Bari Haske ta Haskaka-daga Apostle Caleb Yakubu

Bari Haske ta Haskaka-daga Apostle Caleb Yakubu Informations de contact, plan et itinéraire, formulaire de contact, heures d'ouverture, services, évaluations, photos, vidéos et annonces de Bari Haske ta Haskaka-daga Apostle Caleb Yakubu, Organisation religieuse, Cotonou.

Afrilu 18, 2026YESU YANA KIRA!Ina kira gare ku, ya ku mutane, muryata kuwa ga ƴan adam ce. Karin Magana 8:4Kada ku yi wa...
18/04/2026

Afrilu 18, 2026

YESU YANA KIRA!
Ina kira gare ku, ya ku mutane, muryata kuwa ga ƴan adam ce. Karin Magana 8:4

Kada ku yi watsi da kiran Allah. Ji yana kiran ku, ku amsa. Ishaya ya ji muryar Ubangiji yana kira, Wa zan aiko, wa zai tafi domin mu? Ishaya ya ce, Ubangiji ga ni, aike ni. Shawulu mutumin Tarsus, yana kan hanyar sa ta zuwa Dimashƙu, ya ji muryar Ubangiji, Saul! Saul! Me ya sa kuke tsananta mini? Ya ce, Wanene kai Ubangiji? Kuma me kuke so in yi? Adamu da Hauwa'u sun ji muryar Ubangiji yana kira a gonar, sai s**a ɓuya. Kada ku ɓuya ga Allah, kada ku yi watsi da kiransa. Sai ku amsa yanzu. Kun dade kuna gudu daga Yesu Kristi. Me kuke so kuyi da rayuwar ku? Ta yaya kuke son ku karishe rayuwar ku? A gare ku, Allah yana kira, muryarsa ga dukan ƴan adam ce. Ina addu'a a gare ku, ba za ku yi watsi da kiran Allah a yau ba, za ku amsa masa kuma zai nuna muku kansa kuma ya albarkace ku a cikin sunar Yesu Kristi. Amin

KU FURTA: Uba! ka yi Mani jinkai da watsi da kiran ka, da boye maka, ka gafarta mani ya ubangiji, na amsa maka yanzu. Amin

SANARWA: kunnuwana suna sauraronka, ya Ubangiji, idanuna suna gare ka ya Ubangiji, ga ni, ka yi magana, gama bawanka yana ji. Amin

ADDU'A: Na gode don jinƙanka, ba zan ƙara yin watsi da kiranka ta ruhunka ba, ta wurin maganarka da addu'o'inka. Zan amsa kuma in yi aiki bisa ga maganarka cikin sunan Yesu. Amin

KARIN LITTAFI: Ishaya 6:1-10, Ayukan Manzanni 9:1-16, 1 Sama’ila 3:1-21, Farawa 3:8-13

8 APRIL 2026INA KUKE GINA RAYUKAN KU?Hakika, duk Wanda ya ji magana na, Kuna Yana yin ta, Yana kamar da Mutum mai hikima...
08/04/2026

8 APRIL 2026

INA KUKE GINA RAYUKAN KU?
Hakika, duk Wanda ya ji magana na, Kuna Yana yin ta, Yana kamar da Mutum mai hikima Wanda ya Gina gidan sa a Kain dutse. Matta 7:24

Karatun litafi Mai tsarki ko Kuma Jin wa'azin Ubangiji Allah, babu biyayya Bata da anfani sai kun aikata ta. biyayya da maganar Ubangiji Allah ne kadai takan kawo albarku da Rai da ke cikin ta. A kain me kuke Gina rayukan Ku? Ko gidajen ku? Kada ku Gina rayukan Ku da bangaskiyar ku a Kain arzikin ku, ko malakar ku, ko iyali, da sauran su. Idan guguwan rayuwa ta zo, duk ababai Nan zata ta rushe ta shude ta bar ku da asara. Ku Gina rayukan Ku da bangaskiyar ku cikin maganar Allah a kulayomi. Kuna karatun ta, da Jin wa'azi, da nazarin ta, da biyayya da ita a kowace yeneyi Babu fasawa cikin Yesu Kristi. Hakanan, Ko iska, da guguwan rayuwa ta zo, ba za ku yi asara ba a cikin sunar yesu. Ubangiji Allah, ta wurin ikon ruhu sa ya sa Ku ginu cikin maganar sa ta wurin biyayya da shi a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceton mu. Amin

