Darul fairah

Darul fairah Darul fairah shafi ne na Masoyan Manzon Allah saw Shehu tijjani RTA DA Shehu ibrahim inyass RTA

Ku cigaba da kasancewa tare da mu

(hikimar sufaye)

NASARAR ƊA NAMIJI; AKWAI GOYON BAYAN MATARSAƊan adam (namiji) Allah ya sanya shi halifa a doron ƙasa, an kallafa masa lu...
03/09/2026

NASARAR ƊA NAMIJI; AKWAI GOYON BAYAN MATARSA

Ɗan adam (namiji) Allah ya sanya shi halifa a doron ƙasa, an kallafa masa lura da gyara duk wata halitta da Allah ya wanzar a gidan duniya, bishiya ko shuka, kiyashi ko giwa kulawa da kiyaye su yana hannun ɗan adam (namiji).

وَإذْ قالَ رَبُّكَ لِلْمَلَآئِكَةِ إنِّي جاعِلٌ في الْأَرِضِ خَلِيفَةً

Sabõda haka Allah Shi ne mafi sani, ya sani cewa mutum ba zai iya kaiwa ga ci ba, har sai an samar masa da mai goyon bayansa, goyon baya daga matarsa akan duk abin da ya tasamma k**a daga karatu ne ko jagoranci, yakan samu nasara mafi gwaɓi a sak**akon dafa masa baya da matarsa za ta yi.

Sayyidun an-Nabiyy {s} ya isar mana 'Sayyidatuna Khadijah {as} yadda ta ƙarfafe Shi {s}, ta mara masa baya, ta zame masa garkuwa, ta rungume Shi lokacin da kowa ya ƙi Shi, ta so Shi lokacin da kowa ya guje Shi, ta zauna da Shi lokacin da aka tsane Shi, ta sadaukar da rai da dukiyarta wajen ƙarfafa masa gwiwa, wanda a wani tsagi Addini ya kafu ne sak**akon jajircewa da Uwar muminai Khadijah {as} ta yi.

Babu laifi idan aka yi tambaya 'shin mene ne ya janyo hoɓɓasa ga Sayyidatuna Khadijah jajircewa wajen ƙarfafar muradin Annabi (na dasa imani a zukata)?'

Amsa a nan ita ce "Mar'atun Salihah", 'Matar kirki', wadda ba ta da hadafi ko buri da ya wuce gaskiya/daidai ta tabbata.

- Idan ƙaramin yaro ne ka gan shi da ƙwarin gwiwa da ƙwazo (shaja'a), bincika za ka samu asalin hakan daga mahaifiyar ce, mai goyon bayansa, idan ta kirki ce: yaron zai tashi da ƙwazo da kirki, akasi sai ya tashi da ƙwazo da.. Wata mahaifiyar kuma yaron na tashi ba ƙwazon b***e kirki, sai wata irin rayuwa da ba sai an bayyana ba.

An ce: "Nasarar ɗa namiji ba ta cika har sai da akwai macen kirki a bayansa. Iyali ce ko mahaifiya, idan ya haɗa biyun, to ka kira shi 'ɗan baiwa' ba shakka".

Shawara: Ka da ki yarda ra'ayinki ya ringa saɓawa da na mijinki, sai dai idan ya zo da alfasha, wannan kuma daban. Kai kuma ka tsaya inda Allah ya ajiye ka, ka bi abin da aka kallafa maka,

🚨 ABIN MAMAKI DA ZAI SA KA TSAYA KA KARANTA! ﷺ 🚨ANNABI MUHAMMAD ﷺ YANA GANIN GABANSA DA BAYANSA! 😮❤️Anas bn Malik (RA) y...
02/09/2026

🚨 ABIN MAMAKI DA ZAI SA KA TSAYA KA KARANTA! ﷺ 🚨

ANNABI MUHAMMAD ﷺ YANA GANIN GABANSA DA BAYANSA! 😮❤️

Anas bn Malik (RA) ya ruwaito cewa, wata rana aka kusa tayar da Sallah, sai Manzon Allah ﷺ ya ce:

«“Ya ku mutane! Hakika ni ne limaminku. Kada ku rika rigina a cikin Ruku’u ko Sujada, kuma kada ku rika ɗaga kawunanku kafin nawa. Domin hakika ina ganinku ta gabana da kuma ta bayana.”»

