Nasrul Ilm Hausa CI.

Nasrul Ilm Hausa CI. Assalamu Alaikum!!! WANNAN SHAFIN AN BUDE SHINE DOMIN GUDANAR DA AYYUKAN TIRIQAR TIJJANIYA A KASAR

27/04/2022

Sanarwa daga bakin IMAM SHEIKH SHERIF UMAR ABDELAZIZ RTA.

FASSARAR RUHUL ADAB (5)أعـــوذ باللــه من الشـيطن الرجيــــمبـــــــسم اللـه الرحــمن الرحــــــيماللهـم صل علي أبو الفا...
07/04/2022

FASSARAR RUHUL ADAB (5)

أعـــوذ باللــه من الشـيطن الرجيــــم
بـــــــسم اللـه الرحــمن الرحــــــيم
اللهـم صل علي أبو الفاطـــمة سيدنا محمد رنبز بن عبد الله و علي آله حق قدره و مقداره الـــعظيم

Bayan haka Yan uwa ina muku Barka da wannan lokacin ,K*m kai tsaye zamu Dora daga inda na tsaya a satin daya gabata.

K*ma zamu tashi baiti na 12.

Shehu yaci gaba da cewa ....

12) ولازم الخضور والسكونا
كذا ك خلوة تعين حين
K*ma Ku lazimci natsuwa ta kankan dakai da K*ma natsuwa ta zahiri

Haka na kebancewa yayin karanta lazimin zai taimaka sosai da sosai

13) واطلب مربيا خبيرا ناصحا
كامل عرفان إما صالحا
K*ma ka nemi shehi murabbi Wanda ya kewaye da komai K*ma me nasiha

Wada yake ciki da maarifa K*ma shugaba Salihi.
......
To Yan uwa Anan Akwai Jan hankali sosai Wanda ya kamata kowa ya santa

Lallai dole ne mutum ya ne mawa kansa shehi

Wanda kunga a yanzu ba haka akeyi ba

A yanzu shehi ne yake Neman muridai

Amma ba miridai ne suke zaban shehi da Kansu ba

To sharadi na farko shine kafin ka karbi darika wajibinka ne ka ne mawa kanka shehi

Shine ta hanyar bibiyar shehu nan kafin ka ta'allaka kanka da shi

Ka duba kaga shin ya kewaye da darikar.

Shin ya kewaye da hukunce hukuncenta

Shin yana da saukakawa ko yana tsananta wa muridai da dorawa muridai takalif

Shin yacika da maarifa ko kuwa , Kada kaje ka ci karo da Dan gyara samun SAA ya angizaka rami

Ta hakane zaka gane ya yake ya halayensa suke da dabi'unsa shin yana koyarqa Abu Annabi da shari'ar Annabi ko K*ma ba haka yake ba

Sabida baa bin ka'idar yanda aka shimfida tafiyar

Mina fata Allah ya gyara mana K*ma ya sanya irin wannan fadakarwa domin samarin mu su fahimci ma in aka dosa

To kunga Ashe shehu yana bamu shawara da cewa ba a wajen kowa zamu je mu karbi darika ba , Aa lallai Mi caje mu bincika mu kuma natsuwa kafin zabar shehi.

Domin duk Wanda ka zaba ya zaa shehinka to fa ka daka masa rayuwrka ne gaba daya.

To kuwa kunga dole a natsu a sami direba ko K*ma a afaka a cikin hadari.

To yan uwa Anan nake son in tsaya gobe InshaAllah.

Nasrul Ilm Hausa CI.
Sheikh Sherif Umar ABDEL'aziz RTA.

FASSARAR RUHUL ADAB (4) أعـــوذ باللــه من الشـيطن الرجيــــمبـــــــسم اللـه الرحــمن الرحــــــيماللهـم صل علي أبو الف...
06/04/2022

FASSARAR RUHUL ADAB (4)

أعـــوذ باللــه من الشـيطن الرجيــــم
بـــــــسم اللـه الرحــمن الرحــــــيم
اللهـم صل علي أبو الفاطـــمة سيدنا محمد رنبز بن عبد الله و علي آله حق قدره و مقداره الـــعظيم

Bayan haka Yan uwa insha Allah yau zamu ci gaba a inda muka tsaya a wannan karatu na fassarar Ruhul adab.

