Bari Haske ta Haskaka-daga Apostle Caleb Yakubu

Bari Haske ta Haskaka-daga Apostle Caleb Yakubu Informations de contact, plan et itinéraire, formulaire de contact, heures d'ouverture, services, évaluations, photos, vidéos et annonces de Bari Haske ta Haskaka-daga Apostle Caleb Yakubu, Organisation religieuse, Cotonou.

30 YULI 2026AKWAI ZAKIMai kiwiya ya kan ce, akwai zaki a waje. Za a kashe ni a kan tituna. Karin Magana 22:13Mai kiwiya ...
30/07/2026

30 YULI 2026

AKWAI ZAKI
Mai kiwiya ya kan ce, akwai zaki a waje. Za a kashe ni a kan tituna. Karin Magana 22:13

Mai kiwiya ba zai daina bayar da dalilin rashin fita aiki ba. Akwai wani abu da ba daidai ba a wurin aikin. Ba irin aikin da yake so ba ne ko kuma suna biyansa kudin da bai cancanci hakan ba, ai babu aika ko wanda zai taimaka masa ya sami aiki. Bai san cewa shi mai kiwiya ne Kuma talauci na Akain sa. Kada ku raina karamar aikin nan. Kada ku Reina ta. Ka tuna kai mai nasara ne. Kada ka reina ƙaramin farkonka wadatar ku. Ku fara daga wannan ƙaramin wuri ku ga yadda Ubangiji zai albarkaci ƙaramin kuma ya buɗe maku ƙarin ƙofofin alheri. Ian maku Addua, Ubangiji ya sa ayyukan hannuwanka su yi albarka su kuma yawaita. Za su ɗaukaka ku da yawanai alheri, wadata kuma zata zo maku. Arziki naku ne cikin sunan Yesu Kristi mai cetonmu. Amin

IKRAƊI: Ya Ubangiji, ka gafarta mini inda na raina ƙananan farawa, ka ba da uzuri don rashin zuwa aiki. Amin

SANARWA: Zan fita in yi aiki, domin albarkar Ubangiji tana tare da ni don in sami wadata. Tsarki ya tabbata ga Allah! Amin

ADDU'A: Uba, na gode domin layi zai faɗi a gare ni a wurare masu daɗi. Talauci ba nawa ba ne. Zan yi aiki kuma in sami albarka cikin sunan Yesu mai ceto. Amin

ƘARIN NASSOSHI: Misalai 22:13, Misalai 23:30-32, 3 Yahaya 1:2

28 YULI 2026KU RIƘE UBANGIJI Ubangiji nagari ne, mafaka a kwanakin wahala, kuma ya san waɗanda s**a dogara gare shi. Nah...
28/07/2026

28 YULI 2026

KU RIƘE UBANGIJI
Ubangiji nagari ne, mafaka a kwanakin wahala, kuma ya san waɗanda s**a dogara gare shi. Nahum 1:7

Muna cikin kwanakin wahala na ƙarshen zamani. Akwai guguwa a ko'ina. Tsoro da tasan hankula suna a kan mutane, al'ummai da kuma duniya baki ɗaya. Amma ba za ku taɓa Kainku ba a cikin sunan Yesu krista. Yesu ya ce "a cikin wannan duniya, za ku fuskanci matsaloli, amma ku yi farin ciki, na shawo kansu". Ubangiji ne ƙarfinku da mafakar ku. Ya san cewa amincewarku tana gare shi ne don ceto, warkarwa, tanadi, kiyayewa da nasara. Ba zai taɓa kunyata da ku ba a cikin sonar Yesu. Ku riƙe amincinku da ƙarfi ga Ubangiji kuma ba za ku taɓa jin tsoro ko ku sha kunya ba. Na yi maku addua, ƙarfafawar bangaskiyarku da amincinku mai ƙarfi ga Ubangiji ne dungum. Ba za ku taɓa girgiza, tsoro ko ku sha kunya ba ko kadan a cikin sunan Yesu Kristi mai ceton mu. Amin

