Darul fairah

Darul fairah Darul fairah shafi ne na Masoyan Manzon Allah saw Shehu tijjani RTA DA Shehu ibrahim inyass RTA

Ku cigaba da kasancewa tare da mu

(hikimar sufaye)

IMAM HASSAN SHEIKH TAHIRU USMAN BAUCHI(R.A) Ya Rubuta Cewa;SHEIKH TAHIRU USMAN BAUCHI(R.A) Yana Cewa;“Idan Mutum Ya Rayu...
02/06/2026

IMAM HASSAN SHEIKH TAHIRU USMAN BAUCHI(R.A) Ya Rubuta Cewa;

SHEIKH TAHIRU USMAN BAUCHI(R.A) Yana Cewa;

“Idan Mutum Ya Rayu a Cikin Wani Lamari Har Ya Saba Da Shi, Lamarin Ya Kan Bi Jininsa(Ruhinsa) Har Ya Zama Shi,

A Duk Lokacin Da Ya Ga Wadansu Mutanen Da Basu Saba Da Wannan Lamarin Na Shi Ba, Sai Zuciyarsa Ta'ki Kar6an Mutanen Sai Ya Ji Baya Sonsu”.

Na Ce; “A Kowace Magana Ta MAULANA SHEHI(R.A) Sai Ka-Ji ‘Kamshin Al-Qur’ani a Cikinta;

"قال معاذ الله أن نأخذ إلا من وجدنا متاعنا عنده إنا إذاً لظالمون"

ALLAH Ya 'Kara wa MAULANA SHEIKH(R.A), kusanci da Manzon Allah saw Ya Barmu Da SoyayyarKU(R.A) Da'iman❤️👏🙏🙏

KOWANNE WALIYI DAGA ƘOFAR IMAM ALI (AS) YAKE SHA 👑A cikin fagen binciken tasawwuf da haƙiƙa, akwai wata gaskiya guda ɗay...
02/06/2026

KOWANNE WALIYI DAGA ƘOFAR IMAM ALI (AS) YAKE SHA 👑

A cikin fagen binciken tasawwuf da haƙiƙa, akwai wata gaskiya guda ɗaya wacce ɗaukacin magabata da manyan shuyukhul ɗariƙa s**a haɗu a kanta: Cewa babu wani waliyi a ɗoron ƙasa, na baya ko na yanzu, face yana samun madadinsa da kwararar sirrinsa ne daga Shugaban Waliyai—Amirul Muminina Imam Ali bin Abi Talib (as).

Ga hujjoji tabbatattu da manyan littattafai da kalaman shuwagabannin Ɗariƙar Tijjaniyya s**a tabbatar:

1. Daga Littattafai da Kalaman Shehu Ibrahim Inyass (RTA)
Malaminmu Shehu al-Islam Ibrahim Inyass, a cikin littafinsa mai daraja na fassara da yabon Manzon Allah (saww) da iyalansa, da kuma kalaman da yake yi a wuraren taron ilimi, ya sha nanata cewa kowace faɗakarwa da buɗi na waliyai yana da alaƙa da Imam Ali:
Shehu Ibrahim (RTA) ya tabbatar da cewa dukkan silsilolin sufanci da kofofin dake kai mutum ga sanin Allah, to lallai suna komawa ne ga Imam Ali (as), wanda shi ne ƙofar birnin ilimi na Annabi (saww).

A cikin waƙoƙinsa na yabo (Diwani), Shehu Ibrahim ya nuna cewa soyayya da alaƙa da Imam Ali da Ahlul Bayt ita ce jigon da kowane babban waliyi yake takama da shi domin samun kariya da madadin da ba ya yankewa.

2. Daga Asalin Koyarwar Shehu Ahmadu al-Tijjani (RTA)
Idan aka duba littafin "Jawahirul Ma'ani", wanda shi ne babban littafin tushe na Ɗariƙar Tijjaniyya, an kawo cewa:
Kafin Shehu Ahmadu al-Tijjani ya sami buɗi na musamman kai-tsaye daga hannun Manzon Allah (saww) a falke, ya karɓi ɗariƙu da dama na magabata (kamar su Ɗariƙar Qadiriyya, Shaziliyya, da sauran su).

Dukkan waɗannan ɗariƙu da ya riƙe a farkon lamari, silsilarsu tana komawa ne ta hannun manyan tabi'ai zuwa ga Imam Ali (as). Wannan ya nuna cewa tun kafin bayyanar babban rabo, kofofin Imam Ali ne suke tarbiyyantar da manyan waliyai.

