Daarus-sahaabah Network

Daarus-sahaabah Network “Doing religion best on teaching of Alqur'an and Sunna according to understanding of Prophet and his companion.”

18/06/2020

KIMIYYAR HADISI A SAUKAKE

Littafi na 1 Darasi na 11

✍️: Sheikh Muhammad Auwal Nuhu Allemawy

BABI NA BIYU:

RABE-RABEN HADISI DUBA DA INDA YA TUKE:

Bayan mun taba wani bangare na bayanan da s**a shafi sanadin hadisi kamar yadda ya gabata, na bayanin mutawatiri da Áhád, yanzu kuma za mu tsallaka mu waiwayi bangaren Matanin hadisi mu san wani abu daga siffofi da lakubbansa kafin mu dawo mu sake waiwayar sanadi da izinin Allah s.w.t.

Idan ba a manta ba a baya mun yi bayanin ma`anar matani cewa: shine abin da aka jinginawa Manzon Allah s.a.w ko waninsa, na daga zance ko aiki ko goyon bayan aikin wani.

Yanzu kuma abin da za mu sani a wannan babi da yardar Allah shine rabe-raben hadisi duba da inda mataninsa ya tuke.

Abin nufi da inda matanin hadisi ya tuke, shine wanda aka dangantawa abin da matanin hadisin ya kunsa, misali a ce Allah s.w.t ya ce kaza, ko Manzon Allah s.a.w ya ce kaza, ko sahabi wane ya ce kaza, ko tabi`i wane ya ce kaza.

Idan muka lura da wannan bayanin na karshe za mu ga cewa an danganta matanin hadisi zuwa bangarori hudu.

1- An danganta matani na farko zuwa ga Allah s.w.t kai tsaye a ka ce: Allah s.w.t ya ce kaza.
2- An danganta matani na biyu zuwa ga Manzon Allah s.a.w aka ce: Manzon Allah s.a.w ya ce kaza ko ya aikata kaza ko ya ga ana yin kaza ya goyi baya.
3- An danganta matani na uku zuwa ga sahabin Manzon Allah s.a.w aka ce sahabi wane ya ce kaza ko ya aikata kaza.
4- An danganta matani na hudu zuwa tabi`i (wanda ya ga sahabi yana mai imani kuma ya rasu bisa imani) aka ce tabi`i kaza ya ce kaza.

Duba da wadannan banbance-banbance ne malaman hadisi s**a raba mataninsa zuwa nau`o`i guda hudu, s**a kuma lakabta wa kowanne nau`i daga cikinsu sunansa da ya dace da shi.

Sunayen sune kamar haka:

- Alhadisul kudusy
(الحديث القدسي)
- Almarfu`u.
(المرفوع)
- Almaukufu
(الموقوف)
- Almakxu`u.
(المقطوع)

In sha`allahu za mu xauki wadannan nau`o`i daya bayan daya mu yi bayaninsu.

NAU`I NA FARKO: ALHADISUL KUDUSY
(الحديث القدسي)

1- Tanta

17/06/2020

KIMIYYAR HADISI A SAUKAKE

Littafi na 1 Darasi na 10

✍️ Sheikh Muhammad Auwal Nuhu Allemawy

HUKUNCIN HADISI ÁHÁD

Yanzu dai -in sha`allah- mai karatu ka fahimci abin da ake nufi da hadisi Áhád, shine hadisin da bai kai matsayin tawaturi ba, ka kuma fahimci raben rabensa (Algarib – Al`aziz – Almashhur) da bayani a kan kowannensu.

Abin da ya rage yanzu shine: sanin hukuncin wannan nau`i na hadisi. Sai mu ce:

Hadisi Áhád -sawa`un Garibi ko Azizi ko Mashhuri- idan sanadinsa ya inganta kuma ya kubuta daga boyayyun illoli, to za a karbe shi a kuma kafa hujja da shi a yi aiki da shi cikin shari`ar musulinci.