KU CE: Ka yi mini jinƙai Ubangiji, inda na ji tsoro kuma na girgiza da matsalolin da nake fuskanta. Amin

FURTA: Dogarata tana gare ka Ubangiji, ba zan taɓa jin tsoro ba domin kana nan koyaushe don taimako da cetona. Amin

ADDU'A: Uba na gode maka saboda rahamarka, ka kawar da tsoro daga gare ni, ka ba ni aminci marar girgiza a gare ka ta wurin kalmarka da ruhunka cikin sunan Yesu. Amin

ƘARIN NASSOSHI: Zabura 125:1-5, Yahaya 16:33, 1 Yahaya 4:4

25 YULI 2026KADA KU FADA MASU Da ya zo garinsu, ya koya musu a majami'arsu, har s**a yi mamaki, s**a ce, “Daga ina mutum...
25/07/2026

25 YULI 2026

KADA KU FADA MASU
Da ya zo garinsu, ya koya musu a majami'arsu, har s**a yi mamaki, s**a ce, “Daga ina mutumin nan ya sami wannan hikima haka, da kuma mu'ujizan nan? Matta 13:54

Kada ku gaya masu. Yesu yayi koyaswa a garinsu. Mutane s**a yi mamaki da hikima da iko da s**a gani da Kuma ji. Maimoko su girmama Ubangiji su dogara da shi, sai s**a shige bincike. Suna cewa, daga Ina ne ya Sami wannan hikima da iko da muke Ji da gani? Domin suna gani sun san da iyalin da ya fito da yan'uwan sa. KU ji! Duk Wanda suke gani kamar baza KU Zama komai ba ko KU zama masu wadata da girma ba domin sun san inda Kuka fito, za su Sha mamaki abun da Ubangiji za ya yi a rayukan Ku. Ubangiji na zaya fifita ku a cikin sunar yesu Kristi. Zasu gan daukakkan ku su Kuma ji a cikin sunar Yesu Kristi. Sa'anda s**a shige bincike, suna tambaya, Yaya aka yi? Daga Ina? Kada ku gaya masu. Domin daga farkon Basu tare da Ku, Kuma Basu gaskanta zaku Zama komai ba. Ko Kun gaya masu, baza su yarda ba, ko Kuma su yi anfani da shi domin su Bata ku da sunan ku. Duk Wanda Yana anfani da ababai da Kuka gaya masu game da rayukan Ku, da jarin ku, da arzikin ku, ko gidan auren ku da sauran su, suna Bata sunayen ku a gari da yin maku mugunta, Bari ta komo kainsu a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceton mu. Amin

KA FURTA: Ya Ubangiji Allah, yi Mani jinkai, inda na gaya wa abokanai wasu asirin iyalina, jari na, arziki na, da sauran su, suna anfani da shi domin su Bata suna na da Kuma Yi Mani mugunta. Amin

KA CE: CeCe Ni ya Ubangiji daga hannun su. Ka juya manufa muguntar su a kainsu. Amin

ADDU'A: Nagode ya Ubangiji Allah, domin jinkai'n ka, taimaka Mani da ruhun ka yayin da ka daga Ni, ka Kuma albarkace ni, kada in ba wa magabci zarafi da asirin albarku na ta wurin maganganu da nake Yi da abokanai a cikin sunan Yesu Kristi Mai ceto. Amin

KARIN AYOYI: Matta 13:53-58, Yahaya 18:1-11, Luka 20:1-8, Yahaya 1:43-51

24 Yuli 2026ALBARKU DOMIN KUAlbarkace, ya Ubangiji, arzikin shi da aikin hannuwan sa, ka yake duk Wanda suke tayar Masa ...
24/07/2026

24 Yuli 2026

ALBARKU DOMIN KU
Albarkace, ya Ubangiji, arzikin shi da aikin hannuwan sa, ka yake duk Wanda suke tayar Masa da Kuma nuna masa kiyayya, kada su sake tasowa. Deuteronomy 33:1