3. Karin Hujjoji Daga Manyan Littattafan Sufaye na Duniya
Littafin "Futuhatul Makkiyya" (Na Ibn Arabi): Ya bayyana cewa: "Imam Ali shi ne asali kuma madubin da dukkan waliyai suke kallon hasken Ubangiji ta cikinsa. Matsayinsu reshe ne na bishiyar Wilayah ta Imam Ali (as)."

Littafin "Kashful Mahjub" (Na Al-Hujwiri): "Imam Ali (as) shi ne jagoran dukkan silsila da asirin sufaye. Ɗaukacin waliyan Allah suna duba zuwa gare shi wajen sanin ƙofofin haƙiƙa."

Kamar yadda Annabi (saww) ya ce: "Ni ne birnin ilimi, Ali kuma shi ne ƙofarsa."
Haka abin yake a fagen sufanci: Annabi shi ne tekun madadi, Imam Ali kuma SH ne bututun da yake raba ruwan ga dukkan waliyan duniya.

Shehu Ahmadu al-Tijjani da Shehu Ibrahim Inyass sun koyar da mu cewa girma da daukaka suna tabbata ne kawai ga wanda ya san darajar waɗannan kofofi.

Aliyu abussubdain ✍️

Wasu Hotunan Gidan Shehu Ahmad Tijjani RTA Dake Garin Fass A Kasar Morocco. Allah ya bamu albarkacin Sheikh Ahmad Tijjan...
02/06/2026

Wasu Hotunan Gidan Shehu Ahmad Tijjani RTA Dake Garin Fass A Kasar Morocco. Allah ya bamu albarkacin Sheikh Ahmad Tijjani RTA. Amiin

An Kawowa Annabi MUHAMMADU, SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM, Ruwa A 'Kwarya.\Sai WaNi Daga Cikin Sahabbai, Yaga Tsinke A Ciki...
02/06/2026

An Kawowa Annabi MUHAMMADU, SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM, Ruwa A 'Kwarya.
\
Sai WaNi Daga Cikin Sahabbai, Yaga Tsinke A Cikin Ruwa, Sai Yace.
\
Ya Rasulullahi, Akwai Tsinke A Cikin Ruwan Da Aka Kawo, KayiMin Na Cireshi.
\
Rasulullahi, Yayi Godiya, Ya Dinga Gode Wannan Abun, Sannan Yace Da Sahabin ALLAH Ya 'Dan'dasaka.
\
Nan Take Sahabin Ya Zama Kyakkyawa Na Gaban Kwatance.
|
|
A Lokacin Ya'kin Badar, Takobin Ukashatu {RA}, Ya Karye.
\
Annabi MUHAMMADU, SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM, Ya Karyo Itacen Dabino.
\
Ya Sarce Ganyen Dake Jikin Dabinon, YaNa 'Daga Itacen Sama.
\
Saiya Zama Takobin Da Duk Filin Ya'kin Babu KamarSa.
\
ALLAH Ya Rufa MaNa Asiri.
\
ALLAH Yasa Mu Cika Da IMANI.
\
Dan Albarkar Annabi MUHAMMADU, SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM.

02/06/2026

GARI YA WAYE
Gaisuwa Zuwa Ga. 😍👇
Muhammadur Rasulullahi. ﷺ

WAZIFA. 1- fatiha (daya 1)2- Istigfari (talatin 30)3- salatin Annabi (hamsin 50)4- lailahaillallahu (dari 100)5- Jauhara...
02/06/2026

WAZIFA.
1- fatiha (daya 1)
2- Istigfari (talatin 30)
3- salatin Annabi (hamsin 50)
4- lailahaillallahu (dari 100)
5- Jauharatul Kamali (sha biyu 12)

LAZIMI (morning and evening)

1. Fatiha (daya 1)
2. Istigfari (dari 100)
3. Salatin Annabi (dari 100)
4. Hailala (dari 100).

This is the work of Tijaniiya, nothing els.

INNA LILLAHI WA INNAA ILAIHI RAJI'UNMuna sanar da ƴanuwa babban rashi da muka yi jinya Litinin 01/06/2026 na ɗaya daga c...
02/06/2026

INNA LILLAHI WA INNAA ILAIHI RAJI'UN

Muna sanar da ƴanuwa babban rashi da muka yi jinya Litinin 01/06/2026 na ɗaya daga cikin manyan bayin Allah Alh. Ahmadu Laushi wanda yayiwa Shehu Ibrahim Radhiyallahu Ta'ala Anhu hidimar zirga-zirga da shi lokacin da yazo Jos, sannan hadimi ne na bayin Allah. Tare da haka muna sanar da cewa yau baza mu samu damar karatun Rimahu ba sakamakon wannan rasuwa.