Sai ya ƙara da cewa:

“Ina rantsuwa da Wanda raina yake hannunsa, da kuna ganin abin da nake gani, da kun yi dariya kaɗan, kuka kuma yi kuka mai yawa.”

Sahabbai s**a tambaya:

“Ya Rasulallahi ﷺ, me ka gani?”

Sai Manzon Allah ﷺ ya ce:

“NA GA ALJANNAH DA KUMA WUTA.” 😢🔥🌹

📖 Hadisi Sahihi ne. Imam Muslim ya ruwaito shi a cikin Kitabus-Salati, haka nan Imam Bukhari da Muslim sun ruwaito wasu lafuzzansa.

💚 Ya Rasulallahi ﷺ, kai ne Annabin Rahama, Hasken Shiriya, Shugabanmu kuma abin alfaharin wannan Al'umma.

Allah Ya ƙara mana soyayyarka ﷺ, Ya haɗa mu da kai a Aljannar Firdausi. 🤲❤️

اللهم صل وسلم وبارك على سيدنا محمد ﷺ وعلى آله وصحبه أجمعين.

TARBIYAR SUFAYE A tsarin tarbiyya da jagorancin sufaye, akwai matakai daban-daban da Shehunai s**a shimfiɗa domin gyaran...
02/09/2026

TARBIYAR SUFAYE

A tsarin tarbiyya da jagorancin sufaye, akwai matakai daban-daban da Shehunai s**a shimfiɗa domin gyaran muridai. Wannan tsari ya samo asali daga koyarwar manyan Shehunanmu, na ga wani tsari na Maulanmu Al-Allama Sidi Muhammad al-Mashri da ya kawo shi a cikin littafinsa mai suna Rawḍ al-Muḥibb al-Fānī, inda ya bayyana yadda Shehi yake karɓar muridi da yadda yake tafiyar da shi a bisa matakai har zuwa ga karshen kusanci.

Da’irar Shehi

Shehi yana da wasu da’irori guda uku na tarbiyyartar da muridi:

1. Da’irar Nesa (الدايرة البعيدة)

2. Da’irar Tsaka-tsaki (الدايرة المتوسطة)

3. Da’irar Kusa (الدايرة القريبة)

1. Da’irar Nesa

Idan murid ya fara zuwa wajen Shehi, zai karɓe shi da abin da ya dace da halinsa – ya ba shi wuridi (azkar) tare da wasu addu’o’i da s**a dace. Sai ya sanya shi a da'ira nesa, ya bar shi tare da sauran jama’a, ba tare da ɗora masa wasu sharadi ba har ma ya bar shi da wasu halayensa babu batun tilasta masa wani abu, sai dai kawai wuridi. A wannan lokaci Shehi yana lura da shi daga nesa, yana kallo ko zai samu cigaba.

2. Da’irar Tsaka-tsaki

Idan Shehi ya lura murid ya fara nuna ƙwazo, sha’awa da niyyar bin hanyar sufanci, sai ya shigar da shi cikin da'irar tsaka-tsaki. A nan Shehi zai fara ba shi wasu umarni, ya hana shi wasu abubuwa, amma ba tare da tsanantawa ba. Wannan mataki ne na horo amma cikin sauƙi da sassauci.