Rayuwa mara albarka, rayuwa ne Mai wuya da azarbar. Shi ya sa tun daga farko, Ubangiji ya albarkace halitatun sa. Kuma, duk lokacin da an furta albarka komai ya kan Zama da sauki da Kuma kyau. Da Ubangiji ya albarkace halitatun, ya ce Masu, ku ribabanya, ku yadu.. Farawa 1:1-28, tun lokacin, halitatu suna bada ya'ya iri ta kainsu, sun Kuma yadu. Bari albarkun Ubangiji ta bayana a dukan yeneyi rayuwa ku. Ta wurin kalmar ubangiji a yau, Ubangiji Allah ya albarkace arzikin ku da aikin hannuwan ku, ya Kuma taka duk Wanda ya tayar maku da makiyin ku, ba zasu Kuma taso maku ba a cikin sunar Yesu Kristi. Salama da wadata CE rayuwar ku za ta ta Bata yau da kullum a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceton mu. Amin

KA FURTA: Nagode ya Ubangiji domin albarkun ka a rayuwa na da dukan aikin hannuwa na. Amin

KA CE: Na karbi albarkun ka ya Ubangiji yau da kullum, harabada. Amin

ADDU'A: Karbi yabo na da daukakka ya Ubangiji na Domin ababai masu kyau da kake Yi Mani yau da kullum, da albarkun ka a kain rayuwa na. Nagode kwarai da gaskiye a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceto. Amin.

KARIN AYOYI: Deuteronomy 33:1-29, Farawa 1:28, Matta 5:1-12, Deuteronomy 28:1-29

2 YUNI 2026BANI HIKIMAYanzu sai ka ba ni hikima da sani yadda zan iya kai da kawowa a gaban wannan jama'a, gama wa zai i...
23/07/2026

2 YUNI 2026

BANI HIKIMA
Yanzu sai ka ba ni hikima da sani yadda zan iya kai da kawowa a gaban wannan jama'a, gama wa zai iya mulkin wannan jama'a taka mai yawa haka?”2 Tar 1:10

Hikima shi ne mahimin Abu. Kowa na neman hikima a duk yeneyin rayuwa ta yau da kullum. Ko a makarantu, ko wurin jari, da iyalai, da wurin aiki, da sarauta ko masu mulkin. Sulemanu, sarkin isra'ilawa, ya ga yarda baban'sa sarkin Dauda ya bi da jama'a a kullum, ya gane cewa, Yana neman hikima in har za ya ci nasara mulkin jama'ar sa. Ya roki Ubangiji, Ubangiji Allah Kuma ya bashi fiye da yarda yeke samani. Mu ya'yan Ubangiji Allah ne, Mai bayaswa hikima a yawarce da kuma hanu sake. Mu roka, zaya bamu. Karbi hikimar Ubangiji Allah a cikin sunar Yesu Kristi. Hikiman Nan za ta bayana a dukan yeneyin rayuwar ku. Amin

KA FURTA: Yafe Ni ya Ubangiji, duk inda na Yi wawanci ko rashin hikima a duk yeneyin rayuwa na da baka ji Dadi ba. Amin

KA CE: Ya Ubangiji Allah, na roki, ba bani hikimar ka. Na kuma karbi yanzun a cikin sunar Yesu Kristi. Amin

ADDU'A: Nagode ya Ubangiji Allah, Domin jinkai da alherin ka. Da Kuma hikima da ka bani. Bari ta bayana a duk ababai da Zan yi a cikin sunar Yesu Kristi. Amin

KARIN AYOYI: 2 Tar 1:6-13, Yakub :5,17, misalai 4:7

22 Yuli 2026RAYUWAR MUTUM Ya kuma ce musu, “Ku kula fa, ku yi nesa da kowane irin kwaɗayi, don yawan kaya wadata ba shi ...
22/07/2026

22 Yuli 2026

RAYUWAR MUTUM
Ya kuma ce musu, “Ku kula fa, ku yi nesa da kowane irin kwaɗayi, don yawan kaya wadata ba shi ne rayuwa ba. Luka 12:15