Zamu tashi baiti na 8 da izinin Allah

معظما لأهله جميعا
لا سيما الخصة كن مطيعا

Lallai muridi ya zama me girmamawa ne ga ahalin wannan darika

Musamman khassawan cikinta ya zama me biyayya garesu.

Ma'ana wajibi ne muridi ya zama yana girmama duk Yan uwansa Yan wannan darika K*ma musamman manya shehunnan cikinta dole ya zama ya na me girmamasu.

Kunga kenan Anan ma shehu yana mana nuni izuwa ga ladabi da girmama magabata na wannan darika.

9 ) إذا شرعت في أذكار الورد
فلازم الأدب قدر الحد

Idan mutum ya shiga maana ya fara wuridin zikiran da suke cikin wannan darika

To lallai mutum ya lazimci ladabi gwargwadon iyakokin da aka sanya maana sharuddan da aka saka na wuridi.

Kunga Anan ma shehu yana sanar damu cewa ba haka kai tsaye akeyin wuridin ba Aa komai a wannan darika yana da sharadi da ka'idoji.

10 ) تأدب في ظاهر وباطن
به يرقي المرأ للمواطن

Anaso muridi ya yi ladabin a zahiri da K*ma badini

Dayin hakane mutum zai sami tarakin hauhawa kan mukamai na walitta.

Kunga kenan idan babu ladabi mutum Bazai sami tarakin hawa kan wasu mukaman ba.

Kunga dole mu shiga taitayinmu musamman ma matasa da a farka a koma kan ainahin koyarwar wannan darika me albarka.

11) واستحضرن شيخك المربي
كذا شيخهه بدون ريب

K*ma muridi ya dinga halarto shehinsa murabbi

Haka na da halarta shehun shehinka batare da kokwanto ba

Anan akwai bukatar jawabi Abin da ake nufi shine

Duk da dai Wanda yake binmu tin karatun fikhun darika zai San wannan
Amma Sabida sababbi Zamu kara jawabi

Yaa daga ladabin karanta lazimi wannan darika
Halarto shehinka a zuciyarka da shehinsa Har kan shehu tijjani Mafi girma ma Halarto shugaba s.a.w.w.

A zuciya lallai hakan yana karasa muridi natsuwa da koyi wajen ladabi inda ta hakane zai sami saukin samun adadi da tarkki da kuma samun fatahi da zai kara kusanta ma da Allah.

Yan uwana Anan zan cigaba gobe InshaAllah.

Nasrul Ilm Hausa CI.
Sheick Sherif Umar ABDEL'aziz RTA.

FASSARAR RUHUL ADAB (3) أعـــوذ باللــه من الشـيطن الرجيــــمبـــــــسم اللـه الرحــمن الرحــــــيماللهـم صل علي أبو الف...
05/04/2022

FASSARAR RUHUL ADAB (3)

أعـــوذ باللــه من الشـيطن الرجيــــم
بـــــــسم اللـه الرحــمن الرحــــــيم
اللهـم صل علي أبو الفاطـــمة سيدنا محمد رنبز بن عبد الله و علي آله حق قدره و مقداره الـــعظيم

Ƴan uwa Asslam alaikum , kuma zan ɗora a inda aka tsaya a fassara wannan littafi na ruhul adab.

5) فلازموا لازمذي الطريق
بذا ينال الربح بالتحقيق

Ku lazimci lazimin wannan ɗariƙa

Ta hakane mutum zai sami riba (ta kasancewa ɗan tijjaniyya) ta haƙiƙa.

6) فلست في أخذ الطريقة تربح
إلا إذا كنت دواما تصلح

Ba zai yiyu ace daga ka karɓi ɗariƙa ka zama ka sami falalar dake ƙarƙashinta

Sai dai idan ya zama ya dawwama aka kyawawan ɗabi`u da halaye.

7) مكملا شروطه المقررا
مكبدا آدبه المعتبرا

(mutum bazai zama ya dami romon da ake sami a ɗariƙar tijjaniyya ba) sai ya zama me cika duka sharɗɗan ta waɗanda aka tabbatar dasu

K*ma ya zama me cakuɗuwa da ladubbanta waɗanda suke ababan lura ne (idan ka lura da kyau babu wani sharaɗi da ya kaisce wa shari`a).
.........