KA FURTA: Ya Ubangiji, yafe Ni inda ba in yi cikake biyayya da maganar ka ba,ko Kuma Ina dogara da kayan duniya. Amin

KA CE: Na karbi alherin ka ya Ubangiji, in Yi biyayya da maganar ka kullum, in Gina rayuwa na a Kain dutsen sihiyona. Amin

ADDU'A: Ya Ubangiji Allah, nagode da jinkai'n ka, Gina Mani rayuwa na cikin maganar ka da ruhun ka, yayin da nayi biyayya da kai a cikin sunan Yesu Kristi Mai ceto. Amin

KARIN AYOYI: Matta 7:24-27, Matta 6:19-35, Luka 18:18-30

19 MARCH 2026YESU NA KIRA!A gare ku, ya mutane, Ina Kira, Kuma muriya ta zuwa ga Dan Adam. Misalai 8:4Ubangiji Allah na ...
19/03/2026

19 MARCH 2026

YESU NA KIRA!
A gare ku, ya mutane, Ina Kira, Kuma muriya ta zuwa ga Dan Adam. Misalai 8:4

Ubangiji Allah na Kira. Ku amsa kirar sa. Ishaya ya ji kirar Ubangiji Allah na cewa, wa za mu aiki? Wa za ya je Mana? Sai ya amsa, gani Nan ya Ubangiji Allah, aike Ni. Shaullu na Tarsus, ya ji kirar Ubangiji sa'anda Yana hanyar zuwa Damascus na cewa, shaullu! Shaullu! Me yasa kake kisa na? Shaullu ya amsa, waye Kai ya Ubangiji? Me Kuma Keke so da Ni? Adamu da Hawa'u sun ji kirar Ubangiji sa'anda Ya ziyarce su a lambu Eden, sai s**a boya daga muriyar da fuskar Ubangiji. Kada Ku buya daga fuskar Ubangiji, kada ku taurara daga kirar sa. Ku amsa Masa. Shi Mai jinkai ne. Zaya yafe maku, ya sake KU, ya kuma Yi anfani da KU bisa misali. Na Yi maku addu'a, ba zaku ki Jin kirar sa ba, ko guji fuskar sa. Zaku amsa Masa, Kuma zaya Maya's da ku babban makamin sa da abun mamaki ga duniya a cikin sunar Yesu Almasihu Mai ceton mu. Amin.

KA FURTA: Ya Ubangiji Allah, ka my Mani jinkai kira da kake yi Mani Kuma na taurara da Kuma gudun fuskar ka da na ke yi. Amin.

KA CE: Ya Ubangiji Allah, yau na and kirar ka, yi magana da Ni, nuna Mani fuskar ka. Amin.

ADDU'A, Ya Ubangiji nagode domin kana Ji na, da jinkai da kake Yi Mani kullum. Taimaka Mani in yi biyayya da muriyar ka, yayin da na amsa ta ikon ruhu ka Mai tsarki a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceto. Amin

KARIN AYOYI: lshaya 6:1-10, Ayukan M. 9:1-16, 1 Samaila 3:1-21, Farawa 3:8-12

12 Mars 2026KU DUBA RAYUWAN SUZa ku San su ta wurin Yaya itacen... Matta 7:16Abokai tafiya, na iya Gina ku ko kuma su ru...
12/03/2026