Yawancin mutane, suna gani rayuwa shine a Yi arziki da wadata, a ji Dadi da Kuma tare-tare kayan duniya. Ko da shike suna da kyau Kuma Ubangiji Yana so mu more su mu Kuma ji Dadi. Amma, Ubangiji baya so mu damre rayukan mu ga kayan duniya da Kuka Tare. Baya so domin an Sami abinda ake so, KU manta da shi aki zumunta da shi da yanwa cikin Kristi, ana Ababai da aka gan dama. Amma a cigaba cikin zumunta da uba da ya'yan sa, ana taimaka wa yan'uwa da Basu da shi da kuma yin bishara da ababai da ya albarkace mu da shi. Kada mu dogara da arziki da wadata da muka tare. Mu dogara ga Ubangiji Allah kadai. Me zai anfane mu, in mun malaki duniya duka, Amma mu Rasa rain mu? Ceton rayukan mu yafi dukan komai. Ba mu zo duniya da komai ba, ba za mu Kuma koma da komai ba. Ba za mu dogara da arziki da wadata da muka Tara ba, Amma za mu dogara ga Ubangiji Allah da sunar sa kadai a cikin sunar Yesu Kristi harabada. Amin

KA FURTA: Yafe Ni ya Ubangiji, duk in na dogara ga kaina, ko mutum, da arziki ko wadata da na tare. Amin

KA CE: Ni na dogara ga Ubangiji Allah na, ba Zan sa bege na ga wani ba ko yawan arziki da wadata ba. Amin

ADDU'A: Ya Ubangiji Allah, nagode domin ceton Raina, dogara na da bege a kainka ne, da kalmar ka, da Kuma ikon ruhu ka. Zan Yi anfani da naiwa da ka bani, da arziki da wadata in bauta Maka da Kuma nuna wa mutane kaunar ka ta wurin taimoko da bishara a cikin sunan Yesu Kristi Mai ceto. Amin.

KARIN AYOYI: Luka 12:13-21, Matta 6:33, mark8:36-38, 1tim6:7

20 Juli 2026KU ZAMA MASU BAYASWA..kuna Kuma tunawa da maganar ubangiji yes da ya ce " bayaswa ta fi karban albarka". Ayu...
20/07/2026

20 Juli 2026

KU ZAMA MASU BAYASWA..kuna Kuma tunawa da maganar ubangiji yes da ya ce " bayaswa ta fi karban albarka". Ayukan M.20:35

Ka Zama Mai bayaswa domin tafi albarka. Abun mamaki shine yawancin mu muna so abamu domin a tunanin mu shine yafi albarka. In ka zauna a gefen karba, ka Zama maroki kena. Domin maroki ne ke so abashi a ko wani lokaci. Yesu ya ce. Mai bayaswa na tare da albarka Mai yawa. Sirin arziki kenan bayaswa. A cikin kakanta Abun da ke abashin ka sai ka bayas da zaka, ka bayas don bishara da kuma Gina ikilisiya, ka bayas don pastoci da kuma ka taimaka ma waddanda ba su da shi. Bayaswa allama ce na bangaskiya cikin Ubangiji. Matan Nan da ta ba da anini biu. Ta ba da shi duka. Ba ta yi tunani, abun da za ta ci ba ko kuma sha, ko Kuma kayan sa, ko wurin kwana ba. Ta saka duka. Yesu ya gan wannan ya ce. Ta yi baban bayaswa. Na Tabatha's matan Nan ta samu albarkan Yesu. Ba ta San talauci Kuma ba. Hallelujah! In har Yesu Yana iya Mai da kifi biu da bredi biyar ya ciyas da dinbin mutane. Meyas da matan Nan Mai arziki Mai sauki ne. Ka bayas da kyuata Mai kyau da zai gamshe Ubangiji. Karbi alheri Ubangiji na bayaswa. Yayin da ka bayas, Bari arziki ta sauko maka a ko wace hanya a cikin sunar Yesu Almasihu Mai ceton mu. Amin.