Ƴan uwa duk wanda yayi nazari akan waɗan nan baitoci na karatun mu nayau

Zai ga cewa lallai wannan ɗariƙa tana da tsari da tsaro
K*ma sharaɗin mutum yace shi ɗan wannan ɗariƙa ne shine lallai ya zama ya cika shariɗɗanta.

K*ma yana tafiya akan ladubbanata, bawai daga yazo ya karɓi ɗariƙa ne zai sami duk abinda aƙa faɗa cewa ɗan wannan ɗariƙa zai samuba

Sai lallai ya cika sharuɗɗan ta wannan ɗariƙa da ladubbanta

Ƴan uwa kuyi nazari da kanku kan abinda yake faruwa a wannan zamani ,zaku bawa kanku da kanku amsa.

Anan zan tsaya zan ci gaba gobe InshaAllah.

Nasrul Ilm Hausa CI

Sheikh Sherif Umar ABDEL'aziz RTA.

FASSARAR RUHUL ADAB (2)أعـــوذ باللــه من الشـيطن الرجيــــمبـــــــسم اللـه الرحــمن الرحــــــيماللهـم صل علي أبو الفا...
03/04/2022

FASSARAR RUHUL ADAB (2)

أعـــوذ باللــه من الشـيطن الرجيــــم
بـــــــسم اللـه الرحــمن الرحــــــيم
اللهـم صل علي أبو الفاطـــمة سيدنا محمد رنبز بن عبد الله و علي آله حق قدره و مقداره الـــعظيم

Bayan haka ƴan uwa Assalam alaikum
K*ma kai tsaye zamu ɗora a inda muka tsaya a fassarar littafin ruhul adab.

٤) طريق مخض الفضل والرضوان
أسس بالسنة والفر قان
Shehu yace

Ita wannan ɗariƙa da nake kiranku zuwa riƙo da ita , to hanya ce ta tsantsar falala da samun yardar Allah

Wadda aka ginata da sunna (wato hadisai kenan) da kuma Alƙur`ani.

Ya ku ƴan uwa kowa ya kawo hankalinsa nan yaga wani muhimmin saƙo daga shehu
Wanda wannan baiti raddine kai tsaye ga masu cewa su mutanen shehu ne ko kuma su ƴan ɗariƙa ne
Amma kuma ayyukansu sun saɓa dana alƙur`ani da kuma sunnar ma`aiki.

To shehu ya faɗa a bayyane cewa shi abinda yake kira da ayi riƙo dashi shine Tijjaniyya kuma tijjaniyar da yake kira zuwa gareta an ginata ne bisa sunnar shugaba s.a.w.w da kuma alƙur`ani.

Lallai dolene mu lura da kyau cewa duk wanda yake aikata wani aiki wanda ya saɓa da sunna da ƙur`ani to kai tsaye waɗannan ba mutanen shehu bane kuma ba ƴan tijjaniyya bane.

Wajibine dukkanmu mu ɗauki nauyin yaɗawa da bayyanawa bakin iyawar mu domin lallai muna cikin wani zamani da muka sami ƴan sojan gona da suke cewa suma wai ƴan tijjaniyya ne.

Allah ya shiryar damu hanya ta dai dai
Anan zan tsaya zan ci gaba gobe InshaAllah.

Nasrul Ilm Hausa CI.

Sheikh Sherif Umar ABDEL'aziz RTA.

FASSARAR LITAFFIN RUHUL ADAB.  (1)أعـــوذ باللــه من الشـيطن الرجيـــمبـــــــسم اللـه الرحــمن الرحــــــيماللهـم صل عل...
02/04/2022

FASSARAR LITAFFIN RUHUL ADAB. (1)

أعـــوذ باللــه من الشـيطن الرجيـــم
بـــــــسم اللـه الرحــمن الرحــــــيم
اللهـم صل علي أبو الفاطـــمة سيدنا محمد رنبز بن عبد الله و علي آله حق قدره و مقداره الـــعظيم

Bayan haka ƴan uwa ina muku barka da wannan lokaci kuma yai ɗinnan yanzunnan zamu fara fassara littafin shehu na ruhul adab.

Wanda akace shehu ya wallafashi ne a lokacin da yake ɗan shekara 21.