Wannan shine sananne kuma karbabben hukunci wajan magabatan kwarai tun daga zamanin Manzon Allah s.a.w har zuwa wadanda s**a biyo bayansa na daga malaman karnonin farko mfiya falala.

Za mu kawo wasu daga dalilai daga magabata da ke tabbatar da ingancin karbar hadisi Áhád tare da aiki da shi:

1- TAKRIRIN MANZON ALLAH S.A.W: Manzon Allah s.a.w ya kasance yana aiken mutum daya zuwa ga sarakuna da talakawansu, don isar musu da addini da kuma karantar da su shi idan sun karba, kamar yadda ya aiki Mu`az ibnu Jbal zuwa Yaman daga baya ya sake tura Abu Musa Al`ash`ary don su raba aiki da Mu`az. Hakanan ya tura Dihyah Alkalby zuwa ga shugabannin kasar farisa.

2- AIKIN SAHABBAI: Sahabban Manzon Allah s.a.w sun kasance suna karbar hadisin mutum daya ba tare da wani inkari ba. Wannan shahararren abu ne ya yadu cikinsu kuma duk mai bibiyyar sira da kalamansu ya san haka. Misali a kan haka:

- Lokacin wafatin Manzon Allah s.a.w sahabbai sun kasance ba su san ina ya kamata su binne shi ba, don haka s**a fara shawarar inda za a binne shi, sai Abubakar ya ce: ya ji Manzon Allah s.a.w yana cewa Annabawa ana binne su ne a inda s**a rasu
Yarda da maganar Abubakar r.a ta sa sahabbai s**a binne Annabi s.a.w a dakin A`isha r.a kasancewarsa a nan ne ya cika.

- Hakanan Umar Ibnu Khaddab ya karbi maganar Abdurraahman Ibnu Auf yayin da ya ba shi labari cewa ya ji Manzon Allah s.a.w yan

17/06/2020

KIMIYYAR HADISI A SAUKAKE

Littafi na 1 Darasi na 9

✍️ Sheikh Muhammad Auwal Nuhu Allemawy

(ci gaban bayani a kan Mashhur)

JAN HANKALI

Sau da yawa malamai kan kira hadisi da mashhuri amma ba suna nufin mushhuri na isdilahi wanda bayani ya gabata kansa ba, sai dai suna nufin shaharar hadisin a bakin mutane ko a wajan wasu nau`i na ma`abota ilimi.

Irin wannan shaharar kuwa ba ta da alaka da shahara ta isdilahi da ake bukatar mutum uku ko sama da uku su rawaito hadisi kafin ta tabbata.

Wannan shaharar da malamai kan ambata tana da alaka ne kawai da yaduwar hadisin cikin wasu nau`i na jama`a, don haka hadisin da aka siffanta da ita, na iya kasance garibi ko azizi ko mashhuri na isdilahi ko ma ya zama ba shi da isnadi kwata kwata.

Irin wannan shaharar ta kasu gida gida gwargwadon mutanen da hadisin ya shahara cikinsu.

- Akwai hadisan da sun shahara a wajan malaman hadisi. Misali: fadin Manzon Allah s.a.w:

«نضر الله امرأ سمع مقالتي فوعاها فبلغها كما سمعها»

Ma`ana: "Allah ya haskaka mutumin da ya ji maganata sai ya kiyaye ta, ya je ya isar da ita (ga wani) kamar yadda ya ji.."
Wannan hadisi ne da ya shahara a bakunan malaman hadisi, don haka idan aka kira shi mashhuri ana nufin shahara ta lugga ba ta isdilahi ba.

Amma da za mu koma ga isnadinsa za mu sa shi ne a layin hadisai mutawatirai, kamar yadda Alhafiz Assuyudy yake cewa: "wannan hadisi ne mutawatiri, kwatankwacin sahabbai talatin ne s**a rawaitoshi".