KA FURTA: Ni me bayaswa ne cikin sunar Yesu. Amin

KA CE: Ni bana gefen karba, ina gefen bayaswa. Amin

ADU'A: Ya Yesu? Nagode domin zarafi don in nuna maka kauna da sujada ta wurin bayaswa. Na karbi alherin ka na bayaswa a cikin sunar Yesu Kristi mai ceto. Albarkan ka ta Tabatha a rayuwa na. Amin

KARIN AYOYI: Filibiyawa 4:18-19, Luka 6:38, Matta 6:30-34, 2 Korintiyawa 9:7, Luka 12:13-21

16 YULI 2026KADA KU FADA MASU Da ya zo garinsu, ya koya musu a majami'arsu, har s**a yi mamaki, s**a ce, “Daga ina mutum...
16/07/2026

16 YULI 2026

KADA KU FADA MASU
Da ya zo garinsu, ya koya musu a majami'arsu, har s**a yi mamaki, s**a ce, “Daga ina mutumin nan ya sami wannan hikima haka, da kuma mu'ujizan nan? Matta 13:54

Kada ku gaya masu. Yesu yayi koyaswa a garinsu. Mutane s**a yi mamaki da hikima da iko da s**a gani da Kuma ji. Maimoko su girmama Ubangiji su dogara da shi, sai s**a shige bincike. Suna cewa, daga Ina ne ya Sami wannan hikima da iko da muke Ji da gani? Domin suna gani sun san da iyalin da ya fito da yan'uwan sa. KU ji! Duk Wanda suke gani kamar baza KU Zama komai ba ko KU zama masu wadata da girma ba domin sun san inda Kuka fito, za su Sha mamaki abun da Ubangiji za ya yi a rayukan Ku. Ubangiji na zaya fifita ku a cikin sunar yesu Kristi. Zasu gan daukakkan ku su Kuma ji a cikin sunar Yesu Kristi. Sa'anda s**a shige bincike, suna tambaya, Yaya aka yi? Daga Ina? Kada ku gaya masu. Domin daga farkon Basu tare da Ku, Kuma Basu gaskanta zaku Zama komai ba. Ko Kun gaya masu, baza su yarda ba, ko Kuma su yi anfani da shi domin su Bata ku da sunan ku. Duk Wanda Yana anfani da ababai da Kuka gaya masu game da rayukan Ku, da jarin ku, da arzikin ku, ko gidan auren ku da sauran su, suna Bata sunayen ku a gari da yin maku mugunta, Bari ta komo kainsu a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceton mu. Amin

KA FURTA: Ya Ubangiji Allah, yi Mani jinkai, inda na gaya wa abokanai wasu asirin iyalina, jari na, arziki na, da sauran su, suna anfani da shi domin su Bata suna na da Kuma Yi Mani mugunta. Amin

KA CE: CeCe Ni ya Ubangiji daga hannun su. Ka juya manufa muguntar su a kainsu. Amin

ADDU'A: Nagode ya Ubangiji Allah, domin jinkai'n ka, taimaka Mani da ruhun ka yayin da ka daga Ni, ka Kuma albarkace ni, kada in ba wa magabci zarafi da asirin albarku na ta wurin maganganu da nake Yi da abokanai a cikin sunan Yesu Kristi Mai ceto. Amin

KARIN AYOYI: Matta 13:53-58, Yahaya 18:1-11, Luka 20:1-8, Yahaya 1:43-51

15 YULI 2026MENENE DALILAIN KU?Sai dukansu baki ɗaya s**a fara kawo dalilai. Na farko ya ce masa, ‘Na sayi gona, lallai ...
15/07/2026

15 YULI 2026

MENENE DALILAIN KU?
Sai dukansu baki ɗaya s**a fara kawo dalilai. Na farko ya ce masa, ‘Na sayi gona, lallai ne in je in ga gano ta. Ina roƙonka ka ɗauke mini,’ Luka 14:18