12 Mars 2026

KU DUBA RAYUWAN SU
Za ku San su ta wurin Yaya itacen... Matta 7:16

Abokai tafiya, na iya Gina ku ko kuma su rusa ku. Ku yi hankali da wadanda kuke Kira abokanai rayukan Ku. Ku duba rayuwan su, inda suke zuwa, inda suke Zama, ababai da suke Fadi, shawarar da suke bayar, meme tushin ganewa da hikimar su da ke Gina su, shin Ubangiji Allah ne? Litafin Zabura 1:1 ta ce, Mai albarka ne wanda ba ya anfani da shawarma mugu, da Kuma tsayawa a hanyar masu Zunubi, da zama da magulmata. Rabuwa da irin wadannan mutanin kadai albarka ce, belle Kuna kaunar maganar Ubangiji. In Kuna ciki na, Kuma kalma ta na cikin ku, za ku ribabanya Yaya itace masu Yawa Yahaya 15:5. Ku rabu da abokanai da rayukan su baya gamshe Ubangiji ba. Ku hada Kainku da kalmar Ubangiji da mabiyin sa. Albarkun ku, da wadata, da ceton ku, da girma cikin rohaniya da ta jiki,ya danganta da mutane,ko abokanai da kuke hada Kai da su. Ubangiji Allah ya raba ku da mugayen abokanai,ya Kuma ajiye ku cikin sa da kalmar sa a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceton mu. Amin

KA FURTA: Yafe Ni ya Ubangiji, ka taimaka mani in rabu da abokanai da Basu gamshe ka ba. Amin.

KA CE: Yau na rabu da duk abokantaka da abokanai da ba su gamshe Ubangiji Allah na ba. Amin

ADDU'A: Ya Ubangiji, nagode domin jinkai'n ka,abokina na gaskiya Kai ne da kalmar ka. Yayin da Ina cikin ka Kai Kuma a ciki na Bari haske na ta haskakka,albarku,da wadata ta sauko Mani a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceto. Amin.

KARIN AYOYI: Matta 7:15-20, Zabura 1:1-6, Yahaya 15:1-16, 1 korintiyawa15:33

11 MARCH 2026ALBARKU DOMIN KUAlbarkace, ya Ubangiji, arzikin shi da aikin hannuwan sa, ka yake duk Wanda suke tayar Masa...
11/03/2026

11 MARCH 2026

ALBARKU DOMIN KU
Albarkace, ya Ubangiji, arzikin shi da aikin hannuwan sa, ka yake duk Wanda suke tayar Masa da Kuma nuna masa kiyayya, kada su sake tasowa. Deutronomey 33:1

Rayuwa mara albarka, rayuwa ne Mai wuya da azarbar. Shi ya sa tun daga farko, ubangiji ya albarkace halitatun sa. Kuma, duk lokacin da an furta albarka komai ya kan Zama da sauki da Kuma kyau. Da Ubangiji ya albarkace halitatun, ya ce Masu, ku ribabanya, ku yadu.. Farawa 1:1-28, tun lokacin, halitatu suna bada ya'ya iri ta kainsu, sun Kuma yadu. Bari albarkun Ubangiji ta bayana a dukan yeneyi rayuwa ku. Ta wurin kalmar Ubangiji a yau, Ubangiji Allah ya albarkace arzikin ku da aikin hannuwan ku, ya Kuma take duk Wanda ya tayar maku da ma kiyin ku, ba zasu Kuma taso maku ba a cikin sunar Yesu Kristi. Salama da wadata CE rayuwar ku a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceton mu. Amin

KA FURTA: nagode ya Ubangiji domin albarkun ka a rayuwa na da dukan yeneyi na. Amin

KA CE: Na karbi albarkun ka ya ubangiji yau da kullum, harabada. Amin

ADDU'A: Karbi yabo na da daukakka Domin ababai masu kyau da kake Yi Mani, da albarkun ka a kain rayuwa na. Nagode a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceto. Amin.