- Akwai hadisan da s**a shahara wajan malaman fikhu. Misali: hadisin:

«أبغض الحلال إلى الله الطلاق»

Ma`ana: "halalin da Allah ya fi ki shine sakin aure"

Idan da za mu koma ga isdilahi za mu ga cewa: wannan hadisi ne garibi kuma mai rauni, an rawaito shi ne ta hanyar Ubaidullahi Alwassafy daga Muharib Ibn Disar daga Abdullahi iBnu Umar.

- Akwai kuma hadisan da s**a shahara a bakin malaman nahwu kamar hadisin:

نعم العبد صهيب لو لم يخف الله لم يعصه

Ma`ana: "madalla da wannan bawa Suhaib, ko da ba ya tsoron Allah to ba zai saba masa ba"

Hadisi ne da ba

16/06/2020

Masha Allah!

Marigayi Malam Albaniy Zaria Ya Samu Jika Wadda Babban Dan Shi Abdurrahman (Abu Huraira) Tare Da Matar Shi Halima S**a Haifa. Sun Sanyawa Jaririn Suna Ibrahim.

Allah Shi Raya Ibrahim Yai Mishi Albarka Ya Dora Shi Kan Tafarkin Gwagwarmayar Yada Sunnah Wadda Kakan Shi Yayi Shahada (Insha Allah) Akai.

15/06/2020

KIMIYYAR HADISI A SAUKAKE

Littafi na 1 darasi na 8

✍️ Sheikh Muhammad Auwal Nuhu Allemawy

(Rabe-raben hadisi Áhád)

KASHA NA UKU ALMASHHUR
(لمشهور)

1- TANTANCESHI: Hadisi Mashhur shine hadisin da aka samu daya daga cikin matakan sanadinsa mutum uku ne s**a rawito shi, ko sama da uku, matukar bai kai matsayin tawaturi ba, da sharadin kada a samu kasa da mutum uku a kowanne mataki na sa.

Abin nufi shine: ba za a kira hadisi Mashhuri ba sai ya zama a kowanne mataki daga matakan marawaitansa an samu mutum uku ko fiye da uku, amma kada yawansu ko cin gashin kansu ya kai matsayin da za a basu darajar tawaturi.

2- Misalinsa: Hadisin Addu`ar shiga bayan gida (makewayi).

Imam Bukhary da Muslim sun fitar daga Anas Ibnu Malik r.a ya ce:

كان رسول الله صلى الله عليه وسلم إذا دخل الكنيف قال: «اللهم إني أعوذ بك من الخبث والخبائث»»

Ma`ana: Manzon Allah s.a.w ya kasance idan zai shiga bayan gida yana cewa: "Ya Allah ina neman tsarinka daga (sharrin) mazajen shaidanu da matayensu".

Idan muka bibiyi Isnadin wannan hadisin za mu ga cewa:
Wadanda s**a rawaitoshi daga Anas r.a sune kamar haka:

- Abdul Aziz Ibnu Suhaib, da Abdullahi Ibnu Abi Dalha, da Katadah.

Idan mun sakko kas aga almajiransu kuma za mu ga cewa:

- Mutane da yawa sun rawaitoshi daga Abdul Aziz daga cikinsu akwai: Shu`ubah, da Hammad Ibnu Zaid, da Hushaim, da Isma`il Ibnu Ulayyah. (hadisin Shu`ubah yana cikin Sahihul Bukhary. Hadisin Hammad da Hushaim yana cikin Sahihu Muslim, Hadisin Ibnu Ulayyah yana cikin Musnad na Ahmad).

- Wanda ya rawaitoshi daga katada kuma shine Adiyyu Ibnu Abi Umarah. (Hadisinsa yana cikin littafin Addu`a na Dabarany).

- Wanda ya rawaito daga Abdullahi Ibnu Abi Dalha kuma shine: Najih Abu Mi`ishar. (Hadisinsa yana cikin littafin Almusannaf na Ibnu Abi Shaibah).