Alh. Ahmadu Laushi babban hadimin Faira ne. Sannan muna roƙon ƴanuwa waɗanda za su iya su karanta masa Hailala Dubu Saba'in (70,000) saboda hidimar sa cikin sha'anin Faira.

Muna sake miƙa Ta'aziyya ga Iyalai, dangi, ƴanuwa da masoya. Allah ya jaddada masa Rahmah Albarkar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Alihi Wa Sahbihi Wa Sallamm

Mun gode

Wasiyyar Sheikh Ibrahim Nias (R.T.A) zuwa gare mu 🌿Sheikh Ibrahim Nias (R.T.A) ya kasance yana cewa:Ina yi muku wasiyya ...
01/06/2026

Wasiyyar Sheikh Ibrahim Nias (R.T.A) zuwa gare mu 🌿

Sheikh Ibrahim Nias (R.T.A) ya kasance yana cewa:

Ina yi muku wasiyya da ku kiyaye sirrinku, ko da kuwa abubuwan duniya ne. Domin duk wanda ya ɓoye sirrinsa, to ya mallaki al’amarin rayuwarsa da tafiyar harkokinsa.

Ku lazimci haƙuri a kan kowace jarrabawa da Allah Ya ƙaddara muku, kuma ku kasance daga cikin masu yarda da ƙaddara.

Ku so juna saboda Allah.

Ku ziyarci juna saboda Allah.

Ku zauna tare da juna saboda Allah.

Kuma ku lazimci yi wa sheikh ɗinku hidima.

Sufaye suna cewa:

“Duk wanda ya yi mana hidima, za mu gabatar da shi zuwa ga Ubangijinsa, ko da himmarsa ba ta kai shi ba.”

Saboda haka:

Kada ku yanke igiyoyin ’yan’uwantaka saboda Allah a tsakaninku.

Kada wani daga cikinku ya juya wa ɗan’uwansa baya saboda wani kuskure da ya aikata.

Kada ku yi hassada a tsakaninku.

Kada ku ƙi juna saboda son zuciya.

Ku kasance bayin Allah masu ’yan’uwantaka saboda Allah.

Ya Allah, Ka ƙara wa sheikhinmu karamci da ɗaukaka, Ka sanya mu cikin masu samun madadinsa da albarkarsa, saboda alfarmar shugabanmu Manzon Allah ﷺ.

Amin 🤲

Barhama Tv

🌙 LITININ – Babbar Rana Ta Albarka 🌙Ranar da An Haifi Sarkin Halitta (S.A.W),Ranar da Annabta ta sauka masa,Ranar da Ya ...
01/06/2026

🌙 LITININ – Babbar Rana Ta Albarka 🌙

Ranar da An Haifi Sarkin Halitta (S.A.W),
Ranar da Annabta ta sauka masa,
Ranar da Ya ɗauki Hijira,
Ranar da Ya shiga Madina cikin karamci da haske,
Ranar da Ya ɗora Dutse ya raba gardama,
Ranar da An haifi Sayyida Fadima (A.S),
Ranar da Fathul Makka ta tabbata,
Ranar da Suratul Ma’ida ta sauka,
Har ma da ranar da Ya koma ga Rahmar Ubangiji (S.A.W).

LITININ, rana ce da Annabi ya haskaka ta da kasancewarsa.
Rana ce da mala'iku ke shawagi da albarka,
Rana ce da masoya ke ƙara kusantar Rahma.

🕋 Ya Allah, Don darajar wannan LITININ mai ɗauke da hasken Mustapha (S.A.W):
▪️ Ka yaye damuwarmu,
▪️ Ka buɗe mana ƙofofin arziki,
▪️ Ka kawo mana sauƙi cikin al’amuranmu,
▪️ Ka ƙara mana soyayyar Annabi (S.A.W),
▪️ Ka yi mana albarka cikin dukkan al’amuranmu.

🕋 Ya Allah, don albarkar wannan rana mai daraja,
Ka zuba mana nutsuwa a zukata,
Ka yaye damuwarmu,
Ka cika burikanmu na alkhairi,
Ka albarkaci rayuwarmu da hasken Annabi (S.A.W).

Ameeeeeen.

DARUL Fairah

💫 Duk wanda ya yawaita salati, Allah yana yawaita masa alheri.  ✍️ Amiru Alkarimeyya 🫶
31/05/2026

💫 Duk wanda ya yawaita salati, Allah yana yawaita masa alheri.
✍️ Amiru Alkarimeyya 🫶

Address

Alone Ganye Road
Yola
641122

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Darul fairah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share