KARIN AYOYI: Deutronomey 33:1-29, farawa 1:28, Matta 5:1-12, Deutronomey 28:1-29

10 MARCH 2026SAI DAI KUN GASKANTADa haka ne Kuma Kuka Sami ceto, in Kun hadace wa'azin da na Yi maku, sai dai Kun gaskan...
10/03/2026

10 MARCH 2026

SAI DAI KUN GASKANTA
Da haka ne Kuma Kuka Sami ceto, in Kun hadace wa'azin da na Yi maku, sai dai Kun gaskanta, zata Zama banza. 1 korintiyawa 15:2

Hadace litafi Mai tsarki tana da kyau, ko hadace wa'azin da aka koyas daga litafi Mai tsarki. Amma in ba Ku gaskanta da kalmar Ubangiji ba, ta zama banza. Litafi Mai tsarki ta gaya Mana, Ibrahim ya gaskanta, an kirga shi Mai adalci. Alisabatu ta cewa mariyama, Mai albarka ce ke, da Kika gaskanta, Gama za a aikata ababai da aka gaya maki. Yesu Kristi da kainsa ya ce, in ka gaskanta komai Mai yiwuwa ne. Ubangiji ba zaya iya yin maku komai ba domin Kun hadace litafi Mai tsarki ba, sai dai Kun gaskanta da kalmar sa. Na Yi maku addu'a, domin Kun gaskanta Bari Ubangiji ya albarkace ku, ya yi amsa addu'oyin ku, ya Kuma bayana kainsa a gare ku ta wurin ruhu Mai tsarki da ikon kalmar sa a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceton mu. Amin

CONFESSION: Ya Ubangiji yafe in da na hadace kalmar Amma bangaskiya na ta kasa, taimaka wa bangaskiya na a cikin sunar Yesu Kristi. Amin

KA CE: Ya Ubangiji na gaskanta da Kai,da kalmar ka, da anabi da ka aiko Domina, na Kuma karbi albarku da amsoshin addu'oyi na a cikin sunar Yesu Kristi. Amin.

ADDU'A: Ya Ubangiji, nagode domin jinkai'n ka, karfafa bangaskiya na kullum ta wurin kalmar ka da Kuma ruhun Mai tsarki a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceto. Amin.

KARIN AYOYI: Luka 8:40-56, Markus 9:14-29, Matta 9:27-31

8 Mars 2026 GUNAGUNI!Kada kuma ku yi gunaguni kamar yadda waɗansunsu s**a yi gunaguni, masu hallakarwa s**a hallaka su. ...
08/03/2026

8 Mars 2026

GUNAGUNI!
Kada kuma ku yi gunaguni kamar yadda waɗansunsu s**a yi gunaguni, masu hallakarwa s**a hallaka su. 1 Korinthiyawa 10:10

Yin gunaguni babban zunubi ne a gaban ubangiji. Isra’ilawa sun yi gunaguni ga Allah a cikin jeji saboda bukatunsu. Allah ya biya musu bukatunsu amma sun sami ukuba. Wasu daga cikinsu sun mutu, da yawa ba su ga Ƙasar alkawari ba saboda zunubin gunaguni. Har a yau, mutane da yawa har yanzu suna yin wannan zunubi a cikin zukatansu har ma ga Ubangiji. Allah baya kaunar gunaguni, amma yana do a tambaye sa bukatun a cikin addu'a. Kada ku ba da sarari a cikin zuciyar ku don gunaguni da gunagunai. Kada ku kula da kome, sai dai ta wurin addu'a da roƙo tare da godiya, ku sanar da Allah roƙonku. A viking sunar yesu, kun 'yantu yanzu daga kowane nau'yi da wahala da ke cikin zuciyarku. Kun rabu da gunaguni da gunaguni cikin sunan Yesu. Ubangiji zai biya muku dukan bukatun ku bisa ga wadatarsa cikin ɗaukaka ta wurin Almasihu Yesu. Amin

YARDA: Uba, ka yafe ni inda na yi gunaguni da gunagunai da masu ruguzawa da halaka sun zo mini. Ka yi mani jinkai ya Ubangiji.

