Manuniya Tv

Manuniya Tv Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Manuniya Tv, Abuja.

Shugaban INEC ya bukaci ADC ta dakatar da shirin gudanar da babban taronta na NijeriyaJoash ya nemi jam'iyyar ta dauki d...
03/04/2026

Shugaban INEC ya bukaci ADC ta dakatar da shirin gudanar da babban taronta na Nijeriya

Joash ya nemi jam'iyyar ta dauki darasi ga rikicin jam'iyyun da ya faru a jihohin Zamfara da Filato, wanda ya sabbaba soke nasarar wasu 'yan takarar gwamnoninsu.

A wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise a ranar Juma’a, Amupitan ya ce ci gaba da gudanar da tarukan na ADC na iya haifar da mummunan sak**ako na fuskantar fushin doka.

Me za ku ce?

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gana da dangin waɗanda harin Jos ya shafa. Yayin ziyarar da ya kai jihar Filato domin j...
02/04/2026

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gana da dangin waɗanda harin Jos ya shafa.

Yayin ziyarar da ya kai jihar Filato domin jajanta musu, shugaban ya yi alƙawarin ɗaukar matakan da za su kawo karshen tashe-tashen hankulan da ake fuskanta a jihar.

📸 - Gwamnatin jihar Filato

Shugaba Tinubu ya isa Jos jihar Plateau ziyarar ta'aziyya da jajanta wa al'ummar jihar
02/04/2026

Shugaba Tinubu ya isa Jos jihar Plateau ziyarar ta'aziyya da jajanta wa al'ummar jihar

Kiristocin Jos 1. Gwamnan Jos Kirista ne2. Mataimakin gwamnan Jos kirista ne3. Kwamishinoni 21 duk kiristoci ne4. Darakt...
02/04/2026

Kiristocin Jos

1. Gwamnan Jos Kirista ne

2. Mataimakin gwamnan Jos kirista ne

3. Kwamishinoni 21 duk kiristoci ne

4. Daraktoci 9 a fadin ma'aikatu duk kiristoci ne

5. Masu ba gwamna shawara na musamman mutum (20) acikinsu duk kiristoci ne

6. Acikin hukumomin tsaro guda (8), kaso 99 na jami'an tsaro duk kiristoci ne

7. Shugabannin dukkan hukumomin tsaro kiristoci ne

8. Addinin da ya fi rinjaye kirista ne

DUK DA HAKA KUKE CEWA MUSULMI SUNA KASHE KU. Bana tsammanin akwai wani mutum mai tunani mai hankali wanda zai yarda da wannan zance naku. Shawarata ga Musulmin Jihar Filato ita ce ina ganin lokaci ya yi da za ku tashi ku yi fafutukar kare haƙƙunankamu. Ku shiga siyasa, ku daina wannan tunanin na cewa, "kun bar musu ofisoshin siyasa domin samun zaman lafiya" ku tsaida ɗan takara mafi kyau wanda zai kare rayukanku, domin daga yadda abubuwa ke tafiya, waɗannan mutanen ba za su taɓa barin ku ku huta ba.

- Sun kashe matafiya, amma an yafe musu.

- Sun kashe kansu kuma har yanzu suna ɗora laifin a kanku, suna neman gwamnatinsu ta gurfanar da ku a gaban hukuma, duk da cewa yawancinsu sun shaida cewa ba a san waɗanda s**a aikata laifin ba. Amma idan aka k**a masu laifin kuma aka samu cewa su Kiristoci ne, sai a rufe zancen.

Me ya sa ba sa faɗin komai game da k**a Rev. Father saboda samar wa 'yan ta'adda mak**ai?📌

Me ya faru da ma'ajin cocin da ya sace fastocinsa tare da abokansa? Aka ce musulmi ne 📌

Me ya faru da faston da ya ɗauki hayar mutane don su kashe mahaifin Gwamna?📌

Me ya faru da masu kisan Janar Alkali Ali? 📌

Me ya faru da masu kisan matafiya 26 na Maulud a 2021? 📌

Me ya faru da masu kisan matafiya kan hanyar su ta zuwa daurin aure daga Zariya a 2024? 📌

Me ya faru da wadanda s**a kashe 'yan kasuwa Musulmi 5 da aka kashe a lokacin azumi a shekarar 2026? 📌

Me ya faru da wadanda s**a kashe Musulmi 5 da aka kashe a wani gidan mai?📌

Allah ka kare yan uwan mu Musulmin Jihar Filato da Najeriya 🇳🇬

Umar Abusufyan Yusuf

Yadda mataimakin sakataren APC na Kano ya rasu a Otel Mataimakin sakataren tsare-tsare na jam’iyyar APC a Jihar Kano, Ab...
02/04/2026

Yadda mataimakin sakataren APC na Kano ya rasu a Otel

Mataimakin sakataren tsare-tsare na jam’iyyar APC a Jihar Kano, Abdussalami Ginsau, ya rasu a otel ɗin Chida da ke Utako a Abuja.

Ya rasu ne bayan lalacewar na’urar mahaya ta Otel ɗin, a lokacin da yake ciki.