Tun da mun samu mutum uku sun rawaito wannan hadisi daga Anas r.a, kuma kowannensu an samu hanyoyi daban daban daya ko fiye da daya daga kowannensu shikenan hadisin ya zama mashhuri daga Anas r.a.

Duba taswirar da ke k

14/06/2020

JAN KUNNE MAI AMFANI!
✍ Mansur Sokoto
Lahadi 22 ga Shawwal 1441H
(14/06/2020)

عَنْ أبي عَبْدِالرَّحمنِ بِلال بنِ الحارثِ المُزنيِّ رضي الله عنه أنَّ رَسُولَ اللَّه ﷺ قالَ: إنَّ الرَّجُلَ ليَتَكَلَّمُ بالْكَلِمَةِ مِنْ رِضْوانِ اللَّهِ تَعالى مَا كَانَ يَظُنُّ أنْ تَبْلُغَ مَا بلَغَتْ يكْتُبُ اللَّه لَهُ بهَا رِضْوَانَهُ إِلَى يَوْمِ يلْقَاهُ، وَإنَّ الرَّجُلَ لَيَتَكَلَّمُ بالكَلِمةِ مِنْ سَخَطِ اللَّه مَا كَانَ يظُنُّ أنْ تَبْلُغَ مَا بلَغَتْ يكْتُبُ اللَّه لَهُ بهَا سَخَطَهُ إِلَى يَوْمِ يلْقَاهُ.
رواهُ مالك في "المُوطَّإِ" والترمذي وقال: حديثٌ حسنٌ صحيحٌ.
Hadisi ya zo daga Bilal bn Al-Harith Al-Muzani (R.A) ya ce, Manzon Allah (S) ya ce: _"Tabbas, mutum yakan furta wata kalma ta yardar Allah bai zata za ta kai in da ta kai ba, amma ta zama dalilin Allah ya wajabta masa yardarsa daga nan har zuwa tashin kiyama. Wani mutum kuma yakan furta wata kalma mai janyo fushin Allah, bai zata za ta kai in da ta kai ba, amma ta zama dalilin Allah ya wajabta masa fushinsa daga nan har ranar da zai hadu da shi"_.*
Imam Malik ne ya ruwaito shi a Muwatta, Tirmidhi ma haka, kuma ya inganta shi.

Marubuta a kafaifan sadarwa, mu kiyaye wannan Hadisi, mu ji tsoron sa, mu yi hattara da gargadin da ya kunsa.

A da, idan ka yi magana mutane kadan za su ji ta. A yau idan ka yi posting mutane bila adadin za su karanta. Wasu za su yi "like" ko "comment" ko "share" sai su kara watsa shi. Idan alheri ne adadin yana karuwa ladarka tana hauhawa. Idan kuma zunubi ne adadin yana karuwa zunubin yana hauhawa, daga nan zai iya kai ka/ki ga halaka.

Duk wanda ya san ya rubuta ko ya yi sharing abinda ba zai samar masa da ladar da za ta amfane shi ba, ina ba shi shawarar ya goge. Idan kuma wanda ba a iya gogewa ne (kamar na Whatsapp da aka tura a Groups mutane s**a sauke) to, ya rubuta wani abin alheri da zai rufe shi.

Allah _ta'ala_ ya ce: "Hakika, ayyukan kwarai suna tafiyar da na laifi" Suratu Hud: 114

Manzon Allah (S) ya ce: "Kuma ka bi aikin zunubi da wani na lada sai ya share shi" Tirmid

13/06/2020

*KIMIYYAR HADISI A SAUKAKE*
Littafi na 1 darasi na 5

✍️ Sheikh Muhammad Auwal Nuhu Allemawy
*_Manazarci a Matakin digirgir a Kolejin Hadisi ta Jami'ar Musulunci a Birnin Madina_*

(ci gaban bayani a kan Mutawatir)