Yesu Kristi ya bada wata misali, ya ce "akwai wani babban mutum ya shirya liyafa, sai ya gayace mutane duka. Ranar liyafa ta Kai, sai ya aiki bayin sa su gayato su. Amma mutanen gabaki Daya s**a kawo Masa dalilai rashin zuwan su. Babban mutumin Nan Mai buki ya yi fushi da su". Haka Nan ubangiji Allah yana shirya albarku a kowace zumunta, ko sujada, da taruwai ya'yan isa almasihu. Amma mutane na kin zuwa. Menene dalilain ku? Ubangiji na fushi duk lokacin da aka gaiyato ku, Amma Kuna bayas da dalilain rashin zuwa. Ubangiji Allah shi Yi Mana jinkai'n. Duk abinda zata tayar da fushin da la'anar Ubangiji a rayukan mu Ubangiji Allah ya dauke Mana a cikin sunar Yesu Kristi. Ruhu Mai tsarki, ta bishe ku yayin da zaku amsa, ku Kuma kasance a duk Wata liyafa, da Ubangiji ya shirya maku domin ya albarkace ku. Ba za ku rasa albarkun ku soboda dalilai ba a cikin sunar Yesu Kristi Mai ceton mu. Amin

KA FURTA: Ya Ubangiji Allah, ka yafe duk lokatai da na Yi ta ba da dalilain kin zuwa sujada, ko zumunta, da taruwai domin ka albarkace ni. Yi Mani jinkai ka dauke fushi da la'anar ka. Amin

KA CE: Da taimokon ruhun Mai tsarki, ba Zan fasa zuwa gaiyatan ka ba ya Ubangiji na. Za kasance da Kai, in zauna tare da kai, in Kuma mora albarkun liyafa da ka shirya Mani. Amin

ADDU'A: Nagode ya Ubangiji domin jinkai'n ka. Bishe da ruhun ka in kasance a duk taruwai, liyafa, sujada, duk Wata Zumunta da kake. Ba Zan Rasa albarku da ka shirya Mani ba a cikin sunan Yesu Almasihu mai ceto. Amin.

KARIN AYOYI: Luka 14:15-33, Matta 14:13-21, Yahaya 2:1-10

13 YULI 2026ME KAKE SO“Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ya Ubangiji, in sami ganin gari". Luka 18:41Yesu Yana wucewa ta g...
13/07/2026

13 YULI 2026

ME KAKE SO
“Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ya Ubangiji, in sami ganin gari". Luka 18:41

Yesu Yana wucewa ta garin Jericho. Sai wani makaho, maroki da ke bakin hanya. Ya sami Ganewa cewa yesu ne ke wucewa. Sai ya tayar da muriya sa yana roka. Yana cewa "Ya Dan Dauda, kayi mani jinkai". Sai Yesu ya ji muriyar sa, ya tsaya, ya Kuma kirawo sa. Sai ya tambaye shi. Me kake so, in yi maka? Sai ya ce, "Ina so in Sami ganin gari". Yesu Kuma ya bude idannun sa. Ya Sami ganin gari. Me kuke so Ubangiji Allah yayi maku? Menene bukatun ku? Gaya was Yesu yanzun, shi za ya amsa maku. A cikin sunar Yesu Kristi karbi amsoshin tamboyoyin ku da albarku da kuke bege a cikin sunar Yesu Kristi. Amin

KA FURTA: Ya Ubangiji Allah, ka yi mani jinkai ka biya Mani bukatu na a cikin sunar yesu Kristi. Amin

KA CE: Na gaskanta ya Ubangiji, Kuma na karbi amsoshin tamboyoyi, da bukatu na a cikin sunar Yesu Kristi. Amin

ADDU'A: Ya Ubangiji Allah, nagode domin jinkai'n ka da alherin ka. Kana ji na a kowace lokaci, Kuma yau ka ji Ni Kuma ka amsa mani. Na good a cikin sunar Yesu Kristi. Amin.

KARIN AYOYI: Filibiyawa 4:19, Yahaya 16:23-24, Yakubu :3

Adresse

Cotonou

Téléphone

+22990005773

Site Web

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Bari Haske ta Haskaka-daga Apostle Caleb Yakubu publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Raccourcis

Partager