12/03/2026
"Idan sun gama da Iran za su koma kan Saudiyya, da sauran ƙasashen Musulmi...".
Wannan shi ne hujjar wasu masu cewa; dole a goyi bayan Iran, a yaƙuƙuwan da take yi da Izraila da Amerka. Don haka suke cewa; -wai- Iran ta zama garkuwa wa ƙasashen Musulmi.
To, wannar magana tana da ma'anoni guda biyu:
1- Idan suna nufin cewa; Izraila da Amerka sun shagaltu da Iran, saboda haka ƙasashen Musulmai sun tsira, saboda ba ta su ake yi ba, to sai in ce: wannan zai iya zama dadai, duk da cewa; ba dole ba ne hakan ya zama sababin ƙin yaƙarsu, saboda mun ga su Izraila da Amerkan, yaƙi ba ya shagaltar da su daga wani yaƙin, shi ya a yanzu ma, Izraila tana kai hare-hare ƙasar Lebanon, a daidai lokacin da take yaƙi da Iran. Kuma haka s**a yi a yaƙin watannin baya, har Houthis na Yemen su ma an kara da su.
2- Idan kuma suna nufin Iran ita ce garkuwa mai kare Musulmai, don haka idan an rusa ta to Musulmai sun rasa ƙasa mai tare musu faɗa, saboda Iran ita ce mai taimakon Muslunci, da taimakon ƴan'uwansu Musulmai, to a wannan sai na ce ba haka ba ne. A Tarihi Iran ba ta taɓa tare wa Musulmai faɗa ba, ko ta karɓa musu faɗa. Misali a kan haka; Iran a kullum suna kasuwanci da matsalar Falasɗinawa, amma Izraila ta yi shekara biyu tana ɓarin wuta a Gaza, tana ruguza yankin, amma Iran ba ta shiga faɗan ba, alhali tana da makamai masu linzami da za ta iya harbawa daga Iran su sauka a Izraila, su yi ɓarna. Amma a yanzu da aka tinkare ta, sai ga shi tana ta harba makamai masu linzami, masu isa har cikin Izraila.
Kuma ka duba ka ga irin ta'addancin da Iran ta yi a ƙasashen Musulmai, tana cikin ƙasashen da s**a taimaki Amerka ta rusa Afganistan.
Ita ta taimaki Amerka ta rusa Iraq, ta mamaye ta.
Ita ta taimaki Rasha ta Asad s**a yi kisan kiyashi wa Musulmai a Syria.
Haka Yemen, da Lebanon.
A yau kuma, ga shi tana ta kai hari a kan ƙasashen Musulmai, musamman ƙasashen yankin Gulf, da Jordan.
To don haka, ta yaya garkuwanka, mai ba ka kariya zai yi maka haka?.
VS