Zawiyan Arufu Wukari LGA

Zawiyan Arufu Wukari LGA This page was created to spread knowledge and educate our brothers who are followers of Sheikh Tijja

Eid Mubarak 🌙✨ I extend my warmest wishes to you all on this blessed occasion of Sallah. May this sacred celebration bri...
21/03/2026

Eid Mubarak 🌙✨

I extend my warmest wishes to you all on this blessed occasion of Sallah. May this sacred celebration bring peace, joy, and abundant blessings to your homes and families.

May your prayers be accepted, your sacrifices rewarded, and your hearts filled with gratitude and love. Let us continue to uphold unity, compassion, and kindness in our community.

Mallam IBRAHIM.K. AHMAD (Chief IMAN ARUFU)

📢 SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!Cikin farin ciki muke sanar da al’ummar Musulmi na garin Jalingo, Jihar Taraba cewa:A yau...
19/02/2026

📢 SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!
Cikin farin ciki muke sanar da al’ummar Musulmi na garin Jalingo, Jihar Taraba cewa:
A yau Alhamis, 19 ga Fabrairu 2026,
Sheikh Habibu Hassan Almakki zai fara gabatar da Tafsirin Al-Qur’ani Mai Girma, kamar yadda ya saba duk shekara.
🕌 Wuri: Masallacin Sarkin Muri, Jalingo
🕑 Lokaci: Bayan Sallar Azahar — 2:00 na rana
Muna roƙon Allah (SWT) Ya ba mu ikon halarta tare da samun albarka da amfanin wannan majalisi mai daraja. Ameen.
A sanar da juna domin kowa ya amfana.

14/02/2026

Addu’ar Maraba da Watan Ramadan daga nan Zawiyan Arufu Wukari LGA ga yan-uwa baki daya.
Godiya ga Mahalicci:
Neman Albarkacin Watan Ramadan:
* Isar da mu: Ya Allah, ka nuna mana wannan wata na Ramadan Kareem da yake gabatowa.
* Lafiya da Aminci: Allah ka sa mu fara azumin nan cikin koshin lafiya, mu kuma kammala shi lafiya.
* Karbar Ayyuka: Ka ba mu ikon gudanar da ibadu yadda kake so, kuma ka karba mana.
Alfarmar Annabi (SAW):
"Muna rokonka Allah ka amsa mana wadannan addu'o'i namu, albarkacin Shugabanmu Manzon Allah, Sallallahu Alaihi Wasallam."
Ramadan Kareem a gareka da daukacin iyali.

INNALILLAHI WA'INNA'ILAIHI RAJI'UNWallahi, duniya ta yi babban rashi; cikin alhini muke sanar daku Allah yayiwa Sheikh U...
02/02/2026

INNALILLAHI WA'INNA'ILAIHI RAJI'UN

Wallahi, duniya ta yi babban rashi; cikin alhini muke sanar daku Allah yayiwa Sheikh Usman Kusfa Rigirigi na Annabi Muhammad (S.A.W.)rasuwa cikin wannan dare. Jana’iza ƙarfe huɗu da rabi (4:30 PM) a filin Locos, wajen da yake yin Maulidin Annabi Muhammad S.A.W. yau Litinin, Allah ya yi masa rahama, alfarmar Annabi Muhammad S.A.W. Amin.*

31/01/2026
29/01/2026
28/01/2026
Yaumul Kiswa
27/01/2026

Yaumul Kiswa

GA DALAR ZINARE BABU BATTAR DIBA!  Da dayawanmu an san irin ababen da wannan littafi ya kunsa na tarin ilmai game da dar...
23/01/2026

GA DALAR ZINARE BABU BATTAR DIBA!

Da dayawanmu an san irin ababen da wannan littafi ya kunsa na tarin ilmai game da darikar Tijjaniyya, to da lallai za'a sanya sharadi na cewa babu wani da lakanawa wuridin wannan Darika har sai an karantar dashi wannan littafi ya karanta ya sauke ya fahimci abinda ya kunsa.

Maulana Sharif ya aje karatu mai cike da fadakarwa, warwarewa, nasiha, wa'azi da kuma kwaranyo bayanai na ilmi masu shiryarwa zuwa fayyacewa da cikinsu mutum zai fahimci darikar, hukunce-hukuncenta, sharuddanta da sauran ababe dake da alaka da ita.

LALLAI A NEMI WANNAN LITTAFI, HAKIKA ZA'A RABAUTA CIKI, KUMA ZA'A DACE CIKIN ABINDA YAKE SHIRYARWA.

ALLAH YA KARA LAFIYA.

ALHAMDULILLAH.

FREE Sheikh Sani Khalifa Zaria 👌Neman Adalci kan Tsare Sheikh Sani Khalifa Ba Bisa Ka’ida Ba na Tsawon Kwanaki 23, Ba Ta...
04/01/2026

FREE Sheikh Sani Khalifa Zaria 👌

Neman Adalci kan Tsare Sheikh Sani Khalifa Ba Bisa Ka’ida Ba na Tsawon Kwanaki 23, Ba Tare da Bayyana Inda Yake Ko Barin Sa Tattaunawa da Kowa Ba

An tsare Sheikh Sani Khalifa tsawon kwanaki 23 ba tare da bayyana inda yake, ba tare da sanar da iyalansa takamaiman laifi, kuma ba a barin sa magana da kowa ba, abin da ya saba wa ka’idojin doka da hakkin dan Adam.