3. Da’irar Kusa

Idan Allah Ya so murid ɗin ya shiga halartar sirri (ḥaḍra), Ya shirya shi da soyayyar Allah, soyayyar Manzon Allah (Sallalahu alaihi wa salam), da soyayyar Shehinsa, sannan ya yi niyya ta gaskiya wajen hidima da ɗaure zuciya cikin tsarkakewa – Shehi zai tabbatar cewa muridi ba shi da wata manufa wajen bin Shehi sai tsira daga halaka ta lahira.
A wannan lokacin sai Shehi ya shigar da shi cikin da'irar kusa, inda yake ɗora masa sharudda bisa ga halinsa da matsayin tarbiyyarsa. Wannan shi ne cikakken kusanci da Shehi.

Wannan tsari na matakai uku yana nuni da hikima da tausasawar Shehunanmu wajen tarbiyyar muridai. Ba sa tilasta murid a matakin farko, sai sun ga ya nuna ƙwazo da ƙaunar tafiyar. Har sai zuciyarsa ta cika da soyayyar Allah da Manzo da Shehi, sannan a dauke shi zuwa ga matakin kusanci. Wannan tsari yana tabbatar da cewa tarbiyyar sufaye tana tafiya ne bisa hikima, hankali da tausayi, domin a karshe murid ya zama bawan Allah na gaskiya,.

Rashin bin wannan tsari na mataki mataki ne ya haifar mana da gurbattatun muridi yanzu lamarin ya koma k**ar gasa, da mutum ya zo babu jarabawa mataki mataki sai kawai a ce ya k**ata ka yi wusuli.

Kafin wannan lokacin idan kaje a baka wazifa ba dukka za a ce an baka ba wani Shehi cewa zai yi kaje ka dinga yin iya lazimun safe da idan ka kwana biyu kana yi sai a ce to ga lazimun yamma idan ka tabbata kana yi sai a baka wazifa kuma a ce ka dinga zuwa zikirin Juma'a

Dan Allah sabbabin Shehunanmu a dinga kula da irin wannan.

Mujaheed M Muh'd
2/9/2026

saw
01/09/2026

saw

DUNIYA BA KOMAI BACE A GURIN ALLAH!.-"Duk wanda za kaga ya riƙi duniya a matsayin abokiyarsa, to lallai shi wawa ne, hau...
31/08/2026

DUNIYA BA KOMAI BACE A GURIN ALLAH!.
-
"Duk wanda za kaga ya riƙi duniya a matsayin abokiyarsa, to lallai shi wawa ne, hausawa ma s**ace: duniya budurwar wawa, mai hankali shine wanda yake nesantar duniya, yake ribatarta da neman lahirarsa acikinta"
-
"Inda ace duniya wata abace mai matuƙar falala a gurin Allah, to lallai bazai taɓa barin wanda baiyi imani dashi ba yayi walwala acikinta, amma da yake lahira tafi alkhairi fiyeda da duniya, sai yake dauwamar da waɗanda s**ayi imani dashi acikin rahamarsa, (aljannah), kuma yake dauwamar da waɗanda basuyi imani dashi ba acikin fushinsa, (wuta)"
-
"Duniya ba komai bane acikinta face ruɗu da kayan yaudara, duk wanda ya riƙi duniya gidan sakankancewar sa, gidan walawarsa, to lallai yana gab-da yayi asara, domin lallai ita duniya ba gidan hutawa bace, sauro ma ya fita, Manzon Allah ﷺ, yace: lallai inda ace duniya tana daidai da fuffuken sauro (wajen daraja), a gurin Allah, to lallai da kuwa kafiri baisha ruwa acikinta ba koda maƙwarwa ɗaya"
Jami'i At-tirmiziy (2320)
-
-ALLAH YASA MU WANYE LAFIYA

MAULUDUN NABIY SAW (03)******FARKON DUNIYA ZUWA HAIHUWAR ANNABI SAW***Bayan halittar Annabi Adam izuwa saukar dashi ciki...
27/08/2026

MAULUDUN NABIY SAW (03)
*
**
***
FARKON DUNIYA ZUWA HAIHUWAR ANNABI SAW
***

Bayan halittar Annabi Adam izuwa saukar dashi cikin duniya, har zuwa yaɗuwar zuri'arsa a bayan qasa, Allah bai bar mutane kara-zube ba face yana aiko Annabawa da manzanni dan suyi kira da gargadi da bushara ga Al'umma. Wasu suji, wasu su bijire.