4- HUKUNCINSA: Hadisi Mutawatiri babu shakka a kan ingancinsa zuwa ga Manzon Allah s.a.w.
Don haka da zarar ya hadisi ya cika sharuddan tawaturi to ana da yakini cewa lallai Manzon Allah s.a.w ya fadeshi ko ya aikata shi, babu kokwanto kan haka.
Don haka ne ma ko binciken halayen mazajen isnadansa ba a yi, domin ya fi karfin bincike.
Wanda kuwa y ace zai tsaya binciken ingacin hadisi mutawatiri bayan ya tabbatar da ya cikan sharuddan tawaturi to kada ka nesanta wannan mutumin zai iya sanya shakku game da ingancin Alkur`ani, domin shima alkur`ani ta hanyar tawaturi ya zo mana.

5- RABE-RABENSA: hadisi mutawatiri ya kasu kashi biyu:
- Hadisin da lafazinsa ya cika sharuddan tawaturi:
Malamai suna kiransa da suna: Almutawatir Allafzy
(المتواتر اللفظي)
Wannan shine hadisin da adadi mai yawa s**a rawaito shi a kowanne mataki na sanadinsa, tun daga farko har karshe da lafazi iri daya.
- Sai kuma wanda ma`anarsa ta cika sharuddan tawaturi ba lafazinsa ba:
Malamai suna kiransa da suna: Almutawatir Alma`anawy.
(المتواتر المعنوي)
Wannan kuwa shine tarin hadisan da marawaita da yawa s**a rawaito da lafuzza daban daban na wasu abubuwa da s**a faru ko wasu hukunce hukunce da Manzo Allah s.a.w ya bayar a lokuta daban daban, amma a cikin wadannan hadisan akwai wata ma`ana guda daya da s**a yi tarayya a ciki. (misali zai biyo baya).

6- MISALANSA:

- Misalin hadisin da lafazinsa ya cika sharuddan tawaturi: hadisin da ya gabata a farkon littafin, fadin manzon Allah s.a.w:
«من كذب عليّ متعمدا فليتبوأ مقعده من النار»
Ma`ana: "Wanda ya yi mini karya da gangan to ya tanadi mazauninsa a wuta".

Kamar yadda ya gabata sahabbai masu yawa s**a rawaito wannan hadisi, wasu malamai sun ce: mutm (62) wasu sun ce sama da haka, wasu kuma kasa da haka.
Snnan kowanne sahabi akwai

11/06/2020

KIMIYYAR HADISI A SAUKAKE

Littafi na 1 Darasi na 6

✍️ Sheikh Muhammad Auwal Nuhu Allemawy
(Manazarci a matakin digirgir a tsangayar Hadisi ta Jami'ar Madina)

KASHI NA BIYU: AL-ÁHÁD
(الآحاد)
Abin da ake nufi da hadisi Áhád shine: dukkan hadisin da adadin marawaitansa basu kai matakin tawaturi ba.

Hadisi Áhád ya rabu gida uku (3) sune:
1- Al-garib (الغريب)
2- Al-Aziz (العزيز)
3- Al-mashhur (المشهور)
Za mu dauki wadannan nau`o`i daya bayan daya mu yi bayaninsu filla filla in sha`Allahu.

AL-GARIB (الغريب)
1- Tantanceshi: shine hadisin da marawaici daya kadai ya rawaitoshi a daya daga cikin matakan sanadinsa.

Abin nufi a nan shine: A samu daya daga matakan sanadin hadisi babu wanda ya rawaito shi sai mutum daya, sawa`un a matakin tabi`ai ko na kasa da su, har zuwa kan mawallafin da ya sanya hadisin cikin littafinsa.
Da zarar an samu mataki daya da cinkin matakansa da ba wanda ya rawaito shi sai mutum daya, to shikenan ya zama Garibi ko da kuwa a sauran matakan isnadin fiye da mutum daya ne s**a rawaito.

2- MISALINSA:

Shahararren hadisinnan na Umar bnu Alkhaddab dake bayani game da niyya.