Kai tsaye Abinda wannan suna na wannan littafi yake nufi na RUHUL ADAB shine TARBIYYAR RUHI.

Idan muka nutsu muka yi duba a cikin wannan saƙo da shehu ya aiko mana to na tabbata duka ruhikanmi zasu sami cikakken saiti.

Muna fatan Allah yasa muyi anfani da abinda zamuji a zahiri da baɗini.

Bayan Ta`awizi da Basmala shehu ya fara da .........

يقول إبراهيم نجل الحاج
عبد الإله بدرنا الوهاج

IBRAHIM ƊAN ALHAJI ABDULLAHI

WANDA YA ZAMA WANI WATA NAMU ME TSANANIN HASKE YANA CEWA.

من بعد بسم الله ثم الحمد
لله ذي الطول العظيم المجد

BAYAN FARAWA DA SUNAN ALLAH DA KUMA GODIYA

GA ALLAH WANNAN DA YAKE MA`ABOCIN BAIWA ME YALWA KUMA MA`ABOCIN ƊAUKAKAR DARAJA.

نصيحة مني الي إخواني
فلتمسكوا طريقة التجاني

Sababin wannan rubutu nawa shine
WATA NASIHA CE DAGA GARENI ZUWA GA ƳAN UWANA

LALLAI KO WANNEN KU YAYI RIƘO DA ƊARIƘAR SHEHU TIJJANI R.T.A.

Wannan shinfiɗa da shehu yayi ya nuna kwarewa irinta marubuta , Idan kun lura shehu ya dunkule saƙon da yake so ya isar tin baiyi ma wani nisaba a cikin wannan rubutu.

Bayan basmala da salati kawai sai shehu yake kai tsaye kan maudu`in da zai tauna a wannan littafi.

InshaAllah zamu ci gaba.

Nasrul Ilm Hausa CI

Sheick Sherif Umar ABDEL'aziz RTA.

Maulana Imam Sheikh Sherif Umar AbdelAziz rta.Yana yiwa daukacin jamaar Musulmai barka da zuwan wannan wata na Ramadan l...
01/04/2022

Maulana Imam Sheikh Sherif Umar AbdelAziz rta.

Yana yiwa daukacin jamaar Musulmai barka da zuwan wannan wata na Ramadan lafiya.
Allah yasa mu fara shi lafiya mu qare lafiya.
Allah ya bamu dukkanin abubuwan da Allah ke bayarwa acikin watan mai Albarka.

Amin summa Amin.
NASRUL ILMI HAUSA 🇨🇮

Alhamdulillah Alhamdulillah Maulana Sheikh Sherif Umar AbdelAziz rta tareda Yayansa Sheikh Sherif Aminu sun sauka lafiya...
30/03/2022

Alhamdulillah Alhamdulillah
Maulana Sheikh Sherif Umar AbdelAziz rta tareda Yayansa Sheikh Sherif Aminu sun sauka lafiya kuma cikin koshin lafiya,

Alhamdulillah 😍 😍

Inna lillahi wa'ina illaihi rajuun. Allah Yayiwa Sheikh Imam Ali Alfalaki kasar Ghana 🇬🇭 garin Takoradi Rasuwa muna mika...
29/03/2022

Inna lillahi wa'ina illaihi rajuun.

Allah Yayiwa Sheikh Imam Ali Alfalaki kasar Ghana 🇬🇭 garin Takoradi Rasuwa muna mika sakon ta'aziyar mu,

Allah ya jadadda rahama gareshi. Ameeen

Khalifan SHEHU IBRAHIM INAYSS RTA, anan Kasar Cote D'Ivoire. Sheikh Sherif Umar Abdulaziz rta.
26/03/2022

Khalifan SHEHU IBRAHIM INAYSS RTA, anan Kasar Cote D'Ivoire.
Sheikh Sherif Umar Abdulaziz rta.

Imam Sheikh Sherif Umar AbdelAziz rta. Tareda Yayansa, Sherif Aminu Cikin wani masallaci a kasar Abu Dhabi Juma'a mubara...
25/03/2022

Imam Sheikh Sherif Umar AbdelAziz rta.
Tareda Yayansa, Sherif Aminu Cikin wani masallaci a kasar Abu Dhabi

Juma'a mubarak

Adresse

Abidjan

Site Web

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Nasrul Ilm Hausa CI. publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Partager