Amma fa ita duniya daga ranar da aka halicci Annabi Adam daga gareta take kuka saboda tsabar baqinciki da takaici.

Kunsan dalili?

Saboda Abinda Mala'iku s**a hango na cewar Ya'yan Annabi Adam zasu aikata fasadi a bayan ƙasa. Lallai kuwa haka ne, domin Laifin farko da Aka fara yi a duniya shine ki*san kai akan mace, kuma ya'yan Annabi Adam ɗin ne s**a yi haka.

Laifukan kuwa ba a daina ba, sai ma qaruwa suke yi kullum.

Kwatsam watarana akaji duniya tayi tsit! Tayi gunji tayi girgiza ta fashe da dariya. Sanadiyyar Dariyar nan aka ga gumaka suna karyewa suna zubewa Qasa, Bokaye suna kururuwa domin Allolin su sun Tarwatse, Koramar Tsafi ta Qafe, Wutar tsafi ta mutu, katangar tsafi ta karye ta rushe.

Duniya harda waqar ta tana faɗin

LALE DA SAUKA MAHIYAL KUFRI
HASKEN ALLAHU NURUN ALA NURI

SHUGABA TAKA SANNU BABU SAURI
DAN KAI AKAYI NI YA MUNIRI

AHLAN BIKA SAYYADINA BASHEERI
MARHABA BIKA MAULANA QADEERI

Ashe maigida ne ya iso
Ashe shugaba ne ya iso
Ashe ubangida ne ya iso
Ashe haske ne ya iso
Ashe garkuwa ne ya iso

Ashe Sayyadina Muhammadu ne Hasken Allahu, Ubangidan Jinnu Da Arwahu, Mai sanya zuciya tayi Farhu, Ɗan Abdallah baka da Shehu, Kai ka sanya kafurai suyi i*hu, lale da zuwa masoyin Allahu.

Daga ranar Duniya take farinciki

DUNIYA MUNA TAYA KI MURNAR SAMUN YANCI.

27/08/2026
ILIMIN SUFANCIDuk wani abu da ka sani ko wanda baka sani ba, idan ka shiga cikin zurfin ilimin sufaye, za ka fahimci cew...
27/08/2026

ILIMIN SUFANCI

Duk wani abu da ka sani ko wanda baka sani ba, idan ka shiga cikin zurfin ilimin sufaye, za ka fahimci cewa akwai wasu ma’anoni da ba a fahimtar su sai da zurfin ilimi da tarbiyya.

A yau za mu kawo wasu daga cikin bayanan ILIMIN SUFANCI a taƙaice. 👇

① MA’ANAR «لَا إِلٰهَ إِلَّا اللهُ»

A duniyar Musulunci, wannan kalma tana da sunaye da laƙabai daban-daban. Amma a fahimtar sufaye, ana yawan kiranta da:

كَلِمَةُ التَّوْحِيدِ
Kalmar Kaɗaita Allah.

Addinin Musulunci ya ƙunshi manyan matakai guda uku k**ar yadda Hadisin Jibrilu ya zo da su:

1. ISLAM
2. IMAN
3. IHSAN

A fahimtar sufaye, ma’anar لَا إِلٰهَ إِلَّا اللهُ tana zurfafawa gwargwadon wannan matsayi.

🔹 ISLAM:
“Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah.”

A nan, kalmar tana tabbatar da cewa Allah Shi kaɗai ne Ya cancanci a bauta Masa, da sallah, azumi, zakka da sauran ibadu.

🔹 IMAN:
A nan bawa yana ƙara fahimtar cewa duk abin da ya same shi, mai kyau ko mara kyau, yana faruwa ne cikin ilimi da ƙaddarar Allah. Wannan fahimtar tana taimaka wa bawa wajen haƙuri da yafiya.