عن عمر بن الخطاب رضي الله عنه، قال سمعت رسول الله صلى الله عليه وسلم يقول (إنما الأعمال بالنيات وإنما لكل امرىء ما نوى فمن كانت هجرته إلى دنيا يصيبها أو إلى امرأة ينكحها فهجرته إلى ما جاهر إليه)
Wannan hadisin babu wata hanya da aka rawaito shi (ingattacciya) sai hanyar Umar bnu khaddab.
Hakanan babu wanda ya rawaito shi daga Umar sai Alkamah ibnu Wakkas Allaisy.
Hakanan Babu wanda ya rawaito daga Alkamah sai Muhammad ibnu Ibrahim Attaimy.
Hakanan babu wanda ya rawaito shi daga Muhammad ibnu Ibrahim sai Yahya Ibnu Sa`id Al`ansary.
Daga wajan Yahya ne almajiransa da yawa s**a rawaito hadisin, wasu suna cewa kusan mutum dari biyu s**a rawaito shi daga gareshi.

A nan za mu ga cewa kusan mataki uku daga matakan marawaitan hadisin duka mutum dai dai ne s**a rawaito shi.

Wannan kuwa shine ake kira da hadisi garibi.

Tambihi: ba sharadi ba ne sai ya kasance mutum daya tal n

11/06/2020

Daarul Hadeethis Salafiyyah, Zaria-Nigeria.

BismilLaahir Rahmaanir Raheem...

Bayan haka:

Assalamu Alaikum wa RahmatulLaah...

Muna amfani da wannan damar wajen sanar da ɗaukacin Al'ummar Musulmi cewa za'a Tsayar da Sallar Juma'a
A *Jaami'us-Salafiy* dake muciya, haka kuma a
Daarul Hadeethis-Salafiyyah, da ke Gaskiya a gobe juma'a in shaa Allaah, sakamakon sanarwan gwamnatin jaha da ta sassuta dokar kulle sakamakon annobar covid-19.

Lokacin Sallah 12:00 na rana.

Kada a manta a sanya takunkumin rufe baki da hanci (watau: facemasks) 😷

Allaah Ya sa mudace.

11/06/2020

Allah Sarki. Ga abinda na rubuta a bara. Na dauka maganar ta wuce. Sai ga Vision FM Kaduna sun bugo mani jiya suna neman lallai a sake kara yi wa mutane bayani. Zaku saurari firar yau a wani shiri na musamman.

*Dr. Gumi da Azumin Sittu Shawwal: Magana ta Karshe*
✍ Dr. Mansur Sokoto
8 ga Shawwal 1440H (11 ga Yuni 2019)

Bismillahir Rahmanir Rahim
✒ Yau mako daya kenan da yin Sallar Idi. Kuma a kowace rana ta Allah sai wani Malami ya yi raddi kan da'awar Dr. Gumi cewa: "Azumin Sittu Shawwal bidi'a ne".
✒ Da dama daga cikin mutane sun kalli abin a matsayin sabanin Malamai ne wanda, za ka iya daukar duk maganar da ka ga dama a ciki. Wasu kuma suna kallon abin ba wata muhimmiyar magana ba ce tunda ma azumin kololuwarsa ya zama mustahabbi.
✒ Almajiran Dr suna ganin wata bajinta ce ya fito da ita inda ya kalubalanci kusan duk Malaman Sunnah, kuma ya zo da wani karatu wanda ba su da shi.
✒ Wasu da dama sun kammala azumin Sittu Shawwal a yau, wasu kuma sun fasa yi tunda yake sun gamsu cewa ba wani aikin alheri ne da Shari'a ta san da shi ba.

