar da yake rayuwa a cikin su sun yi kewarshi tare da shaidar da da ayyukan kirki da mu'amala ta gari. Ya tarbiyyantar da iyalansa cikin addini da ilimi, sannan bai taba amincewa da zalunci ko kwaɗayin wani abin duniya ba.



24/05/2026

Shahadar Imam Muhammad Al-Baqir (Amincin Allah ya tabbata a gare shi) 7 ga Zulhijja. Lokacin da Hisham Ibn Abdul Malik y...
24/05/2026

Shahadar Imam Muhammad Al-Baqir (Amincin Allah ya tabbata a gare shi) 7 ga Zulhijja.

Lokacin da Hisham Ibn Abdul Malik ya karbi mulki, mulkinsa ya koma na ta'addanci da zalunci. Siyasar zalunci da azabtarwa ita ce ta haifar da tawayen su Shahid Zaid ɗan Imam Ali Al-Sajjad (SA) wanda ya yi shahada tare da sahabbansa aka kona gawarsu.

Haka kuma Hisham ya tsananta wa ɗaliban Imam Muhammad Al-Baqir (Amincin Allah ya tabbata a gare shi), duk da haka wadannan matakan zalunci ba su hana yaɗuwar Musulunci da wayar da kan Al'umma akan addini ba. Hisham Ibn Abdulmalik ya bada umarnin a sanya wa Imam Muhammad Al-Baqir (SA) guba wanda ya zama sanadin shahadar sa (S) a tafarkin Allah. Imam yayi shahada yana da shekaru 57.

السلامُ عليكَ يا حجة الله على الخلق أجمعين،

أعظم الله أجورنا وأجوركم بذكرى شهادة الإمام الباقر عليه السلام

's Gallery



07/ZulHijja/1447
24/06/2026

"Muddin Najeriya ta ci gaba da tafiya a wannan tsarin, za ta ci gaba da anfani ga wasu, ba ga ƴan Najeriya ba. Hakan zai...
23/05/2026

"Muddin Najeriya ta ci gaba da tafiya a wannan tsarin, za ta ci gaba da anfani ga wasu, ba ga ƴan Najeriya ba. Hakan zai ci gaba ne har sai lokacin da ƴan Najeriya s**a zauna s**a yanke shawarar neman mafitar da ta dace da tsarin rayuwarsu, ba tsarin da ya dogara da tunanin ƴan mulkin mallaka ba.”

— Sheikh Ibraheem Yaqoub Zakzaky (H) cikin Wani jawabi da ya gabatar a ranar 1 ga Oktoba, 2010



23/05/2026

Shahida Sayyida Fatima yaqub (Goggon kaura) ta kasance yar uwa ce ga Jagoran Harkar Musulunci Sheikh Yaqoub Zakzaky (H),...
23/05/2026

Shahida Sayyida Fatima yaqub (Goggon kaura) ta kasance yar uwa ce ga Jagoran Harkar Musulunci Sheikh Yaqoub Zakzaky (H), ta rayu a duniya tsawon shekaru 60 kafin tsohon Shugaban Ƙasar Najeriya Buhari ya aika sojoji su kashe ta a gidan ta ta hanyar ƙona ta da ran ta.

Ya Allah ka la'anci buhari kamai mummunan kamu da duk Wanda s**a tayashi wannan mummunar aikin.

Ya Allah ka karbi uzurinta ka tayar da ita a matsayin shaheeda ka tashe ta tare da kakanninta Imam Hussain (As)



23/05/2025

Address

Maraba
Abuja

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sheikh Zakzaky's Gallery posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share