🔹 IHSAN:
A nan ake neman zurfin sanin Allah da kallon komai cikin dogaro da ikonSa da mulkinSa, tare da fahimtar cewa babu wani abu da yake fita daga sanin Allah da ikonSa.

لَا إِلٰهَ إِلَّا اللهُ مُحَمَّدٌ رَسُولُ اللهِ ﷺ

---

② AL-QUR’ANI

Al-Qur’ani shi ne Littafin Allah da aka saukar wa Shugaban Annabawa kuma Cik**akin Manzanni, Annabi Muhammad ﷺ.

Allah Ya bayyana girman kalmominsa a cikin Al-Qur’ani:

«قُلْ لَوْ كَانَ الْبَحْرُ مِدَادًا لِكَلِمَاتِ رَبِّي لَنَفِدَ الْبَحْرُ قَبْلَ أَنْ تَنْفَدَ كَلِمَاتُ رَبِّي»

Ma’ana: “Ka ce: da teku ya zama tawada domin kalmomin Ubangijina, da teku ya ƙare kafin kalmomin Ubangijina su ƙare.”

Wannan yana nuna girman ilimin Allah da yalwar kalmominsa.

A fahimtar sufaye, fahimtar Al-Qur’ani tana da matakai daban-daban gwargwadon zurfin ilimin bawa.

1. AMMAWA

Ma’abota wannan matsayi suna fahimtar Al-Qur’ani ta hanyar ma’anar zahiri da sharhin kalmomin ayoyi.

Misali:

رَبِّ زِدْنِي عِلْمًا

“Ya Ubangijina, Ka ƙara mini ilimi.”

A nan, ilimi na iya nufin ƙarin sanin abubuwan addini da dokokinsa.

2. KHASSA

A nan ana neman zurfin ma’anar da take bayan zahirin lafazi, musamman ma’anonin tarbiyya da sanin Allah.

وَاتَّقُوا اللهَ وَيُعَلِّمُكُمُ اللهُ

“Ku ji tsoron Allah, kuma Allah Ya sanar da ku.”

3. KHASSATUL KHASSA

Wannan shi ne matakin da ake magana a kai wajen zurfafa bincike cikin haruffa, kalmomi da ma’anonin Al-Qur’ani.

Misali, ana iya yin nazari kan haruffan الم da sauran ḥurūful muqaṭṭaʿāt, tare da neman hikimomi da ma’anoni na ruhaniya.

A cikin wannan tafarki, ana danganta zurfin sanin Allah da matakan fana’i, tarbiyya da kusanci da Allah.

---

🌿 DARASI MAI MUHIMMANCI

Wannan ilimi yana koya wa ɗalibin sufanci cewa ilimi ba karatun kalmomi kawai ba ne; akwai tarbiyyar zuciya, tsarkake niyya, haƙuri, tawali’u da kyautatawa ga bayin Allah.

📖 LABARI MAI DARASI

An taɓa ba da labarin wani attajiri da ya manta da jakar kuɗinsa a masallaci. Bayan ya dawo, sai ya samu wani talaka ya tsinci jakar, ya kuma dawo masa da ita ba tare da ya ɗauki komai ba.

Attajirin ya yi mamakin dalilin da ya sa talakan ya dawo da kuɗin duk da yana cikin buƙata.

Sai ya ce:

“Ni saboda Allah na dawo maka da shi, kuma Allah ne zai biya ni.”

Attajirin ya yi farin ciki sosai har ya ce masa:

“Wallahi kai ɗan Aljanna ne!”

Daga baya sai ya fara tunanin hukuncin maganar da ya faɗa. Ya je wurin malamai domin neman fatawa, amma wasu s**a ɗauki maganar a zahirinta.