02/04/2026

AN SAKE KAI WA MALAM HARI

Wannan shine kusan karo na hudu da aka yi yunkurin ha||aka Sheikh Bashir Ahmad Sani Sokoto

Amma wanda ya kawo harin na yau an k**ashi, kuma an mikashi zuwa ga hukuma

Na rasa me Malam Bashir Ahmad Sani Sokoto yayi ake neman ha||aka shi

Muna rokon Allah Ya cigaba da bawa Malam kariya

DSS ta k**a wata mata a Kano da ke safarar alburusai ga ƴan ta'adda a Katsina Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta k**a ...
02/04/2026

DSS ta k**a wata mata a Kano da ke safarar alburusai ga ƴan ta'adda a Katsina

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta k**a wata mata mai shekaru 25 mai suna Nafisa Usman bisa zargin safarar harsasai tsakanin jihohi, inda aka same ta da sabbin harsasai guda 200.

Rahotanni sun ce an cafke ta ne a wata babbar tashar mota a Kano, bayan ta ɓoye harsasan cikin buhunan garri da shinkafa, tana ƙoƙarin jigilar su daga Nasarawa zuwa Kankara a jihar Katsina.

DSS ta bayyana cewa an k**a ta ne bayan samun sahihan bayanan sirri, kuma ta fito daga ƙauyen Zango da ke ƙaramar hukumar Kankara.

A cewar hukumar, wacce ake zargin ta amsa cewa ana kawo mata harsasan daga Lafia, sannan a rarraba su zuwa hannun ‘yanbindiga a dajin Kankara, ciki har da wani da ake kira Mallam Haruna.

Ta kuma ce ta shafe kusan watanni biyu tana wannan sana’a, tare da yin mu’amala da ta kai kusan naira miliyan 5.

Hukumar DSS ta ce za ta gurfanar da wacce ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

Wata kungiya ta mata a jihar Kano ta kaddamar da wani sabon salon sufuri na keken Napep na mata kawai da ake kira "Mata ...
02/04/2026

Wata kungiya ta mata a jihar Kano ta kaddamar da wani sabon salon sufuri na keken Napep na mata kawai da ake kira "Mata Zalla", wanda aka kikira don yi wa mata hidima tare da samar da damar aikin tukin keke ga mata. A karkashin tsarin, mata ne ke tukin kekunan kuma suna daukar fasinjoji mata kawai, al'amarin da kuma ya karfafa tattalin arzikin mata. Mabiya da masoyana, musamman wadanda ke arewacin Najeriya, shin kuna da masaniya game da wannan tsarin mai suna Mata Zalla a Kano? Mene ne ra'ayinku?

Jonathan ya nemi a kafa Kotun Tsarin Mulki don kararrakin zaɓeTsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan ya yi kira da a kaf...
02/04/2026

Jonathan ya nemi a kafa Kotun Tsarin Mulki don kararrakin zaɓe

Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan ya yi kira da a kafa Kotun Tsarin Mulki domin ta rika sauraron kararrakin zaɓe, inda ya soki tsarin matakai uku na yanzu saboda jinkiri da rashin ingancinsa.

Ya bayyana misalin wani tsohon lamari inda aka rushe zaɓen gwamna saboda ƙaramin kuskuren fasaha, yana mai jaddada bukatar tsarin da ya fi sauri kuma mai sauƙi.

Maganar gaskiya sunci amanar addini, kuma ya k**ata hukumomi su ɗauki matakin hukunta suYin hotunan aure acikin masallac...
02/04/2026

Maganar gaskiya sunci amanar addini, kuma ya k**ata hukumomi su ɗauki matakin hukunta su

Yin hotunan aure acikin masallaci, tare da bayyana tsiraici

Idan aka ƙyale wannan, fiye da haka wasu za su aikata watarana.

DA ƊUMI-ƊUMI:🔥 Atiku zai jagoranci taron manema labarai kan janye sahalewar shugabancin ADC daga INECTsohon Mataimakin S...
02/04/2026

DA ƊUMI-ƊUMI:🔥 Atiku zai jagoranci taron manema labarai kan janye sahalewar shugabancin ADC daga INEC

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, zai jagoranci shugabannin ‘yan adawa da sauran manyan masu ruwa da tsaki a harkar siyasa wajen gudanar da taron manema labarai kan batun janye sahalewar shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) daga hannun wani ɓangare na jam’iyyar.

An shirya gudanar da taron ne yau Alhamis, 2 ga Afrilu, 2026, da ƙarfe 1:00 na rana, a Shehu Musa Yar’adua Centre da ke birnin tarayya Abuja.

Rahotanni sun nuna cewa taron na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da taƙaddama kan sahihancin shugabancin ADC, lamarin da ya haddasa ce-ce-ku-ce da zarge-zarge tsakanin ɓangarorin jam’iyyar, musamman bayan matakin da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ɗauka.

Ana sa ran manyan ‘yan siyasa da jagororin jam’iyyun adawa za su halarci taron, inda za a fayyace matsayarsu tare da bayyana matakan da za su ɗauka dangane da wannan rikici.

Wannan mataki na iya ƙara ɗumama siyasar ƙasar nan gabanin babban zaɓen da ke tafe, yayin da rikice-rikicen cikin gida ke ci gaba da girgiza wasu jam’iyyun siyasa.

Address

Abuja
1234

Telephone

+2349134515565

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Manuniya Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to Manuniya Tv:

Share