SANARWA: na kwance kaina daga kowane nauyi da damuwa a cikin zuciyata wanda ya sa ni gunaguni da gunaguni. Na sami 'yanci yanzu cikin sunan Yesu mai girma.

ADDU'A: Ubangiji, yanzu na sami salama da ta'aziyyata saboda jinƙanka, ka sani za ka biya mini bukatuna da wahalata cikin wadata da ɗaukakar Almasihu Yesu. Amin

KARIN LITTAFI: Fitowa 16:1-36, Fitowa 17:1-7 Filibiyawa 4:6-16, 1 Korinthiyawa 10:1-11

6 March 2025RAYUWAR MUTUM Ya kuma ce musu, “Ku kula fa, ku yi nesa da kowane irin kwaɗayi, don yawan kaya wadata ba shi ...
06/03/2026

6 March 2025

RAYUWAR MUTUM
Ya kuma ce musu, “Ku kula fa, ku yi nesa da kowane irin kwaɗayi, don yawan kaya wadata ba shi ne rayuwa ba. Luka 12:15

Yawancin mutane, suna gani rayuwa shine a Yi arziki da wadata, a ji Dadi da Kuma tare-tare kayan duniya. Ko da shike suna da kyau Kuma Ubangiji Yana so mu more su mu Kuma ji Dadi. Amma, Ubangiji baya so mu damre rayukan mu ga kayan duniya da Kuka Tare. Baya so domin an Sami abinda ake so, KU manta da shi aki zumunta da shi da yanwa cikin Kristi, ana Ababai da aka gan dama. Amma a cigaba cikin zumunta da uba da ya'yan sa, ana taimaka wa yan'uwa da Basu da shi da kuma yin bishara da ababai da ya albarkace mu da shi. Kada mu dogara da arziki da wadata da muka tare. Mu dogara ga Ubangiji Allah kadai. Me zai anfane mu, in mun malaki duniya duka, Amma mu Rasa rain mu? Ceton rayukan mu yafi dukan komai. Ba mu zo duniya da komai ba, ba za mu Kuma koma da komai ba. Ba za mu dogara da arziki da wadata da muka Tara ba, Amma za mu dogara ga Ubangiji Allah da sunar sa kadai a cikin sunar Yesu Kristi harabada. Amin

KA FURTA: Yafe Ni ya Ubangiji, duk in na dogara ga kaina, ko mutum, da arziki ko wadata da na tare. Amin

KA CE: Ni na dogara ga Ubangiji Allah na, ba Zan sa bege na ga wani ba ko yawan arziki da wadata ba. Amin

ADDU'A: Ya Ubangiji Allah, nagode domin ceton Raina, dogara na da bege a kainka ne, da kalmar ka, da Kuma ikon ruhu ka. Zan Yi anfani da naiwa da ka bani, da arziki da wadata in bauta Maka da Kuma nuna wa mutane kaunar ka ta wurin taimoko da bishara a cikin sunan Yesu Kristi Mai ceto. Amin.

KARIN AYOYI: Luka 12:13-21, Matta 6:33, mark8:36-38, 1tim6:7

19 FEBRILU 2026YAKE GOLIYA'R KUKuma za' a Yi, wa mutanin Nan da ya kashe shi, sarki zaya albarkace shi da arziki Mai yaw...
19/02/2026

19 FEBRILU 2026

YAKE GOLIYA'R KU
Kuma za' a Yi, wa mutanin Nan da ya kashe shi, sarki zaya albarkace shi da arziki Mai yawa gaskiye, Kuma ya bashi diyar sa ya aura, gidan babban say kuma, ba za su sake biyan haraji a isra'ila ba. 1 Samaila 17:25