Da farko, an rufe asusun bankinsa ba tare da wata sanarwa a rubuce ba. Lokacin da aka tuntubi bankinsa da ke Zaria, aka bayyana cewa ba za a iya bude asusun ba, sai dai ya je babban reshen bankin da ke Abuja. Bayan zuwansa Abuja ne jami’an tsaro s**a zo s**a tafi da shi, bisa zargin cewa wani soja da ake zargi da hannu a yunkurin juyin mulki ya taba tura masa kudin naira miliyan biyu.

Sheikh Sani Khalifa ba shi da wata hulda kai tsaye ta kasuwanci ko sadarwa da wannan sojan. Abin da ya faru kawai shi ne wani almajirinsa ya san sojan, kuma ya taba hada su ta waya inda s**a gaisa kawai. Daga bisani, sojan ya karbi lambar asusun Mallam ta hannun almajirinsa, sannan ya tura Naira miliyan biyu domin neman albarka da addu’a, kamar yadda mutane da dama ke yi wa malamai, ba tare da wata alaka ta siyasa ko laifi ba. Koda ance duk wanda ya taba transaction da wannan sojan ne ake bi ake kamawa.

Hukumomi sun bayanna cewa list din wadanda ake zargin ma ba sunansa, kuma an tabattar da bayada lafin kome amma har yanzu ana tsare shi. Wannan hakan tayar da tambayoyi game da sahihanci da adalci na ci gaba da tsare shi.

Muna kira ga hukumomin da abin ya shafa da su bayyana inda Sheikh Sani Khalifa yake nan take, ko kuma a sake shi ba tare da bata lokaci ba, domin tsare mutum ba tare da cikakken dalili ba zalunci ne kuma sabawa dokane. Duba da cewa shi Kansa yunkurin juyin mulkin gomnatin nigeria ta karyatasa.

✍️

Wataran ana karatun Ashafa sai sheikh aliyu harazimi yace tsaya da karatunnan, wanine nagani ana fadar shugaba shi kuma ...
01/01/2026

Wataran ana karatun Ashafa sai sheikh aliyu harazimi yace tsaya da karatunnan, wanine nagani ana fadar shugaba shi kuma yana bacci, shehi yace dama zaiyiwu ana zancan shugaba mutum ya dinga yin bacci.
ALLAH yakara mana son shugaba Alaihi sallam.

FASSARAR LITTAFIN RUHUL ADAB (39)(Daga Sayyidi Mujaheed M Muh'd)Insha Allah zamu dora a fassarar shahararren littafin Ma...
29/12/2025

FASSARAR LITTAFIN RUHUL ADAB (39)
(Daga Sayyidi Mujaheed M Muh'd)

Insha Allah zamu dora a fassarar shahararren littafin Maulana Shehul Islam Alhaji Ibrahim Niass. Allah ya kara masa yarda na Ruhul adab.
Yau za mu tashi a baiti na Talatin da tara a jerin baitocin

Shehu ya dora mana da cewa:

لا تَحْقِرَنَّ مُسْلِمًا لا تَذْكُرا
عَيْبَ امْرِئٍ وَالعَيْبُ مِنْكَ قَدْ يُرَى

Fassara baitin

Kada ka raina kowane Musulmi;
kada ka ambaci aibin wani, alhali aibin naka ana iya ganinsa.

Ma'anar a na Kada ka raina Musulmi, kada ka fallasa aibin wani, domin watakila aibinka ya fi, nasa amman Allah Ya rufe shi.”

Fassarar Kalma-bayan-Kalma

لا تحقرن مسلما
Kada ka raina ko ƙasƙantar da kowane Musulmi.

لا تذكرن
Kada ka ambata, kada ka fallasa.

عيب امرئ
Aibin wani mutum.

والعيب منك قد يرى
Alhali aibinka yana iya kasancewa a fili, ko ka fi nasa.

Wannan baitin yana nuni da tsantsar Sufanci wanda a yanzu da yawa masu da'awar Sufanci sun sauka da daga wannan ƙa’ida. Zan yi amfani da wannan damar domin na kara yi mana nasiha.

Duk wanda ya raina halittar Allah, to bai san Allah ba. Domin sanin Allah yana bayyana ne ta hanyar girmama abin da Ya halitta. Allah Maɗaukaki Ya halicci mutum da karramawa, Ya busa masa daga Ruhunsa, Ya kuma fifita shi akan yawancin halittunsa. Duk wanda ya raina wani mutum saboda launi, matsayi, talauci ko kuskure, hakika ya raina hikimar Mahalicci, domin rainin halitta na kai tsaye rainin Wanda Ya halicce ta ne.

Allah Maɗaukaki Ya ce:

وَلَقَدۡ كَرَّمۡنَا بَنِیۤ ءَادَمَ وَحَمَلۡنَـٰهُمۡ فِی ٱلۡبَرِّ وَٱلۡبَحۡرِ وَرَزَقۡنَـٰهُم مِّنَ ٱلطَّیِّبَـٰتِ وَفَضَّلۡنَـٰهُمۡ عَلَىٰ كَثِیرࣲ مِّمَّنۡ خَلَقۡنَا تَفۡضِیلࣰا
Surah Al-Isrāʾ: 70

“Lalle Mun karrama ‘ya’yan Adam, Mun kuma ɗauke su a ƙasa da teku, Mun arzuta su da kyawawan abubuwa, Mun kuma fifita su akan da yawa daga cikin abin da Muka halitta.”
(Suratul Isrā’i: 70)

A wata ayar ya ce

یَـٰۤأَیُّهَا ٱلنَّاسُ إِنَّا خَلَقۡنَـٰكُم مِّن ذَكَرࣲ وَأُنثَىٰ وَجَعَلۡنَـٰكُمۡ شُعُوبࣰا وَقَبَاۤىِٕلَ لِتَعَار

Address

Arufu Wukari LGA
Ukari

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zawiyan Arufu Wukari LGA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share