*Abinda nike son jawo hankalin jama'a zuwa gare shi:*
📌 Wannan magana ba ta sabani tsakanin Malamai ce ba. Domin kuwa babu wani Malami - a duk tsawon tarihin Musulunci - da ya ce, azumin Sittu Shawwal bidi'a ne in ban da Dr. Gumi. Shi kansa Imam Malik bai ce haka ba. Cewa ya yi: "Suna tsoron ya kasance bidi'a ne". Wanda ya yi nazari zai gano bambancin wannan magana da waccan. Don haka, kakaf, Malaman Malikiyya, cikin su har da wadanda s**a hardace Muwatta babu wanda ya tafi akan cewa, azumin bidi'a ne. A maimakon haka, sun yi ta nema wa Imam Malik mafita akan wannan magana, kasancewar hadisin ya tabbata daga Annabi (S) babu tantama. Kuma bai yiwuwa Annabi (S) ya yi umurni da yin abu sannan ace bidi'a ne.
📌 Malaman Sunnah sun dukufa wajen mayar da martani akan Dr Gumi ba don suna son su ci gyaransa ba. Ai Malamai har wadanda s**a fi shi suna yin kuskure kuma ayi masu uzuri. Amma shi, a nasa bangaren ba kuskure ba ne, manhaji ne ya da

09/06/2020

KIMIYYAR HADISI A SAUKAKE
Littafi na 1 darasi na 4

✍️ Sheikh Muhammad Auwal Nuhu Allemawy

BABI NA FARKO: RABE RABEN HADISI GWARGWADON YAWAN HANYOYIN DA AKA RAWAITO SHI:

Idan muka yi Nazari ga hanyoyin da marawaitan hadisi ke rawaito mana shi, za mu ga cewa ya kasu gwargwadon yawan marawaitansa kamar haka:

1- Ko dai ya zama an rawaito shi ta hanyoyi da dama mabanbanta juna, ta yadda ko wacce hanya tana cin gashin kanta ba tare da ta hadu da `yar uwarta ba.

2- Ko kuma ya zama ta hanya daya ko honyoyi kadan (biyu ko uku) aka rawaito shi.

Duba da wannan yanayi na riwayar hadisi ne malaman s**a kasa shi gida biyu, kuma ko wanne gida s**a raba shi zuwa wasu adadin dakuna, kuma s**a lakabta wa kowanne sunansa tare da bayanin siffofinsa da za su banbanta shi da dan`uwansa, da sharuddansa, da hukuncinsa.

Ga bayanin yadda abin yake:

KASHI NA FARKO:

Kashi na farko shine hadisin da aka rawaito shi ta hanyoyi masu yawa mabanbanta juna:

1- TANTANCE SHI: shine dukkan hadisin da aka rawaito shi ta hanyoyi masu yawa, kuma ko wacce hanya tana cin gashin kanta, ta yadda a al`adance ba zai yiwu a ce duka marawaitan sun hadu a kan karya ko kuskure ba, kuma yawan adadin ya tabbata a kowanne mataki na warawaitan hadisin, tun daga farkon sanadinsa har zuwa karshe, sannan madogararsu wajan riwaya ta zamo gani ko ji.

2- Sunansa a ilmance: irin wannan hadisin ana kiransa da suna: Al-mutawaatir (المتواتر).

Ma`anar Kalmar Mutawaatir a harshen larabci ita ce: mai bibiyar juna.

Alakar ma`anar da hadisin ita ce kasancewarsa ya zo ta hanyoyi da dama masu bibiyar juna.

3- Sharadinsa: idan mun dubi bayanin da ke lamba ta (1) za mu ga cewa hadisi mutawatiri yana da wasu sharudda guda hudu da sai ya cika su kafin ya tabbata mutawaatir.

Sharuddan kuwa su ne kamar haka:

A- Marawaitansa su zama adadi mai yawa.

B- Rashin yiwuwar haduwarsu bisa karya ko kuskure.

C- Madogarar riwayarsu ta zamo gani ko ji.

D- Yawan adadin ya tabbata a kowanne mataki na marawaitan.

SHARHIN MA`ANAR WAD

Address

No 19 Jushin Gari
Zaria
810241

Telephone

+2347036108733

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daarus-sahaabah Network posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to Daarus-sahaabah Network:

Share