Daga ƙarshe aka kai maganar wurin Shehu Ahmad Tijjani رضي الله عنه, wanda aka ruwaito cewa ya ba da amsa bisa ma’anar ayar:

وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ وَنَهَى النَّفْسَ عَنِ الْهَوَى ۝ فَإِنَّ الْجَنَّةَ هِيَ الْمَأْوَى

Ma’ana:

“Amma wanda ya ji tsoron tsayuwa a gaban Ubangijinsa, ya hana kansa bin son zuciya, to lalle Aljanna ce makomarsa.”

Daga nan aka fahimci cewa maganar tana da alaƙa da tsoron Allah, hana kai bin son zuciya da kyautatawa, ba wai hukuncin sakin matar mutumin kai tsaye ba.

---

🤲 YA ALLAH! KA ƘARA MANA ILIMI MAI AMFANI, KA TSARKAKE ZUKATANMU, KA SHAYAR DA MU KA CIYAR DA MU SIRRIN BAKWAI-Bakwai.

MUNA TAWASSALI DA WANDA YA FARA HADDACE AL-QUR’ANI YANA ƊAN SHEKARA BAKWAI ﷺ.

اللهم صل وسلم وبارك على سيدنا محمد وعلى آله وصحبه أجمعين ﷺ

DARUL FAIRAH — ILIMI, TARBIYYA DA HASKEN ZUCIYA. 🤍

🌙✨ ✨🌙Wato so suke idan watan ya k**a… 🤐Kar mu ce komai, mu yi shiru…Mu bar watan ya ƙare a haka?! 😏WALLAHI KUN YI KAƊAN!...
24/08/2026

🌙✨ ✨🌙

Wato so suke idan watan ya k**a…
🤐

Kar mu ce komai, mu yi shiru…
Mu bar watan ya ƙare a haka?! 😏

WALLAHI KUN YI KAƊAN! ❤️‍🔥

Wannan ba watan yin shiru ba ne!
Wannan watan tunawa ne, farin ciki ne, da yawaita salati ga fiyayyen halitta — Sayyidina Muhammad ﷺ ❤️🌙

MAULIDI DOLE NE A GURIN DUKKAN HALITTUN ALLAH! ﷺ ❤️‍🔥

Mu bayyana ƙauna, mu yawaita salati, mu nuna farin cikinmu da zuwan wannan wata mai albarka. 🥰🤲

اللهم صل وسلم وبارك على سيدنا محمد ﷺ ❤️

Batijjane Bashi da Abinda Ya Wuce AlhamdulillahShehu Muhammadu Nazifi Yana Fadi Cikin Littafin Yaqutatil Farida :👇عليكم ...
24/08/2026

Batijjane Bashi da Abinda Ya Wuce Alhamdulillah

Shehu Muhammadu Nazifi Yana Fadi Cikin Littafin Yaqutatil Farida :
👇
عليكم بشكر الله في كل لحظة * على نعم فاضت وعمت وخصت

Ya Kamata Kuyita Godema Alla Kuna Fadin Alhamdulillah ako wani kiftawan ido, Saboda Irin Baiwar Da Allah yayi Muku na Ni'imomi da suke kwararo maku saboda Mai Gidanku Shehu Tijjani

Wata Rana Shehu Muhammadul Ghaly Ya Tambayi Shehu Tijjani r.a cewa:
"Ya Shehu irin wadannan alhairai da ake ba yan Tijjaniyya sabida Karatun Lazimi da wazifa ko Zikirin Juma'a? ko kuma sabida Salatil fatihi da muke karantawa ne?"
👇👇
Sai Shehu Tijjani Yayi shuru Jim kadan Sai yace:
"Saboda ni ne"

dukkan alhairan muna samune sabida Soyayyarmu ga Shehu Tijjany Da Biyayya a gareshi

Yan Uwa Mu Yawaita Ba junanmu Labaran Shehu Tijjani Sabida Yawancin Musifu da Sukayi Yawa sabida Zagin Waliyyai Da Akeyi ne (Allah Ya Kiyayemu)

Address

Alone Ganye Road
Yola
641122

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Darul fairah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share