Dauda ya yake Goliya, ba don daukakkar Ubangiji kawai ba, ko Kuma cire kunya a Kain sojojin isra'ila ba. Amma, ya yake Goliya domin akwai daukakka Domin sa da gidan Babban sa. Ko da shike, Babban sa baya ganin sa kamar dan'sa na anihi. Kuma Anna nuna masa kiyayya a fili. Ababai da kuke fuskanta a kulayomi in ku fito, ba soboda Kainku kawai ba ne. Amma, Soboda ya'yan ku ne, da gidajen da Kuka fito da kasar ku. Ko da shike ba su kaunace ku ba. Kada KU raunana, kada ku damu. Ba su San cewa Ubangiji Allah na tare da Ku ba. Ku fuskanci Goliya'r Nan kawai a cikin sunar Yesu Kristi. Yau za ku cire Kain sa, Kuma dukan mutane da masu nuna maku kiyayya zasu gan ikon Ubangiji su Kuma bashi daukakka. Za a albarkace, a daukakka ku domin abin da Ubangiji ya yi ta hannun ku. Ubangiji Allah shi albarkace ku da arziki Mai yawan gaskiye soboda Ku da gidajen ku a cikin sunar Yesu kristi mai ceton mu. Amin

KA FURTA: Ya Ubangiji nagode domin ka sa Mani Kain golia nan a hannun na. Bari dukan mutane su gani su Kuma daukakka ka. Amin

KA CE: Ya Kai Goliyar rayuwa na da na gida na har da kasa na, yau a cikin sunar Yesu Kristi na yenke kainka. Amin.

ADDU'A: Ya Ubangiji Allah, girma ta tabbata gare ka, ta wurin ikon ka ne na yi nasara da dukan komai. Na karbi yanci na da albarku na a cikin sunar Yesu Kristi mai ceto. Amin

KARIN AYOYI: 1 Samaila 17:1-58, Farawa 11:1-12, 41:1-57,42:1-34, zabura 118:22

4 FEBRILU 2026BA ZAKU SHA KUNYA BASu Wanda suke kiyayyar ku, za su Yi kayan kunya Kuma wurin zaman masu mugunta za a rus...
04/02/2026

4 FEBRILU 2026

BA ZAKU SHA KUNYA BA
Su Wanda suke kiyayyar ku, za su Yi kayan kunya Kuma wurin zaman masu mugunta za a rusa. Ayuba 8:22

Duniya Nan akwai mugunta da kiyayya. Wannan ba abun mamaki ba ne domin Yesu Kristi ya gaya Mana cewa, mu ba na duniya ba ne. Kuma za' a nuna mana kiyayya soboda shi. Mu kamar tumaki ne a stakanin karnukar jeji. Kada ku ji storon su, domin Yesu ya bamu nasara kan duniya. Wanda ke cikin mu yafi Wanda ke a cikin duniya. Hallelujah! Ku saurare Ni! Duk masu nuna maku kiyayya, za su Yi kayan kunya. Duk wurin zaman masu mugunta ko wata taruwar mugunta a kainku, Ubangiji Allah zaya rusa su a cikin sunar Yesu almasihu. Salama a gare ku. Amin

KA FURTA: Ya Ubangiji nagode domin ta wurin ikon ka, ba Zan Sha kunya ba, ko Fadi cikin hannun masu mugunta. Amin.

KA CE: Ya Ubangiji Allah, duk masu nuna Mani kiyayya, Bari kunya ta sauko masu, duk wurin zaman masu mugunta, da taruwan su a Kai na rusa su yanzun a cikin sunar Yesu Kristi. Amin

ADDU'A: Nagode, ya Ubangiji Allah domin kana tare da Ni. Nasara nawa ne cikin kowace yeneyi domin Kai dake ciki na kafi Wanda ke duniya a cikin sunar Yesu Kristi mai ceto. Amin.

KARIN AYOYI: Ishaya 41:11-15, Matta 10:16-42, 1 Yahaya 4:1-4,

Adresse

Cotonou

Téléphone

+22990005773

Site Web

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Bari Haske ta Haskaka-daga Apostle Caleb Yakubu publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Partager